Kolossiyawa 1 – HCB & BDS

Hausa Contemporary Bible

Kolossiyawa 1:1-29

1Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu,

2Zuwa ga tsarkaka da kuma amintattun ’yan’uwa cikin Kiristi da suke a Kolossi.

Alheri da salama daga Allah Ubanmu, su kasance tare da ku.1.2 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā suna da Uba da Ubangiji Yesu Kiristi

Godiya da addu’a

3Kullum muna gode wa Allah, Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, sa’ad da muke addu’a dominku. 4Gama mun ji labarin bangaskiyarku a cikin Yesu Kiristi da kuma ƙaunar da kuke yi saboda dukan tsarkaka. 5Kuna yin haka ne kuwa domin abin da kuke bege yana a ajiye a sama. Kun riga kun ji game da wannan bege sa’ad da kuka gaskata saƙon nan na gaskiya wanda shi ne bisharar 6da ta zo muku. Ko’ina a duniya wannan bishara tana yi ta haihuwa tana kuma girma, kamar yadda take yi a cikinku tun daga ranar da kuka ji ta kuka kuma fahimci alherin Allah cikin dukan gaskiyarta. 7Kun koyi wannan gaskiya daga wurin Efafaras, ƙaunataccen abokin hidimarmu, wanda yake amintacce mai hidimar Kiristi a madadinmu, 8wanda kuma ya faɗa mana ƙaunar da kuke yi cikin Ruhu.

9Shi ya sa tun daga ranar da muka sami labarin, ba mu fasa yin addu’a dominku ba. Kullum muna roƙon Allah yă sa ku san kome da yake so ku yi, domin ku sami hikima ta Ruhu, ku kuma sami ganewar kome duka. 10Ta haka za ku yi rayuwa wadda ta dace da Ubangiji, ku kuma gamshe shi a ta kowace hanya, kuna yin aiki mai kyau ta kowace hanya, kuna kuma yin girma cikin sanin Allah. 11Allah yă ƙarfafa ku da dukan iko bisa ga ɗaukakar ƙarfinsa domin ku kasance da jimrewa sosai da kuma haƙuri, cikin farin ciki 12kuna gode wa Uba, wanda ya sa kuka cancanci ku sami rabo a gādon tsarkaka a cikin mulkin haske. 13Gama ya riga ya cece mu daga mulkin duhu ya kuma kawo mu cikin mulkin Ɗan da yake ƙauna, 14wanda ta wurinsa muka sami fansa da kuma gafarar zunubai.

Fifikon Kiristi

15Kiristi shi ne surar da ake gani na Allah wanda ba a iya gani, ɗan fari a kan dukan halitta. 16Ta wurinsa aka halicci dukan abu, abubuwan da suke cikin sama da abubuwan da suke a duniya, waɗanda ake gani, da waɗanda ba a gani, ko kursiyoyi ko ikoki ko masu mulki ko hukumomi; an halicci dukan abu ta wurinsa da kuma dominsa ne. 17Ya kasance kafin dukan abu, kuma a cikinsa ne dukan abubuwa suke a harhaɗe. 18Shi ne kuma kan ikkilisiya, wadda take jikinsa. Shi ne mafari da kuma na farko da ya tashi daga matattu, domin a cikin kowane abu yă zama mafifici. 19Gama Allah ya ji daɗi yă sa dukan cikarsa ta kasance a cikin Kiristi, 20ta wurin Kiristi ne ya komar da kome zuwa ga kansa. Ya kawo salama ga abubuwan da suke ƙasa da abubuwan da suke sama, ta wurin jinin Kiristi da ya zubar a kan gicciye.

21A dā kuna a ware da Allah, kuka kuma zama abokan gāba a cikin tunaninku saboda mugun halinku. 22Amma Ɗansa ya zama mutum ya kuma mutu. Saboda haka Allah ya yi sulhu da ku, yanzu kuwa ya bar ku ku tsaya a gabansa da tsarki, marasa aibi, da kuma marasa abin zargi. 23Sai ku ci gaba cikin bangaskiyarku, kuna tsaye a kafe kuma tsayayyu, ba tare da gusawa daga begen da kuka ji daga bishara ba. Wannan ita ce bisharar da kuka ji wadda aka yi shelarta ga kowace halittar da take ƙarƙashin sama, wadda kuma ni Bulus, na zama mai hidimarta.

Hidimar Bulus ga ikkilisiya

24Yanzu, ina farin ciki saboda wuyar da nake sha dominku, don ta wurin wuyan nan zan cika abin da ya rage na wuyar da Kiristi ya sha saboda jikinsa, wato, ikkilisiya. 25Na zama mai hidimar ikkilisiya bisa ga aikin nan da Allah ya ba ni amana saboda ku, domin in sanar da maganar Allah sosai. 26Wannan magana da nake gaya muku asiri ne da yake a ɓoye tun zamanai masu yawa, wanda yanzu aka bayyana ga tsarkaka. 27Su ne Allah ya so yă sanar da yadda irin yalwar ɗaukakar asirin nan take a cikin al’ummai, asirin nan kuwa shi ne Kiristi a cikinku, begen ɗaukakar da za a bayyana.

28Saboda haka ko’ina muka tafi, muna shela, muna gargaɗi, muna kuma koyar da kowa da dukan hikima, don mu miƙa kowa cikakke a cikin Kiristi. 29Don haka ne ina fama, ina kuma ƙoƙari da duk ƙarfin nan da Kiristi ya ba ni.

La Bible du Semeur

Colossiens 1:1-29

Salutation

1Paul, apôtre de Jésus-Christ par la volonté de Dieu, et le frère Timothée, saluent 2ceux qui, à Colosses, font partie du peuple saint par leur union avec Christ et qui sont nos fidèles frères et sœurs en lui.

Que la grâce et la paix vous soient accordées par Dieu notre Père1.2 Certains manuscrits ajoutent : et par le Seigneur Jésus-Christ..

Prière de reconnaissance

3Nous exprimons constamment à Dieu, le Père de notre Seigneur Jésus-Christ, notre reconnaissance à votre sujet dans nos prières pour vous. 4En effet, nous avons entendu parler de votre foi en Jésus-Christ et de votre amour pour tous les membres du peuple saint. 5Cette foi et cet amour se fondent sur ce qui fait votre espérance et que Dieu vous réserve dans les cieux. Cette espérance, vous l’avez connue par la prédication de la vérité, cet Evangile 6qui est parvenu jusqu’à vous, comme il est aussi présent dans le monde entier où il porte du fruit et va de progrès en progrès – ce qui est également le cas parmi vous, depuis le jour où vous avez reçu et reconnu la grâce de Dieu dans toute sa vérité.

7C’est Epaphras, notre cher collaborateur, qui vous en a instruits. Il est un fidèle serviteur de Christ auprès de vous1.7 L’Eglise à Colosses avait été fondée par ce collaborateur de l’apôtre. 8et il nous a appris quel amour l’Esprit vous inspire.

Prière de Paul et hymne à Jésus-Christ

9Aussi, depuis le jour où nous avons entendu parler de vous, nous aussi, nous ne cessons de prier Dieu pour vous. Nous lui demandons qu’il vous fasse connaître pleinement sa volonté, en vous donnant, par le Saint-Esprit, une entière sagesse et un parfait discernement. 10Ainsi vous pourrez avoir une conduite digne du Seigneur et qui lui plaise à tous égards. Car vous porterez comme fruit toutes sortes d’œuvres bonnes et vous ferez des progrès dans la connaissance de Dieu. 11Dieu vous fortifiera pleinement à la mesure de sa puissance glorieuse, pour que vous puissiez tout supporter et persévérer jusqu’au bout – et cela avec joie1.11 Autre traduction : et persévérer jusqu’au bout. Avec joie, vous exprimerez votre reconnaissance au Père…. 12Vous exprimerez votre reconnaissance au Père qui vous a rendus capables d’avoir part à l’héritage qu’il réserve dans la lumière aux membres de son peuple saint1.12 Dans l’ancienne alliance, les Juifs ont reçu le pays promis comme héritage ; maintenant les non-Juifs sont co-héritiers avec eux du nouveau pays promis, c’est-à-dire du royaume de Dieu.. Car :

13Il nous a arrachés

au pouvoir des ténèbres

et nous a fait passer

dans le royaume

de son Fils bien-aimé.

14Etant unis à lui,

nous sommes délivrés,

car nous avons reçu

le pardon des péchés.

15Ce Fils,

il est l’image

du Dieu que nul ne voit,

il est le Premier-né

de toute création.

16Car c’est en lui

qu’ont été créées toutes choses

dans les cieux comme sur la terre,

les visibles, les invisibles,

les Trônes et les Seigneuries,

les Autorités, les Puissances.

C’est par lui et pour lui

que Dieu a tout créé.

17Il est lui-même

bien avant toutes choses

et tout subsiste en lui.

18Il est lui-même

la tête de son corps

qui est l’Eglise1.18 Jeu de mots : Christ est à la fois la tête et à la tête de son Eglise..

Ce Fils

est le commencement,

le Premier-né

de tous ceux qui sont morts,

afin qu’en toutes choses

il ait le premier rang.

19Car c’est en lui

que Dieu a désiré

que toute plénitude

ait sa demeure.

20Et c’est par lui

qu’il a voulu

réconcilier avec lui-même

l’univers tout entier :

ce qui est sur la terre

et ce qui est au ciel,

en instaurant la paix

par le sang que son Fils

a versé sur la croix.

21Or vous, autrefois, vous étiez exclus de la présence de Dieu, vous étiez ses ennemis à cause de vos pensées qui vous amenaient à faire des œuvres mauvaises ; 22mais maintenant, Dieu vous a réconciliés avec lui par le sacrifice de son Fils qui a livré à la mort son corps humain, pour vous faire paraître saints, irréprochables et sans faute devant lui. 23Mais il vous faut, bien sûr, demeurer dans la foi, fermement établis sur ce fondement sans vous laisser écarter de l’espérance qu’annonce l’Evangile. Cet Evangile, vous l’avez entendu, il a été proclamé parmi toutes les créatures sous le ciel, et moi, Paul, j’en suis devenu le serviteur.

Christ, la vraie sagesse

Le combat de l’apôtre pour l’Eglise

24Maintenant, je me réjouis des souffrances que j’endure pour vous. Car, en ma personne, je complète, pour le bien de son corps – qui est l’Eglise – ce qui manque aux persécutions dirigées contre Christ1.24 D’autres comprennent : car, en ma personne, je complète ce qui manque aux souffrances de Christ pour son corps, qui est l’Eglise.. 25C’est de cette Eglise que je suis devenu le serviteur, selon la responsabilité que Dieu m’a confiée à votre égard. Il m’a chargé d’annoncer sa Parole dans toute sa plénitude 26en vous faisant connaître le secret de son plan tenu caché depuis toujours, de génération en génération, mais qui s’accomplit de façon manifeste pour les membres de son peuple saint. 27Car Dieu a voulu leur faire connaître quelle est la glorieuse richesse que renferme le secret de son plan pour les non-Juifs. Et voici ce secret : Christ en vous1.27 Autre traduction : parmi vous., garantie de votre espérance de la gloire à venir.

28C’est lui, Christ, que nous, nous annonçons, en avertissant et en enseignant tout être humain, en toute sagesse, afin de faire paraître devant Dieu tout homme parvenu à l’état d’adulte dans son union avec Christ. 29Voilà pourquoi je travaille et je combats par la force de Christ qui agit puissamment en moi.