Mattiyu 12 – HCB & NIRV

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 12:1-50

Ubangijin Asabbaci

(Markus 2.23-28; Luka 6.1-5)

1A lokacin nan Yesu ya bi ta gonakin hatsi a ranar Asabbaci. Almajiransa kuwa suna jin yunwa, sai suka fara kakkarya kan hatsi suna ci. 2Sa’ad da Farisiyawa suka ga wannan, sai suka ce masa, “Duba! Almajiranka suna yin abin da doka ta hana a yi a ranar Asabbaci.”

3Sai ya amsa ya ce, “Ba ku karanta abin da Dawuda ya yi ba ne sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa? 4Ya shiga gidan Allah, da shi da abokan tafiyarsa suka ci keɓaɓɓen burodin, wanda doka ta hana su yi, sai firistoci kaɗai. 5Ko kuwa ba ku karanta a Doka cewa a ranar Asabbaci firistoci sukan karya dokar Asabbaci duk da haka ba da yin wani laifi ba? 6Ina faɗa muku cewa wani12.6 Ko kuwa a wani abu; haka ma a ayoyi 41 da 42 wanda ya fi haikali yana a nan. 7Da a ce kun san abin da waɗannan kalmomi suke nufi, ‘Jinƙai nake bukata, ba hadaya ba,’12.7 Hos 6.6 da ba ku zargi marar laifi ba. 8Gama Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabbaci.”

(Markus 3.1-6; Luka 6.6-11)

9Da ya ci gaba daga wurin, sai ya shiga majami’arsu, 10a nan kuwa akwai wani mutum mai shanyayyen hannu. Don neman dalili su zargi Yesu, sai suka tambaye shi suka ce, “Ya dace a warkar a ranar Asabbaci?”

11Ya ce musu, “In waninku yana da tunkiya, ta kuma fāɗa a rami ran Asabbaci, ba zai cire ta daga ramin ba? 12Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja! Saboda haka ya dace a aikata alheri ran Asabbaci.”

13Sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙa hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye, kamar dai ɗayan. 14Amma Farisiyawa suka fita suka ƙulla shawara yadda za su kashe Yesu.

Zaɓaɓɓen bawan Allah

15Da ya gane wannan, sai Yesu ya janye daga wurin. Da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da dukan masu ciwonsu, 16yana jan musu kunne kada su faɗa wa kowa akan ko shi wane ne. 17Wannan kuwa domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya ne cewa,

18“Ga bawana da na zaɓa,

ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi;

zan sa Ruhuna a kansa,

zai kuma yi shelar adalci ga al’ummai.

19Ba zai yi faɗa ko yă ɗaga murya ba,

ba kuwa wanda zai ji muryarsa a kan tituna.

20Kyauron da ya tanƙwasa ba zai karye shi ba.

Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba,

sai ya jagoranci adalci zuwa ga nasara.

21Cikin sunansa al’ummai za su dogara.”12.21 Ish 42.1-4

Yesu da Be’elzebub

(Markus 3.20-30; Luka 11.14-23; 12.10)

22Sai aka kawo masa wani bebe kuma makaho mai aljani, Yesu kuwa ya warkar da shi, har ya iya magana ya kuma sami ganin gari. 23Dukan mutane suka yi mamaki, suka ce, “Wannan Ɗan Dawuda ne kuwa?”

24Amma da Farisiyawa suka ji haka, sai suka ce, “Ahab, da Be’elzebub12.24 Da Girik Be’elzebul Ko kuwa Be’elzebul; haka ma a aya 27 sarkin aljanu ne kaɗai, wannan mutum yake fitar da aljanu.”

25Yesu kuwa ya san tunaninsu sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa zai lalace, kuma duk birni ko gidan da yake rabe gāba da kansa ba zai ɗore ba. 26In Shaiɗan yana fitar da Shaiɗan, ai, ya rabu yana gāba da kansa ke nan. Yaya kuwa mulkinsa zai ɗore? 27In kuwa ta wurin Be’elzebub nake fitar da aljanu, to, ta wa mutanenku suke fitar da su? Saboda haka, su ne za su zama alƙalanku. 28Amma in ina fitar da aljanu ta wurin Ruhun Allah ne, to, fa, mulkin Allah ya zo muku ke nan.

29“Ko kuwa, yaya wani zai iya shiga gidan mai ƙarfi yă ƙwace masa kaya ba tare da ya fara daure mai ƙarfin nan tukuna ba? Sa’an nan zai iya washe gidansa.

30“Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni ne, kuma wanda ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi. 31Saboda haka ina gaya muku, za a gafarta wa mutane kowane zunubi da kuma saɓo, amma saɓo game da Ruhu, ba za a gafarta ba. 32Duk wanda ya zargi Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya zargi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, ko a wannan zamani ko a zamani mai zuwa.

(Luka 6.43-45)

33“Itace mai kyau, yakan ba da ’ya’ya masu kyau. Itace marar kyau kuma, yakan ba da ’ya’ya marasa kyau. Itace dai, da irin ’ya’yansa ne ake gane shi. 34Ku macizai, ta yaya ku da kuke mugaye za ku iya magana kirki? Gama daga baki, mutum yakan faɗi abin da yake cikin zuciya. 35Mutumin kirki yakan fito da abubuwa masu kyau daga ajiyar da aka a yi cikinsa, mugun mutum kuwa yakan fito da mugayen abubuwa daga cikin muguntar da aka yi ajiya a cikinsa. 36Amma ina gaya muku cewa mutane za su ba da lissafi a ranar shari’a a kan kowace kalmar banza da suka faɗa. 37Gama ta wurin kalmominka za a kuɓutar da kai, kuma ta wurin kalmominka za a hukunta ka.”

Alamar Yunana

(Markus 8.11,12; Luka 11.29-32)

38Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka ce masa, “Malam, muna so mu ga wata alama mai banmamaki daga gare ka.”

39Sai ya amsa ya ce, “Mugaye da masu zinan zamanin nan suna neman wata alama mai banmamaki! Amma babu wadda za a nuna musu, sai dai alama ta annabi Yunana. 40Gama kamar yadda Yunana ya yi yini uku da kuma dare uku a cikin wani babban kifi, haka Ɗan Mutum zai yi yini uku da kuma dare uku a cikin ƙasa. 41Mutanen Ninebe za su tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, su kuwa hukunta shi; don sun tuba saboda wa’azin Yunana, yanzu kuwa ga wanda ya fi Yunana girma a nan. 42Sarauniyar Sheba za tă tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, tă kuwa hukunta shi; don ta zo daga ƙarshen duniya, ta saurari hikimar Solomon, yanzu kuwa ga wanda ya fi Solomon girma a nan.

(Luka 11.24-26)

43“Sa’ad da mugun ruhu ya fita daga mutum, yakan bi wuraren da ba ruwa yana neman hutu, ba ya kuwa samu. 44Sa’an nan yakan ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’ Sa’ad da ya iso, ya tarar da gidan ba kowa a ciki, shararre, kuma a kintse. 45Sai yă je yă ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, su kuwa zo su shiga su zauna a can. Ƙarshen mutumin nan fa zai fi farkonsa muni. Haka zai zama ga wannan mugun zamani.”

Mahaifiyar Yesu da ’yan’uwansa

(Markus 3.31-35; Luka 8.19-21)

46Yayinda Yesu yake cikin magana da taron, sai ga mahaifiyarsa da ’yan’uwansa tsaye a waje, suna so su yi magana da shi. 47Wani ya ce masa, “Mahaifiyarka da ’yan’uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai.”12.47 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā ba su da aya 47.

48Ya amsa masa ya ce, “Wace ce mahaifiyata, su wane ne kuma ’yan’uwana?” 49Sai ya miƙa hannu wajen almajiransa ya ce, “Ga mahaifiyata da kuma ’yan’uwana. 50Ai, duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda yake cikin sama, shi ne ɗan’uwana da ’yar’uwata da kuma mahaifiyata.”

New International Reader’s Version

Matthew 12:1-50

Jesus Is Lord of the Sabbath Day

1One Sabbath day Jesus walked through the grainfields. His disciples were hungry. So they began to break off some heads of grain and eat them. 2The Pharisees saw this. They said to Jesus, “Look! It is against the Law to do this on the Sabbath day. But your disciples are doing it anyway!”

3Jesus answered, “Haven’t you read about what David did? He and his men were hungry. 4So he entered the house of God. He and his men ate the holy bread. Only priests were allowed to eat it. 5Haven’t you read the Law? It tells how every Sabbath day the priests in the temple have to do their work on that day. But they are not considered guilty. 6I tell you that something more important than the temple is here. 7Scripture says, ‘I want mercy and not sacrifice.’ (Hosea 6:6) You don’t know what those words mean. If you did, you would not bring charges against those who are not guilty. 8The Son of Man is Lord of the Sabbath day.”

9Going on from that place, Jesus went into their synagogue. 10A man with a weak and twisted hand was there. The Pharisees were trying to accuse Jesus of a crime. So they asked him, “Does the Law allow us to heal on the Sabbath day?”

11He said to them, “What if one of your sheep falls into a pit on the Sabbath day? Won’t you take hold of it and lift it out? 12A person is worth more than sheep! So the Law allows us to do good on the Sabbath day.”

13Then Jesus said to the man, “Stretch out your hand.” So he stretched it out. It had been made as good as new. It was just as good as the other hand. 14But the Pharisees went out and planned how to kill Jesus.

God’s Chosen Servant

15Jesus knew all about the Pharisees’ plans. So he left that place. A large crowd followed him, and he healed all who were sick. 16But he warned them not to tell other people about him. 17This was to make what was spoken through the prophet Isaiah come true. It says,

18“Here is my servant. I have chosen him.

He is the one I love. I am very pleased with him.

I will put my Spirit on him.

He will announce to the nations that everything will be made right.

19He will not argue or cry out.

No one will hear his voice in the streets.

20He will not break a bent twig.

He will not put out a dimly burning flame.

He will make right win over wrong.

21The nations will put their hope in him.” (Isaiah 42:1–4)

Jesus and Beelzebul

22A man controlled by demons was brought to Jesus. The man was blind and could not speak. Jesus healed him. Then the man could speak and see. 23All the people were amazed. They said, “Could this be the Son of David?”

24The Pharisees heard this. So they said, “This fellow drives out demons by the power of Beelzebul, the prince of demons.”

25Jesus knew what they were thinking. So he said to them, “Every kingdom that fights against itself will be destroyed. Every city or family that is divided against itself will not stand. 26If Satan drives out Satan, he fights against himself. Then how can his kingdom stand? 27You say I drive out demons by the power of Beelzebul. Then by whose power do your people drive them out? So then, they will be your judges. 28But suppose I drive out demons by the Spirit of God. Then the kingdom of God has come to you.

29“Or think about this. How can you enter a strong man’s house and just take what the man owns? You must first tie him up. Then you can rob his house.

30“Anyone who is not with me is against me. Anyone who does not gather sheep with me scatters them. 31So here is what I tell you. Every kind of sin and every evil word spoken against God will be forgiven. But speaking evil things against the Holy Spirit will not be forgiven. 32Anyone who speaks a word against the Son of Man will be forgiven. But anyone who speaks against the Holy Spirit will not be forgiven. A person like that won’t be forgiven either now or in days to come.

33“If you make a tree good, its fruit will be good. If you make a tree bad, its fruit will be bad. You can tell a tree by its fruit. 34You nest of poisonous snakes! How can you who are evil say anything good? Your mouths say everything that is in your hearts. 35A good man says good things. These come from the good that is stored up inside him. An evil man says evil things. These come from the evil that is stored up inside him. 36But here is what I tell you. On judgment day, everyone will have to account for every empty word they have spoken. 37By your words you will be found guilty or not guilty.”

The Sign of Jonah

38Some of the Pharisees and the teachers of the law came to Jesus. They said, “Teacher, we want to see a sign from you.”

39He answered, “Evil and unfaithful people ask for a sign! But none will be given except the sign of the prophet Jonah. 40Jonah was in the belly of a huge fish for three days and three nights. Something like that will happen to the Son of Man. He will spend three days and three nights in the grave. 41The men of Nineveh will stand up on judgment day with the people now living. And the Ninevites will prove that these people are guilty. The men of Nineveh turned away from their sins when Jonah preached to them. And now something more important than Jonah is here. 42The Queen of the South will stand up on judgment day with the people now living. And she will prove that they are guilty. She came from very far away to listen to Solomon’s wisdom. And now something more important than Solomon is here.

43“What happens when an evil spirit comes out of a person? It goes through dry areas looking for a place to rest. But it doesn’t find it. 44Then it says, ‘I will return to the house I left.’ When it arrives there, it finds the house empty. The house has been swept clean and put in order. 45Then the evil spirit goes and takes with it seven other spirits more evil than itself. They go in and live there. That person is worse off than before. That is how it will be with the evil people of today.”

Jesus’ Mother and Brothers

46While Jesus was still talking to the crowd, his mother and brothers stood outside. They wanted to speak to him. 47Someone told him, “Your mother and brothers are standing outside. They want to speak to you.”

48Jesus replied to him, “Who is my mother? And who are my brothers?” 49Jesus pointed to his disciples. He said, “Here is my mother! Here are my brothers! 50Anyone who does what my Father in heaven wants is my brother or sister or mother.”