Mattiyu 2 – HCB & CRO

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 2:1-23

Ziyarar Masana

1Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana,2.1 A al’adance Masu Hikima daga gabas suka zo Urushalima 2suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas2.2 Ko kuwa a tauraro sa’ad da ya taso mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”

3Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima. 4Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi. 5Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.

6“ ‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda,

ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba,

gama daga cikinki mai mulki zai zo,

wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’2.6 Mik 5.2

7Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana. 8Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”

9Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake. 10Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai. 11Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur. 12Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.

Tserewa zuwa Masar

13Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”

14Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar, 15inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”2.15 Hos 11.1

16Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan ’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan. 17Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,

18“An ji murya a Rama,

tana kuka da makoki mai tsanani,

Rahila ce take kuka domin ’ya’yanta,

an kāsa ta’azantar da ita,

don ba su.”2.18 Irm 31.15

Komowa zuwa Nazaret

19Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar, 20ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”

21Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila. 22Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili, 23ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”

Knijga O Kristu

Matej 2:1-23

Dar zvjezdoznanaca

1Isus se rodio u gradu Betlehemu u Judeji za vladavine kralja Heroda. U to vrijeme neki mudraci s Istoka stignu u Jeruzalem 2i stanu se raspitivati: “Gdje je taj novorođeni kralj Židova? Vidjeli smo njegovu zvijezdu na istoku pa smo mu se došli pokloniti.”

3To veoma uznemiri kralja Heroda, a i sav Jeruzalem. 4Kralj sazove svećeničke poglavare i pismoznance da se raspita gdje se Krist treba roditi. 5“U Betlehemu u Judeji”, odgovore mu, “jer je prorok napisao:

6‘Betleheme, ti nisi samo nevažno judejsko selo,

jer će iz tebe poteći vladar

koji će voditi moj narod, Izrael.’”2:6 Mihej 5:2; 2 Samuelova 5:2.

7Tada Herod potajno pošalje po mudrace da od njih dozna vrijeme pojavka zvijezde. 8Zatim ih pošalje u Betlehem: “Pođite i pomnjivo se raspitajte za dijete. Kad ga pronađete, vratite se i javite mi da mu se i ja pođem pokloniti.”

9Poslušali su kralja i pošli. I gle! Zvijezda koju su vidjeli da izlazi išla je pred njima sve dok se nije zaustavila iznad mjesta gdje se nalazilo dijete. 10Kad su ju ugledali, silno su se razveselili. 11Uđu u kuću i ugledaju dijete s njegovom majkom Marijom te padnu ničice i poklone mu se. Zatim otvore škrinje s blagom i daruju mu zlato, tamjan i smirnu. 12Poslije toga su u snu dobili upute da se ne vraćaju k Herodu, te su se u svoju zemlju vratili drugim putem.

Bijeg u Egipat

13Kad su otišli, anđeo se Gospodnji ukaže u snu Josipu. “Ustani i bježi u Egipat s djetetom i s njegovom majkom”, reče anđeo, “i ostani ondje sve dok ti ne kažem da se vratiš jer će kralj Herod tražiti dijete da ga ubije.”

14Josip ustane i još se iste noći zaputi u Egipat s Marijom i djetetom. 15Ostao je ondje sve do Herodove smrti. Time se ispunilo što je Gospodin rekao preko proroka: “Pozvao sam svojega sina iz Egipta.”2:15 Hošea 11:1.

16Kad uvidi da su ga mudraci izigrali, Herod se silno razgnjevi i pošalje vojnike da u Betlehemu i po svoj okolici pobiju sve dječake od dvije godine i mlađe, prema vremenu izlaska zvijezde za koje se raspitao u mudraca. 17Tada se ispunilo ono što je rekao prorok Jeremija:

18“U Rami se čuje glas,

zapomaganje i gorak plač;

to Rahela oplakuje svoju djecu

i ne dade se utješiti jer ih više nema.”

Povratak iz Egipta

19Kad je Herod umro, u Egiptu se anđeo Gospodnji ukaže Josipu u snu 20i reče mu: “Ustani i povedi dijete i njegovu majku natrag u izraelsku zemlju, jer su oni koji su ga pokušavali ubiti mrtvi.” 21On ustane, uzme dijete i majku i vrati se u Izrael. 22Putem dozna da je novim kraljem postao Arhelaj, Herodov sin, pa se prestraši. Tada i u snu dobije upozorenje da ne ide u Judeju, te umjesto toga ode u Galileju 23i nastani se u Nazaretu. Time se ispunilo što su o Mesiji napisali proroci: “Zvat će se Nazarećanin.”