Luka 1 – HCB & HHH

Hausa Contemporary Bible

Luka 1:1-80

Gabatarwa

1Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu, 2kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara. 3Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus, 4don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.

An yi faɗar haihuwar Yohanna Mai Baftisma

5A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma ’yar zuriyar Haruna ce. 6Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi. 7Sai dai ba su da ’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.

8Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah, 9sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare. 10Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.

11Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare. 12Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi. 13Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna. 14Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa, 15gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa. 16Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu. 17Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga ’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”

18Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”

19Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi. 20Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”

21Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali. 22Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.

23Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida. 24Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar. 25Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”

Annabcin haihuwar Yesu

26A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili, 27gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu. 28Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”

29Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka? 30Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah. 31Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu. 32Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda, 33zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.”

34Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”

35Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi1.35 Ko kuwa Saboda haka, yaron da za a haifa za a kira shi mai tsarki Ɗan Allah. 36’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida. 37Gama ba abin da zai gagari Allah.”

38Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.

Maryamu ta ziyarci Elizabet

39A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya, 40inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet. 41Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki. 42Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa! 43Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina? 44Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna. 45Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”

Waƙar Maryamu

46Sai Maryamu ta ce,

“Raina yana ɗaukaka Ubangiji

47ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,

48gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa.

Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,

49gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa,

sunansa labudda Mai Tsarki ne.

50Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa,

daga zamani zuwa zamani.

51Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa;

ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.

52Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu

amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.

53Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa

amma ya sallami mawadata hannu wofi.

54Ya taimaki bawansa Isra’ila,

yana tunawa yă nuna jinƙai

55ga Ibrahim da zuriyarsa har abada,

kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.”

56Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.

Haihuwar Yohanna Mai Baftisma

57Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa. 58Maƙwabtanta da ’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.

59A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne, 60amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”

61Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”

62Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron. 63Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki. 64Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah. 65Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya. 66Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.

Waƙar Zakariya

67Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,

68“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila,

domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.

69Ya tā mana ƙahon ceto

a gidan bawansa Dawuda

70(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki),

71cewa zai cece mu daga abokan gābanmu

daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu

72don yă nuna jinƙai ga kakanninmu,

yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,

73rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,

74don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu,

yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,

75cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.

76“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki;

gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,

77don ka sanar da mutanensa ceto,

ta wurin gafarar zunubansu,

78saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna,

hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,

79don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu,

da kuma cikin inuwar mutuwa,

don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”

80Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

Habrit Hakhadasha/Haderekh

הבשורה על-פי לוקס 1:1-80

1תאופילוס היקר, אנשים רבים כבר כתבו על הדברים שהתרחשו בינינו, 2על־פי סיפוריהם של תלמידי ישוע ושל עדי ראייה אחרים. 3גם אני חקרתי היטב את התרחשות הדברים מתחילתם, והחלטתי כי טוב שאכתוב לך אותם לפי סדר העניינים, 4כדי שיהיה לך מידע מדויק על הנושא שלמדת.

5בימי הורדוס מלך יהודה היה בארץ כהן בשם זכריה, אשר היה שייך למחלקת אביה1‏.5 א 5 הכוהנים הרבים במקדש חולקו לעשרים־וארבע מחלקות (ראה דברי הימים א פרק כד). כל מחלקה שרתה בתורנות פעמיים בשנה למשך שבוע בכל פעם. מחלקת אביה הייתה המחלקה השמינית. – ממשרתי בית־המקדש. גם אשתו אלישבע הייתה ממשפחה כוהנית. 6זכריה ואלישבע היו אנשים צדיקים, אשר אהבו את ה׳ ושמרו את כל מצוותיו וחוקותיו. 7אולם לא היו להם ילדים, כי אלישבע הייתה עקרה, ושניהם כבר היו זקנים.

8‏-9יום אחד, כאשר הייתה מחלקתו של זכריה בתורנות בבית־המקדש, נפל בגורלו להיכנס אל היכל ה׳ ולהקטיר קטורת. 10בינתיים עמד כל העם בחוץ והתפלל, כנהוג בעת הקטרת הקטורת.

11לפתע נראה מלאך ה׳ אל זכריה מימין למזבח הקטורת. 12זכריה נבהל ונמלא פחד.

13”אל תירא, זכריה“, הרגיע אותו המלאך. ”באתי לבשר לך שאלוהים שמע את תפילתך, ושאשתך אלישבע תלד לך בן! עליך לקרוא לו ’יוחנן‘. 14לידתו תביא לכם שמחה ואושר, ואנשים רבים ישמחו יחד אתכם, 15כי ה׳ הועיד אותו לגדולות. עליו להינזר מיין ומשקאות חריפים, והוא יימלא ברוח הקודש מעת לידתו. 16יוחנן ישיב רבים מעם ישראל אל ה׳ אלוהיהם. 17הוא ילך לפני ה׳ ברוחו ובגבורתו של אליהו הנביא, ישלים בין אבות לבנים, וישיב את המרדנים לדרך הצדקה והתבונה. אכן, הוא יכין את העם לבואו של האדון.“ 18”כיצד אדע שדבריך נכונים?“ שאל זכריה. ”הלא אדם זקן אני, וגם אשתי כבר זקנה.“

19”אני המלאך גבריאל!“ השיב המלאך. ”אני עומד לפני אלוהים, והוא אשר שלח אותי לבשר לך את ההודעה הזאת. 20דע לך כי כל אשר אמרתי יתקיים בבוא הזמן, אולם מאחר שלא האמנת לדברי, לא תוכל להוציא מילה מפיך מרגע זה ועד שיתקיימו דברי!“

21האנשים אשר התפללו בחוץ המתינו בינתיים לזכריה, ולא הבינו מדוע התעכב. 22לבסוף, כשיצא זכריה החוצה הוא לא יכול היה לדבר אל העם, אולם מסימני ידיים הבינו האנשים שראה חזיון. 23זכריה נשאר בבית־המקדש עד תום ימי התורנות של מחלקתו, ולאחר מכן שב לביתו.

24כעבור זמן קצר הרתה אלישבע אשתו והסתתרה מעיני הציבור כחמישה חודשים.

25”מה טוב הוא אלוהים!“ קראה אלישבע בשמחה רבה. ”ברחמיו הרבים הוא הסיר את חרפת עקרותי!“

26בחודש השישי להריונה של אלישבע שלח אלוהים את המלאך גבריאל אל העיר נצרת שבגליל, 27אל נערה בתולה בשם מרים, ארוסתו של יוסף משושלת בית־דוד.

28גבריאל נגלה אל מרים ואמר לה: ”שלום לך, אשת חן, ה׳ עמך!“

29מרים נבהלה לרגע; דברי המלאך הביכו אותה, והיא ניסתה לנחש בלבה למה הוא התכוון.

30”אל תפחדי, מרים,“ הרגיע אותה המלאך, ”כי מצאת חן בעיני אלוהים והוא החליט לברך אותך. 31בעוד זמן קצר תיכנסי להריון ותלדי בן. בשם ’ישוע‘ תקראי לו. 32הוא יהיה רם־מעלה וייקרא בן־אלוהים. ה׳ ייתן לו את כסא דוד אביו, 33והוא ימלוך על עם־ישראל לעולם ועד; מלכותו לא תסתיים לעולם.“ 34”כיצד אוכל ללדת?“ שאלה מרים בתמיהה. ”הרי אני בתולה!“ 35השיב לה המלאך: ”רוח הקודש תבוא אליך, וגבורת אלוהים תצל עליך. משום כך הבן הקדוש שייוולד ייקרא בן־אלוהים.“ 36המלאך המשיך: ”לפני שישה חודשים נכנסה קרובתך הזקנה אלישבע להריון – כן, זו ששכנותיה קראו לה ’העקרה‘ – וגם היא תלד בן! 37כי אין דבר בלתי אפשרי לאלוהים“.

38”הנני שפחתך, אדוני,“ אמרה מרים בענווה, ”ואני מוכנה לעשות את כל אשר יאמר לי. אמן שיתקיימו דבריך.“ לאחר מכן נעלם המלאך.

39‏-40כעבור ימים אחדים מיהרה מרים אל הרי יהודה, אל ביתו של זכריה, ובהיכנסה אל הבית ברכה את אלישבע לשלום. 41לשמע ברכתה של מרים התנועע התינוק בבטנה של אלישבע, והיא נמלאה ברוח הקודש.

42”ברוכה את בנשים, מרים, וברוך תינוקך!“ פרצה אלישבע בקריאת שמחה. 43”מדוע זכיתי בכבוד הגדול שאם אדוני באה לבקר אותי? 44התינוק בבטני התנועע בשמחה לשמע קול ברכתך! 45אלוהים ברך אותך בצורה נפלאה כזאת משום שהאמנת כי יקיים את דבריו.“

46השיבה מרים:

”ברכי נפשי את ה׳;

47אגיל ואשמח באלוהים מושיעי!

48כי עשה חסד עם שפחתו,

ומעתה יברכוני כל הדורות.

49גדולות ונפלאות עשה עמי אל שדי, קדוש שמו.

50מדור לדור הוא מעניק את חסדו ורחמיו לכל היראים אותו.

51בזרוע נטויה עשה מעשי גבורה,

הפר מזימות גאים ורשעים,

52והוריד שליטים מכיסאם.

אולם את השפלים והנחותים הוא רומם!

53את העניים האכיל ואת העשירים הרעיב!

54‏-55אלוהים תמך בעבדו ישראל,

ולא שכח כי הבטיח לאבותינו

– לאברהם ולזרעו –

לרחם על ישראל לעולם ועד!“

56מרים נשארה אצל אלישבע כשלושה חודשים, ולאחר מכן חזרה לביתה. 57בינתיים תמו ימי הריונה של אלישבע והיא ילדה בן. 58השמועה על החסד שעשה איתה ה׳ התפשטה עד מהרה בין שכניה וקרובי משפחתה, וכולם שמחו בשמחתה.

59ביום השמיני להולדת התינוק התכנסו השכנים והקרובים לטקס ברית־המילה. האורחים היו בטוחים שהתינוק ייקרא ”זכריה“ – על שם אביו, 60אולם אלישבע אמרה: ”לא, שם התינוק יוחנן!“

61”יוחנן?“ התפלאו האורחים. ”אבל אין במשפחתך אף אחד בשם הזה“. 62הם פנו אל זכריה (שעדיין לא היה מסוגל לדבר), ושאלו אותו בתנועות ידיים וברמזים כיצד ייקרא התינוק.

63זכריה ביקש בתנועות ידיים שיביאו לו לוח, וכתב עליו: ”שם הילד יוחנן“. 64באותו רגע חזר אליו כושר הדיבור והוא החל לברך את אלוהים.

65כל השכונה נמלאה יראת כבוד, והדבר היה נושא לשיחה בכל הרי יהודה. 66כל השומעים התרשמו עמוקות ואמרו: ”מעניין למה נועד הילד הזה.“ כי היה ברור להם שאלוהים איתו.

67לאחר מכן נמלא זכריה אביו רוח הקודש וניבא את הנבואה הבאה:

68”ברוך ה׳ אלוהי ישראל,

כי פנה אל עמו, הודיע ופדה אותו.

69ה׳ שלח לנו מושיע גיבור משושלת בית דוד עבדו –

70כפי שהבטיח לנו בפי נביאיו הקדושים עוד לפני זמן רב –

71כדי להצילנו מיד כל אויבינו ושונאינו.

72אלוהים יעשה חסד עם אבותינו

ויזכור את בריתו

73ואת שבועתו לאברהם אבינו:

74‏-75להצילנו מיד אויבינו,

ולהעניק לנו את הזכות

לשרתו כל ימי חיינו בקדושה,

ובצדקה וללא פחד.“

76”ואתה, ילדי הקטן, תיקרא נביא לאל עליון,

כי תלך לפני האדון ותפנה לו את הדרך.

77אתה תלמד את בני־ישראל

כיצד הם יכולים להיוושע על־ידי סליחת חטאיהם.

78בזכות אהבתו, רחמיו וטוב־לבו של אלוהים

יזרח עלינו אור ממרום,

79כדי להאיר לשרויים במוות ובחשכה,

וכדי להוביל את רגלינו אל דרך השלום.“

80הילד גדל, התחזק והתחשל באופיו. הוא התגורר במדבר עד שהגיע המועד להתחיל את שליחותו אל עם־ישראל.