Ibraniyawa 3 – HCB & OL

Hausa Contemporary Bible

Ibraniyawa 3:1-19

Yesu ya fi Musa

1Saboda haka, ’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa. 2Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah. 3An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja. 4Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne. 5Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba. 6Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.

Gargaɗi a kan rashin bangaskiya

7Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce,

“Yau, in kuka ji muryarsa,

8kada ku taurare zukatanku,

yadda kuka yi a tawayen nan,

a lokacin gwaji a hamada,

9inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni,

ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.

10Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani,

na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke,

ba su kuma san hanyoyina ba.’

11Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina,

‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’ ”3.11 Zab 95.7-11

12Ku lura fa, ’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai. 13Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi. 14Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe. 15Kamar yadda aka faɗa cewa,

“Yau, in kuka ji muryarsa,

kada ku taurare zukatanku

kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”3.15 Zab 95.7,8

16Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba? 17Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba? 18Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba? 19Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.

O Livro

Hebreus 3:1-19

Jesus é superior a Moisés

1Portanto, meus irmãos, a quem Deus separou para si e a quem chamou para participarem da vida celestial, atentem para o enviado de Deus, o sumo sacerdote da fé que proclamamos, 2o qual cumpriu fielmente a missão que Deus lhe designou, tal como Moisés serviu fielmente na casa de Deus. 3Mas Jesus é muito superior a Moisés, da mesma maneira que o homem que constrói uma casa tem mais mérito do que a própria casa. 4Se é verdade que não há casa que não tenha sido construída por alguém, não menos verdade é que quem construiu tudo o que existe foi Deus.

5É bem certo que Moisés serviu com toda a fidelidade na casa de Deus,3.5 Nm 12.7. mas o que ele fez foi um serviço, o de anunciar aquilo que haveria de ser revelado mais tarde. 6Mas Cristo é fiel e responsável como Filho sobre a sua própria casa, a qual casa somos nós próprios, se conservarmos a nossa confiança até ao fim, assim como a exultação da esperança nele.

Aviso contra a incredulidade

7Portanto, o Espírito Santo nos avisa, como está escrito:

“Se hoje ouvirem a sua voz,

8não endureçam os vossos corações,

como fizeram na rebelião,

durante o tempo de prova no deserto.

9Ali os vossos pais tentaram a minha paciência

e duvidaram de mim,

mesmo depois de terem visto tudo o que eu fiz.

10Durante quarenta anos andei desgostoso com esta geração.

É um povo que erra constantemente;

eles não conheceram os meus caminhos.

11Por isso, jurei, na minha cólera:

não entrarão no meu descanso.”3.11 Sl 95.7-11.

12Tomem então cuidado, irmãos, para que nenhum de vocês se afaste para longe do Deus vivo, levado pelo seu coração mau e incrédulo. 13Pelo contrário, procurem encorajar-se uns aos outros, enquanto dura esse tempo de “hoje”, a fim de que ninguém endureça o seu coração pelo engano do pecado. 14Porque se mantivermos firmemente, até ao fim, a nossa confiança no Senhor, como quando nos tornámos cristãos, participamos de tudo o que pertence a Cristo. 15Então, não esqueçamos este aviso:

“Se hoje ouvirem a sua voz,

não endureçam os vossos corações,

como fizeram na rebelião.”3.15 Sl 95.7-8.

16E quem foram esses que, depois de ouvirem Deus falar-lhes, o provocaram? Não foram porventura os que por meio de Moisés saíram do Egito? 17E não foram esses que durante quarenta anos tanto exasperaram a Deus e pecaram, tendo os seus cadáveres ficado ali no deserto? 18E não foi a eles que Deus declarou, com juramento, que não haveriam de entrar no seu descanso? Pois foram esses mesmos que lhe desobedeceram. 19Vemos pois que não puderam entrar por causa da sua incredulidade.