Galatiyawa 1 – HCB & CCBT

Hausa Contemporary Bible

Galatiyawa 1:1-24

1Bulus manzo, aikakke ba daga wurin mutum ba, ba kuma ta wurin mutane ba, amma ta wurin Yesu Kiristi da kuma Allah Uba, wanda ya tā da Yesu daga matattu. 2Dukan ’yan’uwan kuma da suke tare da ni a nan,

Suna gai da ikkilisiyoyi a Galatiya.

3Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku. 4Shi wanda ya ba da kansa saboda zunubanmu don yă cece mu daga wannan mugun zamani na yanzu, bisa ga nufin Allah wanda yake kuma Ubanmu, 5a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin.

Babu wata bishara

6Ina mamaki yadda kuka yi saurin yashe wanda ya kira ku ta wurin alherin Kiristi, kuna juyewa ga wata bishara dabam 7wadda a gaskiya ba bishara ba ce ko kaɗan. Tabbatacce waɗansu mutane suna birkitar da ku, suna kuma ƙoƙari su karkatar da bisharar Kiristi. 8Amma ko mu, ko mala’ika daga sama ya yi wa’azin wata bishara dabam da wadda muka yi muku, bari yă zama la’ananne har abada! 9Kamar yadda muka riga muka faɗa, haka yanzu ma ina ƙara cewa in wani yana muku wa’azin wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, bari yă zama la’ananne har abada!

10Za a ce, ina ƙoƙarin neman amincewar mutane ne, ko amincewa ta Allah? Ko kuwa ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne? Da a ce har yanzu ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne, ai, da ban zama bawan Kiristi ba.

Bulus kirayaye na Allah

11Ina so ku sani ’yan’uwa, cewa bisharar da nake wa’azi, ba mutum ne ya ƙago ta ba. 12Ban karɓe ta daga wurin wani mutum ba, ba a kuma koya mini ita ba, a maimako, na karɓe ta, ta wurin wahayi daga Yesu Kiristi ne.

13Kun dai ji labarin rayuwata ta dā a cikin Yahudanci, yadda na tsananta wa ikkilisiyar Allah ƙwarai, na kuma yi ƙoƙarin hallaka ta. 14Na ci gaba a cikin Yahudanci fiye da yawancin Yahudawan da suke tsarana, na kuma yi ƙwazo ƙwarai ga bin al’adun kakannina. 15Amma sa’ad da Allah, wanda ya keɓe ni daga mahaifa1.15 Ko kuwa daga cikin mahaifiyata ya kira ni ta wurin alherinsa, ya kuma gamshe shi 16yă bayyana Ɗansa a cikina, domin in yi wa’azinsa cikin Al’ummai. Ban nemi shawarar wani mutum ba. 17Ban kuma tafi Urushalima domin in ga waɗanda suka riga ni zaman manzanni ba, sai dai na hanzarta na tafi ƙasar Arabiya, daga baya sai na koma Damaskus.

18Bayan shekara uku, sai na haura zuwa Urushalima domin in sadu da Bitrus1.18 Girik Kefas, na kuwa zauna tare da shi kwana goma sha biyar. 19Ban ga wani a ciki sauran manzanni ba, sai dai Yaƙub ɗan’uwan Ubangiji. 20Ina tabbatar muku a gaban Allah cewa abin da nake rubuta muku ba ƙarya ba ne.

21Daga baya sai na tafi Suriya da Silisiya. 22Ikkilisiyoyin da suke cikin Kiristi da suke a Yahudiya ba su san ni ba tukuna. 23Sun dai sami labari ne kawai cewa, “Mutumin da dā yake tsananta mana yanzu yana wa’azin bangaskiyar da dā ya yi ƙoƙari yă hallaka.” 24Sai suka yabi Allah saboda ni.

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

加拉太書 1:1-24

1我是保羅,我作使徒並非受人委派,也不是倚靠人,而是由耶穌基督和叫祂從死裡復活的父上帝委派的。 2我和所有跟我在一起的弟兄寫信給加拉太的各教會。

3願我們的父上帝和主耶穌基督賜給你們恩典和平安! 4基督遵照我們父上帝的旨意為我們的罪獻上了自己,好拯救我們脫離這罪惡的世代。

5願榮耀歸給上帝,直到永永遠遠。阿們!

勿隨別的福音

6我很驚訝,你們竟然那麼快就背棄了藉著基督的恩典呼召你們的上帝,去追隨別的福音! 7其實那並不是福音,只是某些人擾亂你們的信仰,想篡改基督的福音。 8即便是我們或天使,若另傳福音給你們,與我們以前傳給你們的相悖,也該受咒詛。 9我們已經說過,現在我再說一次:如果有人向你們傳別的福音,跟你們以前接受的不同,那人該受咒詛。

10我現在是要贏得人的贊同嗎?還是要贏得上帝的贊同?難道我是要討好人嗎?如果我仍舊要討好人,我就不是基督的奴僕了。

保羅受上帝委派傳福音

11弟兄姊妹,我告訴你們,我傳的福音不是出於人的意思, 12因為這福音既不是我從人那裡領受的,也不是我跟人學來的,而是耶穌基督親自啟示我的。 13你們都聽說過我信奉猶太教時的所作所為,我怎樣殘酷地迫害上帝的教會,試圖摧毀它。 14我在猶太教裡比許多同輩的猶太人更進取,狂熱地維護祖先的傳統。

15然而,當我還在母腹中的時候,上帝就施恩將我分別出來並呼召了我。 16上帝既然樂意把祂的兒子啟示給我,叫我向外族人傳揚祂的福音,我就沒有跟任何人1·16 」希臘文是「血肉」。商量, 17也沒有上耶路撒冷去見那些比我先作使徒的人,而是立刻去了阿拉伯,然後回到大馬士革

18過了三年,我才到耶路撒冷去拜會彼得,和他一起住了十五天。 19我也見了主耶穌的弟弟雅各,此外沒有見過其他使徒。 20我在上帝面前保證,我寫給你們的絕無謊言。

21後來我又到了敘利亞基利迦地區。 22那時,猶太境內基督的眾教會都還沒有見過我的面。 23他們只是聽人說:「那個從前迫害我們的人如今在傳揚他曾試圖摧毀的信仰。」 24於是他們因為我的緣故將榮耀歸給上帝。