Markus 1 – HCB & NRT

Hausa Contemporary Bible

Markus 1:1-45

Yohanna Mai Baftisma ya shirya hanya

(Mattiyu 3.1-12; Luka 3.1-18; Yohanna 1.19-28)

1Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.1.1 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā ba su da Ɗan Allah. 2An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa,

“Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka,

wanda zai shirya hanyarka,”1.2 Mal 3.1

3“muryar mai kira a hamada tana cewa,

‘Ku shirya wa Ubangiji hanya,

ku miƙe hanyoyi dominsa.’ ”1.3 Ish 40.3

4Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai. 5Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun. 6Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji. 7Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba. 8Ina muku baftisma da1.8 Ko kuwa a cikin ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”

Baftisma da kuma gwajin Yesu

(Mattiyu 3.13-17; Luka 3.21,22)

9A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun. 10Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya. 11Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”

12Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada, 13ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.

Kiran Almajirai na farko

(Mattiyu 4.12-17; Luka 4.14,15)

14Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah. 15Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”

(Mattiyu 4.18-22; Luka 5.1-11)

16Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne. 17Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.” 18Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.

19Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu. 20Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da ’yan haya, suka kuwa bi shi.

Yesu ya fitar da mugun ruhu

(Luka 4.31-37)

21Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa. 22Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba. 23Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce, 24“Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”

25Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!” 26Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.

27Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.” 28Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.

Yesu ya warkar da mutane da yawa

(Mattiyu 8.14-17; Luka 4.38-41)

29Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna. 30Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita. 31Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.

32A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu. 33Duk garin ya taru a ƙofar gidan. 34Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.

Yesu ya yi addu’a a wurin da ba kowa

35Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a. 36Siman da abokansa suka fita nemansa. 37Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”

38Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.” 39Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.

Mutum mai kuturta

(Mattiyu 8.1-4; Luka 5.12-16)

40Wani mutum mai kuturta1.40 Kalmar Girik da aka yi amfani da ita don kowace irin cutar da ta shafi fatar jiki ba lalle sai kuturta ba. ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”

41Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!” 42Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.

43Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa, 44“Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.” 45A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.

New Russian Translation

Марка 1:1-45

Иоанн Креститель готовит путь Иисусу

(Мат. 3:1-12; Лк. 3:2-16; Ин. 1:19-28)

1Вот начало Радостной Вести1:1 Букв.: «Евангелия». об Иисусе Христе, Сыне Бога. 2Как написано у пророка Исаии:

«Вот, Я посылаю перед Тобой Моего вестника,

который приготовит Тебе путь»1:2 См. Мал. 3:1..

3«Голос раздается в пустыне:

„Приготовьте путь Господу1:3 Слово, стоящее в греческом тексте, является переводом еврейского «ЙГВГ» (Ис. 40:3). Это имя, под которым Бог открылся Моисею и народу Израиля (см. Исх. 3:13-15). Оно переводится как «Он Есть», показывая неизменность Его природы и характера (см. Пс. 101:26-28).,

сделайте прямыми дороги Его!“»1:3 Ис. 40:3.

4В пустыне появился Иоанн Креститель и проповедовал крещение в знак покаяния для прощения грехов. 5К нему приходили люди со всей Иудеи и все жители Иерусалима. Они исповедовали свои грехи, и Иоанн крестил их в реке Иордане. 6Иоанн носил одежду из верблюжьей шерсти и подпоясывался кожаным поясом. Ел он саранчу и дикий мед. 7В своей проповеди он говорил:

– После меня придет Тот, Кто могущественнее меня, и я даже не достоин, нагнувшись, развязать ремни Его сандалий. 8Я крестил вас водой, а Он будет крестить вас Святым Духом.

Иоанн крестит Иисуса

(Мат. 3:13-17; Лк. 3:21-22; Ин. 1:32-34)

9В то время из галилейского города Назарета пришел Иисус и тоже был крещен Иоанном в Иордане. 10И когда Иисус выходил из воды, Он тотчас увидел раскрывшиеся небеса и Духа, спускающегося на Него в образе голубя. 11И с небес прозвучал голос:

– Ты Мой любимый Сын! В Тебе Моя радость!

Сатана искушает Иисуса в пустыне

(Мат. 4:1-11; Лк. 4:1-13)

12Тотчас Дух побудил Иисуса пойти в пустыню. 13Он находился в пустыне сорок дней, искушаемый сатаной. Иисус был там один, в окружении диких зверей, и ангелы служили Ему.

Иисус начинает Свое служение

(Мат. 4:12-17; Лк. 4:14-15)

14После того как Иоанн был арестован, Иисус пришел в Галилею, возвещая Радостную Весть от Бога.

15– Пришло время, – говорил Он, – Царство Божье уже близко! Покайтесь и верьте в Радостную Весть!

Четыре рыбака следуют за Иисусом

(Мат. 4:18-22; Лк. 5:2-11; Ин. 1:35-42)

16Однажды, проходя вдоль Галилейского озера, Иисус увидел Симона и его брата Андрея. Они забрасывали в озеро сети, так как были рыбаками.

17– Идите за Мной, – сказал им Иисус, – и Я сделаю вас ловцами людей.

18Братья сразу же оставили сети и пошли за Ним. 19Пройдя немного дальше, Он увидел Иакова и Иоанна, сыновей Зеведея, которые сидели в лодке и чинили сети. 20И Он сразу же позвал их, и они, оставив своего отца Зеведея с наемными работниками в лодке, пошли за Ним.

Иисус изгоняет нечистого духа

(Лк. 4:31-37)

21Когда они пришли в Капернаум, Иисус в первую же субботу пошел в синагогу и учил там. 22Люди изумлялись Его учению, потому что Он учил их как имеющий власть, а не как учители Закона. 23Как раз в это время в синагоге находился человек, одержимый нечистым духом, который вдруг закричал:

24– Что Ты хочешь от нас, Иисус из Назарета? Ты пришел, чтобы погубить нас? Я знаю, Кто Ты! Ты – Святой Божий!

25– Замолчи! – строго приказал Иисус. – Выйди из него!

26Нечистый дух сотряс человека и с громким криком вышел из него. 27Люди в изумлении говорили друг другу:

– Что это? Новое учение, да еще и с такой властью! Он даже нечистым духам приказывает, и те подчиняются Ему!

28Слух об Иисусе мгновенно разошелся по всей Галилее.

Иисус исцеляет больных

(Мат. 8:14-16; Лк. 4:38-41)

29Из синагоги они с Иаковом и Иоанном сразу же пошли домой к Симону и Андрею. 30Теща Симона лежала в горячке, и Иисусу сразу сказали о ней. 31Он подошел к ней, взял ее за руку и помог подняться. Жар ее прошел, и она начала накрывать им на стол.

32С наступлением вечера, после захода солнца, к Иисусу стали приносить всех больных и одержимых демонами. 33Весь город собрался у дверей. 34В тот день Иисус исцелил многих от самых различных болезней и изгнал много демонов. Демонам Он запрещал говорить, потому что они знали, Кто Он.

Иисус проповедует в Галилее

(Лк. 4:42-44)

35На следующее утро, когда было еще темно, Иисус вышел из дома, пошел в безлюдное место и там молился. 36Симон и другие ученики бросились искать Его 37и, когда нашли, сказали Ему:

– Все Тебя ищут!

38А Он им ответил:

– Пойдем в другие места, в соседние селения, чтобы Мне и там проповедовать Радостную Весть, Я ведь для этого и пришел.

39И Он ходил по всей Галилее, проповедуя в синагогах и изгоняя демонов.

Иисус исцеляет прокаженного

(Мат. 8:2-4; Лк. 5:12-16)

40Однажды к Нему подошел человек, больной проказой. Упав перед Иисусом на колени, он стал умолять Его:

– Если Ты захочешь, Ты можешь меня очистить.

41Иисусу стало жаль его. Он протянул руку, прикоснулся к нему и сказал:

– Хочу, очистись!

42Как только Он это сказал, проказа сошла с человека, и тот стал чистым. 43Иисус тут же отослал его, строго предупредив:

44– Смотри, никому не говори об этом, но пойди, покажись священнику и принеси в жертву за очищение то, что повелел Моисей1:44 См. Лев. 14:1-32.. Так твое исцеление будет удостоверено перед людьми.

45Но тот пошел и начал повсюду рассказывать о случившемся. Из-за этого Иисусу стало невозможно открыто появляться в городе, и Он оставался в безлюдных местах. Народ, однако, стекался к Нему отовсюду.