Galatiyawa 1 – HCB & CCB

Hausa Contemporary Bible

Galatiyawa 1:1-24

1Bulus manzo, aikakke ba daga wurin mutum ba, ba kuma ta wurin mutane ba, amma ta wurin Yesu Kiristi da kuma Allah Uba, wanda ya tā da Yesu daga matattu. 2Dukan ’yan’uwan kuma da suke tare da ni a nan,

Suna gai da ikkilisiyoyi a Galatiya.

3Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku. 4Shi wanda ya ba da kansa saboda zunubanmu don yă cece mu daga wannan mugun zamani na yanzu, bisa ga nufin Allah wanda yake kuma Ubanmu, 5a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin.

Babu wata bishara

6Ina mamaki yadda kuka yi saurin yashe wanda ya kira ku ta wurin alherin Kiristi, kuna juyewa ga wata bishara dabam 7wadda a gaskiya ba bishara ba ce ko kaɗan. Tabbatacce waɗansu mutane suna birkitar da ku, suna kuma ƙoƙari su karkatar da bisharar Kiristi. 8Amma ko mu, ko mala’ika daga sama ya yi wa’azin wata bishara dabam da wadda muka yi muku, bari yă zama la’ananne har abada! 9Kamar yadda muka riga muka faɗa, haka yanzu ma ina ƙara cewa in wani yana muku wa’azin wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, bari yă zama la’ananne har abada!

10Za a ce, ina ƙoƙarin neman amincewar mutane ne, ko amincewa ta Allah? Ko kuwa ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne? Da a ce har yanzu ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne, ai, da ban zama bawan Kiristi ba.

Bulus kirayaye na Allah

11Ina so ku sani ’yan’uwa, cewa bisharar da nake wa’azi, ba mutum ne ya ƙago ta ba. 12Ban karɓe ta daga wurin wani mutum ba, ba a kuma koya mini ita ba, a maimako, na karɓe ta, ta wurin wahayi daga Yesu Kiristi ne.

13Kun dai ji labarin rayuwata ta dā a cikin Yahudanci, yadda na tsananta wa ikkilisiyar Allah ƙwarai, na kuma yi ƙoƙarin hallaka ta. 14Na ci gaba a cikin Yahudanci fiye da yawancin Yahudawan da suke tsarana, na kuma yi ƙwazo ƙwarai ga bin al’adun kakannina. 15Amma sa’ad da Allah, wanda ya keɓe ni daga mahaifa1.15 Ko kuwa daga cikin mahaifiyata ya kira ni ta wurin alherinsa, ya kuma gamshe shi 16yă bayyana Ɗansa a cikina, domin in yi wa’azinsa cikin Al’ummai. Ban nemi shawarar wani mutum ba. 17Ban kuma tafi Urushalima domin in ga waɗanda suka riga ni zaman manzanni ba, sai dai na hanzarta na tafi ƙasar Arabiya, daga baya sai na koma Damaskus.

18Bayan shekara uku, sai na haura zuwa Urushalima domin in sadu da Bitrus1.18 Girik Kefas, na kuwa zauna tare da shi kwana goma sha biyar. 19Ban ga wani a ciki sauran manzanni ba, sai dai Yaƙub ɗan’uwan Ubangiji. 20Ina tabbatar muku a gaban Allah cewa abin da nake rubuta muku ba ƙarya ba ne.

21Daga baya sai na tafi Suriya da Silisiya. 22Ikkilisiyoyin da suke cikin Kiristi da suke a Yahudiya ba su san ni ba tukuna. 23Sun dai sami labari ne kawai cewa, “Mutumin da dā yake tsananta mana yanzu yana wa’azin bangaskiyar da dā ya yi ƙoƙari yă hallaka.” 24Sai suka yabi Allah saboda ni.

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

加拉太书 1:1-24

1我是保罗,我做使徒并非受人委派,也不是倚靠人,而是由耶稣基督和叫祂从死里复活的父上帝委派的。 2我和所有跟我在一起的弟兄写信给加拉太的各教会。

3愿我们的父上帝和主耶稣基督赐给你们恩典和平安! 4基督遵照我们父上帝的旨意为我们的罪献上了自己,好拯救我们脱离这罪恶的世代。

5愿荣耀归给上帝,直到永永远远。阿们!

勿随别的福音

6我很惊讶,你们竟然那么快就背弃了借着基督的恩典呼召你们的上帝,去追随别的福音! 7其实那并不是福音,只是某些人扰乱你们的信仰,想篡改基督的福音。 8即便是我们或天使,若另传福音给你们,与我们以前传给你们的相悖,也该受咒诅。 9我们已经说过,现在我再说一次:如果有人向你们传别的福音,跟你们以前接受的不同,那人该受咒诅。

10我现在是要赢得人的赞同吗?还是要赢得上帝的赞同?难道我是要讨好人吗?如果我仍旧要讨好人,我就不是基督的奴仆了。

保罗受上帝委派传福音

11弟兄姊妹,我告诉你们,我传的福音不是出于人的意思, 12因为这福音既不是我从人那里领受的,也不是我跟人学来的,而是耶稣基督亲自启示我的。 13你们都听说过我信奉犹太教时的所作所为,我怎样残酷地迫害上帝的教会,试图摧毁它。 14我在犹太教里比许多同辈的犹太人更进取,狂热地维护祖先的传统。

15然而,当我还在母腹中的时候,上帝就施恩将我分别出来并呼召了我。 16上帝既然乐意把祂的儿子启示给我,叫我向外族人传扬祂的福音,我就没有跟任何人1:16 ”希腊文是“血肉”。商量, 17也没有上耶路撒冷去见那些比我先做使徒的人,而是立刻去了阿拉伯,然后回到大马士革

18过了三年,我才到耶路撒冷去拜会彼得,和他一起住了十五天。 19我也见了主耶稣的弟弟雅各,此外没有见过其他使徒。 20我在上帝面前保证,我写给你们的绝无谎言。

21后来我又到了叙利亚基利迦地区。 22那时,犹太境内基督的众教会都还没有见过我的面。 23他们只是听人说:“那个从前迫害我们的人如今在传扬他曾试图摧毁的信仰。” 24于是他们因为我的缘故将荣耀归给上帝。