Mattiyu 16 – HCB & PCB

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 16:1-28

Neman alama

(Markus 8.11-13; Luka 12.54-56)

1Farisiyawa da Sadukiyawa suka zo don su gwada Yesu ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.

2Ya amsa ya ce,16.2 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na farko-farko ba su da raguwar aya 2 da kuma dukan aya 3 “Sa’ad da yamma ta yi, kukan ce, ‘Yanayi zai yi kyau, gama sararin sama ya yi ja,’ 3da safe kuma, ku ce, ‘Yau kam za a yi hadari, gama sararin sama ya yi ja, ya kuma ɓata fuska.’ Kun san yadda za ku fassara yanayin sararin sama, amma ba kwa iya fassarar alamun lokuta. 4Wannan mugu da mazinacin zamani yana neman wani abin banmamaki, amma ba wata alamar da za a nuna wa wannan zamani sai dai ta Yunana.” Sai Yesu ya bar su ya tafi abinsa.

Yistin Farisiyawa da Sadukiyawa

(Markus 8.14-21)

5Da suka ƙetare tafkin, almajiran sun manta su riƙe burodi. 6Yesu ya ce musu, “Ku yi hankali, ku yi taka zallan da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”

7Sai suka fara tattaunawa da junansu suna cewa, “Ko don ba mu kawo burodi ba ne.”

8Sane da abin da suke zance, sai Yesu ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, don me kuke magana da junanku a kan ba ku zo da burodi ba? 9Har yanzu ba ku gane ba ne? Ba ku tuna da gurasa biyar ɗin nan na mutum dubu biyar ba? Kwando nawa kuka tattara cike? 10Ko kuma burodi bakwai nan na mutum dubu huɗu, cikakku manyan kwanduna nawa kuka ɗauka? 11Yaya kuka kāsa gane cewa ba zancen burodi nake yi ba? Sai dai ku yi hankali da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.” 12Sa’an nan suka gane ba cewa yake musu su yi hankali da yistin da ake amfani da shi a burodi ba ne, sai dai su yi hankali da koyarwar Farisiyawa da Sadukiyawa ne.

Shaidar Bitrus a kan Kiristi

(Markus 8.27-30; Luka 9.18-21)

13Sa’ad da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, sai ya tambayi almajiransa ya ce, “Wa mutane suke ce da Ɗan Mutum?”

14Suka amsa, “Waɗansu suna ce Yohanna Mai Baftisma; waɗansu kuma suna ce annabi Iliya; har wa yau waɗansu suna ce Irmiya ne ko kuma ɗaya daga cikin annabawa.”

15Ya tambaye su, “Amma ku fa, wane ne ni a ganinku?”

16Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi,16.16 Ko kuwa a Almasihu; haka ma a aya 20 Ɗan Allah mai rai.”

17Yesu ya amsa ya ce, “Mai albarka ne kai Siman ɗan Yunana, gama ba mutum ne ya bayyana maka wannan ba, sai dai Ubana da yake cikin sama. 18Ina kuwa gaya maka, kai ne Bitrus,16.18 Bitrus yana nufin dutse. a kan wannan dutse zan gina ikkilisiyata, kuma ƙofofin Hades16.18 Ko kuwa a lahira ba za su rinjaye ta ba. 19Zan ba ka mabuɗan mulkin sama; kome ka daure a duniya zai zama a daure a sama, kome kuma ka kunce a duniya zai zama a kunce a sama.” 20Sa’an nan ya gargaɗe almajiransa cewa kada su faɗa wa kowa shi ne Kiristi.

Yesu ya yi zancen mutuwarsa

(Markus 8.31–9.1; Luka 9.22-27)

21Tun daga wannan lokaci Yesu ya fara bayyana wa almajiransa cewa dole yă tafi Urushalima yă sha wahaloli da yawa a hannun dattawa, manyan firistoci da kuma malaman dokoki, dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.

22Bitrus ya ja shi gefe ya fara tsawata masa yana cewa, “Sam, Ubangiji! Wannan ba zai taɓa faruwa da kai ba!”

23Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Rabu da ni, Shaiɗan! Kai abin sa tuntuɓe ne a gare ni; ba ka tunanin al’amuran Allah, sai dai al’amuran mutane.”

24Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk mai son bina, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa, yă bi ni. 25Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, zai same shi. 26Me mutum zai amfana in ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa? Ko kuwa me mutum zai bayar a bakin ransa? 27Gama Ɗan Mutum zai zo cikin ɗaukakar Ubansa, tare da mala’ikunsa, sa’an nan zai ba wa kowane mutum lada gwargwadon abin da ya yi.

28“Gaskiya nake gaya muku, akwai waɗansu da suke tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba sai sun ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin mulkinsa.”

Persian Contemporary Bible

متی‌ٰ 16:1-28

درخواست معجزه

1روزی فريسی‌ها و صدوقی‌ها كه سران مذهبی و سياسی قوم بودند، آمدند تا ادعای عيسی را مبنی بر مسيح بودن، بيازمايند. به اين منظور از او خواستند تا معجزه‌ای آسمانی بكند.

2‏-3او جواب داد: «شما خوب می‌توانيد وضع هوا را پيش‌بينی كنيد. اگر عصر، آسمان سرخ باشد، می‌گوييد فردا هوا خوب خواهد بود؛ و اگر صبح، آسمان سرخ باشد، می‌گوييد كه باران خواهد باريد. چگونه اين چيزها را می‌دانيد، اما نمی‌توانيد علائم و نشانه‌های زمانها را درک كنيد؟ 4اين قوم گناهكار و بی‌ايمان معجزهٔ آسمانی می‌خواهند، ولی غير از معجزهٔ يونس، معجزهٔ ديگری به آنان نشان داده نخواهد شد.» اين را گفت و از ايشان جدا شد.

خميرمايه فريسی‌ها و صدوقی‌ها

5وقتی به آن سوس دريا رسيدند، شاگردان متوجه شدند كه فراموش كرده‌اند چيزی برای خوردن بردارند. 6عيسی به ايشان فرمود: «مواظب باشيد و خود را از خميرمايه فريسی‌ها و صدوقی‌ها دور نگه داريد.»

7شاگردان فكر كردند كه گفتهٔ عيسی به اين علت است كه ايشان فراموش كرده‌اند نان بردارند.

8عيسی فكر ايشان را درک كرد و فرمود: «ای كم‌ايمانها! چرا اينقدر غصه می‌خوريد كه نان به همراه نياورده‌ايد؟ 9آيا هنوز هم نمی‌فهميد؟ آيا فراموش كرده‌ايد كه چطور با پنج نان، پنج هزار نفر را سير كردم؟ آن روز چند سبد از خُرده‌ها جمع كرديد؟ 10يا از ياد برده‌ايد كه يكبار ديگر با هفت نان، چهار هزار نفر را سير كردم؟ چند سبد از خُرده‌ها جمع كرديد؟ 11پس چگونه باز فكر می‌كنيد كه من دربارهٔ نان سخن می‌گويم؟ باز هم می‌گويم: از خميرمايهٔ فريسی‌ها و صدوقی‌ها خود را دور نگاه داريد.»

12بالاخره شاگردان فهميدند كه منظور عيسی از «خميرمايه»، همانا تعليمات فريسی‌ها و صدوقی‌ها است.

عقيدهٔ پطرس دربارهٔ شخصيت عيسی

13وقتی عيسی به قيصريهٔ فيليپ رسيد، از شاگردانش پرسيد: «مردم مرا كه می‌دانند؟»

14جواب دادند: «بعضی‌ها می‌گويند كه شما يحيای پيغمبر هستيد؛ عده‌ای نيز می‌گويند الياس، يا ارميا و يا يكی از پيغمبران ديگر می‌باشيد.»

15سپس پرسيد: «شما مرا كه می‌دانيد؟»

16شمعون پطرس جواب داد: «مسيح، فرزند خدای زنده!»

17عيسی فرمود: «ای شمعون، پسر يونا، خوشا به حال تو! زيرا تو اين حقيقت را از انسان نياموختی، بلكه پدر آسمانی من اين را بر تو آشكار ساخته است. 18تو پطرس، يعنی ”سنگ“ هستی، و من بر روی اين صخره، كليسای خود را بنا می‌كنم، و قدرتهای جهنم هرگز قادر به نابودی آن نخواهند بود. 19من كليدهای ملكوت خدا را در اختيار تو می‌گذارم تا هر دری را بر روی زمين ببندی، در آسمان بسته شود، و هر دری را بگشايی در آسمان نيز گشوده شود.»

20آنگاه به شاگردانش دستور داد به كسی نگويند كه او مسيح است.

پيشگويی عيسی دربارهٔ مرگ خويش

21از آن پس، عيسی آشكارا به شاگردانش می‌گفت كه او به اورشليم خواهد رفت و در آنجا سران يهود و علمای مذهبی او را آزار داده، خواهند كشت؛ اما می‌گفت كه روز سوم زنده خواهد شد.

22پطرس او را به كناری كشيده، با مخالفت به او گفت: «سَروَر من، خدا نكند كه چنين اتفاقی برای شما بيفتد.»

23عيسی برگشت و به پطرس فرمود: «دور شو از من ای شيطان! تو دام خطرناكی برای من می‌باشی! فكر تو فكر بشری است نه الهی.»

24آنگاه عيسی به شاگردانش گفت: «هر كه می‌خواهد مريد من باشد، بايد خود را فراموش كند و صليب خود را برداشته، مرا پيروی كند. 25زيرا هر كه بخواهد جان خود را برای خود حفظ كند، آن را از دست خواهد داد؛ اما كسی كه جانش را به خاطر من فدا كند، آن را دوباره به دست خواهد آورد. 26برای شما چه فايده‌ای دارد اگر تمام دنيا را داشته باشيد، ولی زندگی جاويد را از دست بدهيد؟ آيا چيزی پيدا می‌شود كه قدر و قيمتش از زندگی جاويد بيشتر باشد؟ 27زيرا من با فرشتگان خود در شكوه و جلال پدرم خواهم آمد و هر كس را از روی اعمالش داوری خواهم كرد. 28بعضی از كسانی كه در اينجا هستند، پيش از مرگ، مرا در شكوه ملكوتم خواهند ديد.»