Mattiyu 24 – HCB & NIVUK

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 24:1-51

Alamun ƙarshen zamani

(Markus 13.1,2; Luka 21.5,6)

1Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali. 2Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”

(Markus 13.3-13; Luka 21.7-19)

3Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?”

4Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku. 5Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa. 6Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna. 7Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam. 8Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.

9“Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni. 10A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna, 11annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa. 12Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi, 13amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto. 14Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.

(Markus 13.14-23; Luka 21.20-24)

15“Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’24.15 Dan 9.27; Dan 11.31; Dan 12.11 wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane), 16to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. 17Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida. 18Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa. 19Kaiton mata masu ciki da mata masu renon ’ya’ya a waɗancan kwanakin! 20Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci. 21Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.

22“Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin. 23A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata. 24Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu. 25Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.

26“Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata. 27Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance. 28Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.

(Markus 13.24-27; Luka 21.25-28)

29“Nan da nan bayan tsabar wahalan nan

“ ‘sai a duhunta rana,

wata kuma ba zai ba da haskensa ba;

taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama,

za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’24.29 Ish 13.10; Ish 34.4

30“A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma. 31Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.

(Markus 13.28-31; Luka 21.29-33)

32“Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa. 33Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa. 34Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru. 35Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.

Rana ko sa’a ba a sani ba

(Markus 13.32-37; Luka 17.26-30,34-35)

36“Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai. 37Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum. 38Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi; 39ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum. 40Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya. 41Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.

42“Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba. 43Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida. 44Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.

(Luka 12.35-48)

45“Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci? 46Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka. 47Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa. 48Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’ 49Sa’an nan yă fara dūkan ’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya. 50Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba. 51Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.

New International Version – UK

Matthew 24:1-51

The destruction of the temple and signs of the end times

1Jesus left the temple and was walking away when his disciples came up to him to call his attention to its buildings. 2‘Do you see all these things?’ he asked. ‘Truly I tell you, not one stone here will be left on another; every one will be thrown down.’

3As Jesus was sitting on the Mount of Olives, the disciples came to him privately. ‘Tell us,’ they said, ‘when will this happen, and what will be the sign of your coming and of the end of the age?’

4Jesus answered: ‘Watch out that no-one deceives you. 5For many will come in my name, claiming, “I am the Messiah,” and will deceive many. 6You will hear of wars and rumours of wars, but see to it that you are not alarmed. Such things must happen, but the end is still to come. 7Nation will rise against nation, and kingdom against kingdom. There will be famines and earthquakes in various places. 8All these are the beginning of birth-pains.

9‘Then you will be handed over to be persecuted and put to death, and you will be hated by all nations because of me. 10At that time many will turn away from the faith and will betray and hate each other, 11and many false prophets will appear and deceive many people. 12Because of the increase of wickedness, the love of most will grow cold, 13but the one who stands firm to the end will be saved. 14And this gospel of the kingdom will be preached in the whole world as a testimony to all nations, and then the end will come.

15‘So when you see standing in the holy place “the abomination that causes desolation,”24:15 Daniel 9:27; 11:31; 12:11 spoken of through the prophet Daniel – let the reader understand – 16then let those who are in Judea flee to the mountains. 17Let no-one on the housetop go down to take anything out of the house. 18Let no-one in the field go back to get their cloak. 19How dreadful it will be in those days for pregnant women and nursing mothers! 20Pray that your flight will not take place in winter or on the Sabbath. 21For then there will be great distress, unequalled from the beginning of the world until now – and never to be equalled again.

22‘If those days had not been cut short, no-one would survive, but for the sake of the elect those days will be shortened. 23At that time if anyone says to you, “Look, here is the Messiah!” or, “There he is!” do not believe it. 24For false messiahs and false prophets will appear and perform great signs and wonders to deceive, if possible, even the elect. 25See, I have told you in advance.

26‘So if anyone tells you, “There he is, out in the desert,” do not go out; or, “Here he is, in the inner rooms,” do not believe it. 27For as lightning that comes from the east is visible even in the west, so will be the coming of the Son of Man. 28Wherever there is a carcass, there the vultures will gather.

29‘Immediately after the distress of those days

‘ “the sun will be darkened,

and the moon will not give its light;

the stars will fall from the sky,

and the heavenly bodies will be shaken.”24:29 Isaiah 13:10; 34:4

30‘Then will appear the sign of the Son of Man in heaven. And then all the peoples of the earth24:30 Or the tribes of the land will mourn when they see the Son of Man coming on the clouds of heaven, with power and great glory.24:30 See Daniel 7:13-14. 31And he will send his angels with a loud trumpet call, and they will gather his elect from the four winds, from one end of the heavens to the other.

32‘Now learn this lesson from the fig-tree: as soon as its twigs become tender and its leaves come out, you know that summer is near. 33Even so, when you see all these things, you know that it24:33 Or he is near, right at the door. 34Truly I tell you, this generation will certainly not pass away until all these things have happened. 35Heaven and earth will pass away, but my words will never pass away.

The day and hour unknown

36‘But about that day or hour no-one knows, not even the angels in heaven, nor the Son,24:36 Some manuscripts do not have nor the Son. but only the Father. 37As it was in the days of Noah, so it will be at the coming of the Son of Man. 38For in the days before the flood, people were eating and drinking, marrying and giving in marriage, up to the day Noah entered the ark; 39and they knew nothing about what would happen until the flood came and took them all away. That is how it will be at the coming of the Son of Man. 40Two men will be in the field; one will be taken and the other left. 41Two women will be grinding with a hand-mill; one will be taken and the other left.

42‘Therefore keep watch, because you do not know on what day your Lord will come. 43But understand this: if the owner of the house had known at what time of night the thief was coming, he would have kept watch and would not have let his house be broken into. 44So you also must be ready, because the Son of Man will come at an hour when you do not expect him.

45‘Who then is the faithful and wise servant, whom the master has put in charge of the servants in his household to give them their food at the proper time? 46It will be good for that servant whose master finds him doing so when he returns. 47Truly I tell you, he will put him in charge of all his possessions. 48But suppose that servant is wicked and says to himself, “My master is staying away a long time,” 49and he then begins to beat his fellow servants and to eat and drink with drunkards. 50The master of that servant will come on a day when he does not expect him and at an hour he is not aware of. 51He will cut him to pieces and assign him a place with the hypocrites, where there will be weeping and gnashing of teeth.