Mattiyu 13 – HCB & SNC

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 13:1-58

Misalin mai shuka

(Markus 4.1-9; Luka 8.4-8)

1A ranan nan sai Yesu ya fita daga gida ya je ya zauna a bakin tafkin. 2Taron mutane mai yawan gaske suka taru kewaye da shi har ya kai sai da ya shiga jirgin ruwa ya zauna, yayinda dukan mutane suka tsaya a gaci. 3Sa’an nan ya faɗa musu abubuwa da yawa cikin misalai, yana cewa, “Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa. 4Da yana yafa irin, waɗansu suka fāffāɗi a kan hanya, tsuntsaye kuwa suka zo suka cinye su. 5Waɗansu suka fāɗi a wurare mai duwatsu, inda babu ƙasa sosai, nan da nan kuwa suka tsira, da yake ƙasar ba zurfi. 6Sai dai da rana ta ɗaga, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka kuma yanƙwane domin ba su da saiwa sosai. 7Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya, ƙayan kuwa ta yi girma ta shaƙe su. 8Har yanzu, waɗansu irin suka fāffāɗi a ƙasa mai kyau, inda suka ba da amfani riɓi ɗari, sittin ko kuma talatin na abin da aka shuka. 9Duk mai kunnen ji, yă ji.”

(Markus 4.10-12; Luka 8.9,10)

10Almajiran suka zo wurinsa suka tambaye shi, “Me ya sa kake wa mutane magana da misalai?”

11Ya amsa ya ce, “Sanin asirin mulkin sama kam, ku aka ba wa, amma su ba a ba su ba. 12Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, zai kuwa samu a yalwace. Duk wanda kuma ba shi da shi, ko ɗan abin da yake da shi ma, za a karɓe. 13Abin da ya sa nake musu magana da misalai ke nan.

“Ko da yake suna kallo, ba sa gani;

ko da yake suna saurara, ba sa ji ko su gane.

14A kansu ne aka cika annabcin Ishaya cewa,

“ ‘Za ku yi ta ji amma ba za ku taɓa ganewa ba;

za ku yi ta kallo amma ba za ku taɓa gani ba.

15Gama zuciyar mutanen nan ta taurare;

da ƙyar suke ji da kunnuwansu,

sun kuma rufe idanunsu.

Da ba haka ba, mai yiwuwa su gani da idanunsu,

su kuma ji da kunnuwansu,

su gane a zuciyarsu,

su kuwa juya, in kuma warkar da su.’13.15 Ish 6.9,10

16Amma idanunku masu albarka ne domin suna gani, haka ma kunnuwanku domin suna ji. 17Gama gaskiya nake gaya muku, annabawa da mutane masu adalci da yawa sun yi marmarin ganin abin da kuke gani amma ba su gani ba, su kuma ji abin da kuke ji amma ba su ji ba.

(Markus 4.13-20; Luka 8.11-15)

18“To, ku saurari ma’anar misali na mai shukan nan. 19Duk sa’ad da wani ya ji saƙo game da mulkin bai kuwa fahimce shi ba, mugun nan yakan zo yă ƙwace abin da aka shuka a zuciyarsa. Wannan shi ne irin da ya fāɗi a kan hanya. 20Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a wuraren duwatsu kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, nan da nan kuwa yă karɓe ta da murna. 21Sai dai da yake ba shi da saiwa, yakan ɗan jima kaɗan kawai. Da wata wahala ko tsanani ya auko masa saboda maganar, nan da nan sai yă ja da baya. 22Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi cikin ƙaya kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, sai dai damuwoyin rayuwan nan da jarrabar arzikin duniya sukan shaƙe shi, yă sa maganar ta kāsa amfani. 23Amma wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a ƙasa mai kyau, shi ne mutumin da yakan ji maganar yă kuwa fahimce ta. Yakan ba da amfani wani riɓi ɗari, sittin, ko talatin na abin da aka shuka.”

Misalin ciyayi

24Yesu ya ba su wani misali. “Mulkin sama yana kama da wani da ya shuka iri mai kyau a cikin gonarsa. 25Amma yayinda kowa yake barci, abokin gābansa ya zo ya yafa ciyayi a cikin alkamar, ya tafi abinsa. 26Sa’ad da alkamar ta tashi ta yi kawuna, sai ciyayin ma suka bayyana.

27“Bayin mai gonar suka zo wurinsa suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ashe, ba iri mai kyau ka shuka a gonarka ba? To, ina ciyayin nan suka fito?’

28“Sai ya ce, ‘Abokin gāba ne ya yi wannan.’

“Bayin suka tambaye shi suka ce, ‘Kana so mu je mu tuttumɓuke su?’

29“Ya amsa ya ce, ‘A’a, don kada garin tuttumɓuke ciyayi, ku cire har da alkamar. 30Ku ƙyale su su yi girma tare sai lokacin girbi. A lokacin zan gaya wa masu girbi, da fari ku tara ciyayin ku kuma daure su dami-dami don a ƙone; sa’an nan ku tara alkamar ku kuma kawo su cikin rumbuna.’ ”

Misalai na ƙwayar mustad da na yisti

(Markus 4.30-32; Luka 13.18-21)

31Ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da ƙwayar mustad, wadda mutum ya ɗauka ya shuka a gonarsa. 32Ko da yake ita ce mafi ƙanƙanta cikin ƙwayoyinku, duk da haka sa’ad da ta yi girma, takan zama mafi girma cikin tsire-tsiren lambu ta kuma zama itace, har tsuntsayen sararin sama su zo su yi sheƙa a rassansa.”

33Har yanzu ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da yisti wanda mace ta ɗauka ta kwaɓa garin alkama mai yawa, har sai da yistin ya gauraye yistin duka.”

(Markus 4.33,34)

34Yesu ya faɗa wa taron dukan waɗannan abubuwa cikin misalai; bai faɗa musu kome ba, sai tare da yin amfani da misalai. 35Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta wurin annabi cewa,

“Zan buɗe bakina da misalai,

zan faɗi abubuwan da suke ɓoye tun halittar duniya.”13.35 Zab 78.2

An bayyana misali na ciyayi

36Sa’an nan ya bar taron ya shiga gida. Almajiransa kuwa suka zo wurinsa suka ce, “Bayyana mana misalin ciyayin nan a gona.”

37Ya amsa ya ce, “Mai yafa irin mai kyan nan, shi ne Ɗan Mutum. 38Gonar kuwa ita ce duniya, irin nan mai kyau kuwa suna a matsayin ’ya’yan mulkin. Ciyayin nan kuma su ne ’ya’yan mugun nan, 39abokin gāban da yake shuka su kuwa, Iblis ne. Lokacin girbi kuma shi ne ƙarshen zamani, masu girbin kuwa su ne mala’iku.

40“Kamar yadda aka tattara ciyayin aka kuma ƙone a wuta, haka zai zama a ƙarshen zamani. 41Ɗan Mutum zai aiki mala’ikunsa, su kuwa cire daga mulkinsa kome da yake jawo zunubi da kuma duk masu aikata mugunta. 42Za su jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora. 43Sa’an nan masu adalci za su haskaka kamar rana a mulkin Ubansu. Duk mai kunnen ji, yă ji.”

Misalai na ɓoyayyiyar dukiya da na lu’ulu’u

44“Mulkin sama yana kama da dukiyar da aka ɓoye a gona. Da wani ya same ta, sai yă sāke ɓoye ta, sa’an nan cikin farin cikinsa yă je yă sayar da duk abin da yake da shi yă sayi gonar.

45“Har wa yau dai, mulkin sama yana kama da ɗan kasuwa mai neman lu’ulu’ai masu kyau. 46Da ya sami dutse guda mai daraja sosai, sai ya tafi ya sayar da dukan abin da yake da shi ya saye shi.

Misalin taru

47“Har yanzu, mulkin sama yana kama da abin kamun kifin da aka jefa cikin tafki yă kamo kifi iri-iri. 48Da abin kamun kifi ya cika, masuntan suka jawo shi gaci. Sai suka zauna suka tattara kifi masu kyau a kwanduna, amma suka zubar da marasa kyau. 49Haka zai kasance a ƙarshen zamani. Mala’iku za su zo su ware masu mugunta daga masu adalci 50su kuma jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”

51Yesu ya tambaye su ya ce, “Kun gane dukan waɗannan abubuwa?”

Suka amsa, “I.”

52Sa’an nan ya ce musu, “Saboda haka duk malamin dokokin da ya horu game da koyarwar mulkin sama, yana kama da maigida wanda yakan fitar daga ɗakin ajiyarsa sababbin dukiya da kuma tsofaffi.”

Rashin ganin darajar annabi

(Markus 6.1-6; Luka 4.16-30)

53Sa’ad da Yesu ya gama ba da waɗannan misalai, sai ya ci gaba daga can. 54Yana isowa garinsa, sai ya fara koya wa mutane a cikin majami’arsu, suka kuwa yi mamaki. Suka yi ta tambaya suna cewa, “Ina wannan mutum ya sami irin wannan hikima da kuma ayyukan banmamaki haka? 55Wannan ba shi ne ɗan kafinta nan ba? Ba mahaifiyarsa ba ce Maryamu, ’yan’uwansa kuma Yaƙub, Yusuf, Siman da Yahuda ba? 56Duk ’yan’uwansa mata kuma ba tare da mu suke ba? To, a ina wannan mutum ya sami dukan waɗannan abubuwa?” 57Sai suka ji haushinsa.

Amma Yesu ya ce musu, “Sai a garinsa da kuma a gidansa na kaɗai annabi ba ya samun girma.”

58Bai kuwa yi abubuwan banmamaki da yawa a can ba saboda rashin bangaskiyarsu.

Slovo na cestu

Matouš 13:1-58

Ježíš vypráví podobenství o rozsévači

1Téhož dne vyšel Ježíš z domu a usedl na břehu jezera. 2Zanedlouho se kolem něho shromáždilo tolik lidí, že musel vstoupit do loďky, aby je mohl všechny oslovit.

3Rád vyjadřoval duchovní pravdy obrazně.

Tentokrát začal vyprávět:

4„Rolník zaséval na poli obilí. Některá zrna padla na okraj cesty. Slétli se ptáci a sezobali je. 5Jiná zrna dopadla na skalnatou zem, kde bylo málo ornice. Obilí rychle vyhnalo do výšky, 6ale když začalo pálit slunce, uschlo, protože kořínky nešly do hloubky. 7Další část zrna zapadla mezi bodláky. Když vyrostlo bodláčí, udusilo klásky. 8Ostatní zrna padla do dobré ornice. Vyrostlo obilí a přineslo úrodu. Některý klas měl sto zrnek, jiný šedesát a jiný třicet. 9Víte, co tím myslím?“

Ježíš vysvětluje podobenství o rozsévači

10Učedníci se ho zeptali: „Proč mluvíš v obrazech?“ 11Vysvětlil jim to: „Vám už Bůh odkrývá svoje záměry se světem. Ostatním je to zatím skryto. 12Kdo přijímá ochotně, bude mít stále víc. Kdo je spokojen s tím, co má, přijde nakonec o všechno. 13Používám obrazy, lidé slyší i vidí, a přece nechápou.

14Tak se na nich plní Izajášovo proroctví:

‚Budete poslouchat,

ale neporozumíte,

budete se dívat,

ale neuvidíte.

15Protože srdce tohoto lidu otupělo,

jsou hluší a zavřeli oči,

aby neviděli,

neslyšeli a neporozuměli,

aby se neobrátili k Bohu,

kde by mohli být uzdraveni.‘

16Jak je dobře, že vaše oči vidí a uši slyší. 17Mnoho proroků toužilo vidět to, co vy vidíte, a slyšet to, co vy slyšíte, ale nebylo jim to dopřáno.

18A teď k tomu příběhu o rozsévači. 19Cesta, kam padla některá zrna, představuje srdce lidí, kteří slyší o Božím království a nezajímá je to. Přichází satan a sebere, co bylo zaseto. 20-21Skalnatá země představuje srdce člověka, který slyší Boží poselství a přijímá je sice s velkou radostí, ale povrchně a ono v něm nezapustí kořeny. Když pak přijdou těžkosti nebo pronásledování pro víru, jeho nadšení ochabne a to, co bylo zaseto, zmizí.

22Země porostlá bodláčím představuje člověka, který slyší poselství, ale v jehož srdci záležitosti každodenního života a touha po lepším hmotném zajištění slovo udusí.

23Dobrá ornice představuje srdce člověka, který slyší Boží poselství, rozumí mu a nechává působit jeho životodárný vliv. Užitek z toho je mnohonásobný, u někoho větší, u jiného menší.“

Ježíš vypráví podobenství o plevelu

24Potom použil dalšího přirovnání. „Bůh je jako dobrý hospodář, který zasel na své pole dobré semeno. 25V noci, když lidé spali, hospodářův nepřítel rozhodil mezi pšenici semeno plevele. 26-27Když vyrostlo obilí a s ním i plevel, přišli služebníci za hospodářem a řekli mu: ‚Vždyť jsi zasel dobré semeno, kde se tedy vzal plevel?‘

28‚To udělal nepřítel!‘ odpověděl.

‚My půjdeme a vyplejeme to pole,‘ nabídli se.

29Ten jim na to řekl: ‚Ne, to nedělejte. Spolu s plevelem byste mohli snadno vytrhnout i pšenici. 30Necháme obojí vyrůst a při žních řeknu žencům, aby vybrali plevel a spálili ho a pšenici dali do mé stodoly.‘ “

Ježíš vypráví podobenství o hořčičném zrnu

31Předložil jim jiný obraz: „S Božím dílem je to jako s hořčičným seménkem, které člověk zasel na poli. 32Je sice drobné, ale vyroste z něho tak mohutná bylina, že i ptáci na ní stavějí hnízda.“

33Dále užil tohoto obrazu: „Boží vliv působí jako kvas. Malé množství prokvasí i velkou dávku těsta.“

34V tomto kázání Ježíš používal výhradně podobenství.

35Tak se naplnilo staré proroctví:

„Budu mluvit v obrazech

a vypovím,

co bylo skryto od stvoření světa.“

Ježíš vysvětluje podobenství o plevelu

36Ježíš pak opustil shromážděné posluchače a šel domů. Obklopili ho jeho učedníci a žádali, aby jim vyložil obraz plevele na poli. 37„Dobře,“ řekl, „já jsem ten hospodář, který seje dobré zrní. 38Pole představuje svět a zrna, to jsou lidé, kteří patří Bohu. Plevel, to jsou lidé propadlí zlému. 39Nepřítel, který ho zasel, je ďábel. Žně představují konec světa a ženci jsou andělé. 40Tak jako v tomto příběhu je plevel oddělen a spálen, tak bude na konci světa. 41Pošlu své anděly a ti vyženou z Boží blízkosti všechny, kteří stáli v cestě Boží věci a páchali zlo. 42Jejich konec bude hrozný. Zbyde jim pláč a zoufalství. 43A tehdy ti, kteří plnili Boží vůli, budou v království nebeského Otce zářit jako slunce. Přemýšlejte o tom!

Ježíš vypráví podobenství o pokladu, perle a síti

44Nový život, k němuž vás Bůh volá, je jako poklad zakopaný v poli. Kdo ho najde, zatím o tom nemluví, ale má takovou radost, že prodá všechno, jen aby to pole získal.

45-46Nebo: je jako drahocenná perla, kterou objeví obchodník s perlami. Vyprodá všechno, co má, a koupí ji.

47Boží království je jako síť spuštěná do moře, ve které uváznou nejrůznější tvorové. 48Když je síť plná, vytáhnou ji rybáři na břeh, do košů vyberou dobré ryby a ostatní vyhodí. 49Tak to bude i na konci světa. Přijdou Boží andělé a oddělí zlé od bohabojných 50a zlé hodí do ohně. Tam bude pláč a zoufalství. 51Porozuměli jste všemu?“

„Ano,“ odpověděli. 52Potom dodal: „Každý vykladač Písma, který pochopil, oč mi jde, je jako hospodář, který ze své zásobárny nabízí nové i staré.“

Lidé z Nazaretu odmítají uvěřit

53-54Když Ježíš skončil svůj výklad v podobenstvích, vrátil se do svého domovského města. Učil v tamní synagoze. Všichni se divili: „Kde se v něm bere taková moudrost a moc? 55Vždyť to je tesařův syn, jeho matka je přece Marie, a Jakub, Josef, Šimon a Juda to jsou jeho bratři! 56I jeho sestry žijí mezi námi. Odkud to ten člověk má?“ 57-58Nemohli se s tím vyrovnat a pro jejich nedůvěru tam Ježíš nemohl vykonat mnoho zázraků. Vysvětlil to slovy: „Proroka si váží všude víc než v jeho rodném městě a v jeho domově!“