Filibbiyawa 1 – HCB & NIRV

Hausa Contemporary Bible

Filibbiyawa 1:1-30

1Bulus da Timoti, bayin Kiristi Yesu,

Zuwa ga dukan tsarkaka cikin Kiristi Yesu a Filibbi, tare da masu kula da Ikkilisiya1.1 A al’adance su bishob da kuma masu hidima.

2Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare ku.

Godiya da addu’a

3Ina gode wa Allahna a kowane lokacin da na tuna da ku. 4A cikin dukan addu’o’ina dominku duka, nakan yi addu’a da farin ciki kullum 5saboda tarayyarku a cikin bishara daga ranar farko har yă zuwa yanzu, 6da tabbacin cewa wanda ya fara kyakkyawan aikin nan a cikinku, zai kai shi ga kammalawa har yă zuwa ranar Kiristi Yesu.

7Daidai ne in yi wannan tunani game da dukanku, da yake kuna a zuciyata; domin ko ina daure cikin sarƙoƙi ko ina kāre bishara ina kuma tabbatar da ita, dukanku kuna tarayya cikin alherin Allah tare da ni. 8Allah shi ne shaidata, ya san yadda nake ƙaunarku duka da ƙaunar Kiristi Yesu.

9Addu’ata ita ce ƙaunarku tă yi ta cin gaba da ƙaruwa cikin sani da kuma zurfin ganewa, 10don ku iya rarrabe abin da yake mafi kyau, ku kuma zama da tsarki, marasa aibi har yă zuwa ranar Kiristi, 11cikakku da sakamakon aikin adalci da yake zuwa ta wurin Yesu Kiristi, zuwa ga ɗaukakar Allah da kuma yabonsa.

Sarƙoƙin Bulus sun sa ci gaban bishara

12To, ina so ku sani ’yan’uwa, cewa abin da ya faru da ni ya sa cin gaban bishara. 13Ta haka, ya zama sananne ga dukan masu gadin fada1.13 Ko kuwa dukan fada da kuma ga kowa cewa an daure ni da sarƙoƙi saboda Kiristi. 14Saboda sarƙoƙina, yawancin ’yan’uwa cikin Ubangiji sun sami ƙarfafawa su yi maganar Allah gabagadi da kuma babu tsoro.

15Gaskiya ce cewa waɗansu suna yin wa’azin Kiristi saboda kishi da neman faɗa, amma waɗansu da nufi mai kyau suke yi. 16Na biye suna yin haka cikin ƙauna, da sanin cewa an sa ni a nan ne domin kāriyar bishara. 17Na farin dai suna wa’azin Kiristi da sonkai ne, ba da zuciya ɗaya ba, a sonsu, su wahalar da ni a cikin sarƙoƙi.1.17 Waɗansu rubuce-rubucen hannun da ba su daɗe ba suna da aya 17 kafin aya 16. 18Me kuma? Ta ko yaya dai, ko da gangan, ko da gaske, ana shelar Kiristi. Domin wannan kuwa ina farin ciki.

I, zan kuwa ci gaba da farin ciki, 19gama na san cewa ta wurin addu’o’inku da kuma taimako daga Ruhun Yesu Kiristi, abin da ya same ni zai zama sanadin kuɓutata. 20Ina saurara da marmari da kuma bege cewa ba zan taɓa shan kunya ba, sai dai zan sami issashen ƙarfin hali yanzu kamar kullum, za a ɗaukaka Kiristi a jikina, ko ta wurin rayuwa ko kuma ta wurin mutuwa. 21Gama a gare ni, rai Kiristi ne, mutuwa kuma riba ce. 22In zan ci gaba da rayuwa a cikin jiki, wannan zai zama aiki mai amfani a gare ni. Duk da haka me zan zaɓa? Ban sani ba! 23Na rasa wanda zan zaɓa cikin biyun nan. Ina sha’awa in yi ƙaura in zauna tare da Kiristi, wannan kuwa ya fi kyau nesa ba kusa ba; 24amma ya fi muku muhimmanci in rayu cikin jiki. 25Na tabbata haka ne, na kuwa san zan wanzu in zauna tare da ku duka, domin ku ci gaba, bangaskiyarku tana sa ku farin ciki, 26domin ta wurin kasancewata tare da ku, farin cikinku cikin Kiristi Yesu zai cika sosai ta dalilina.

Rayuwar da ta dace da bishara

27Kome ya faru, ku yi zaman da ya cancanci bisharar Kiristi. Ta haka, ko na zo na gan ku, ko ban zo ba, in ji labari cewa kun tsaya da ƙarfi a cikin ruhu ɗaya, kuna fama kamar mutum ɗaya saboda bangaskiyar bishara 28ba tare da kun ji tsoron waɗanda suke gāba da ku ta kowace hanya ba. Wannan alama ce a gare su cewa za a hallaka su, amma a gare ku za a cece ku, wannan tabbacin kuwa daga wurin Allah ne. 29Gama an ba ku zarafi a madadin Kiristi cewa ba gaskatawa da shi kaɗai ba kuka yi ba, har ma ku sha wahala dominsa, 30da yake kuna shan faman da kuka gan na sha, kuna kuma jin cewa har yanzu ina sha.

New International Reader’s Version

Philippians 1:1-30

1We, Paul and Timothy, are writing this letter. We serve Christ Jesus.

We are sending this letter to you, all God’s holy people in Philippi. You belong to Christ Jesus. We are also sending this letter to your leaders and deacons.

2May God our Father and the Lord Jesus Christ give you grace and peace.

Paul Prays and Gives Thanks

3I thank my God every time I remember you. 4In all my prayers for all of you, I always pray with joy. 5I am happy because you have joined me in spreading the good news. You have done so from the first day until now. 6God began a good work in you. And I am sure that he will carry it on until it is completed. That will be on the day Christ Jesus returns.

7It is right for me to feel this way about all of you. I love you with all my heart. I may be held by chains, or I may be standing up for the truth of the good news. Either way, all of you share in God’s grace together with me. 8God is my witness that I long for all of you. I love you with the love that Christ Jesus gives.

9I pray that your love will grow more and more. And let it be based on knowledge and understanding. 10Then you will be able to know what is best. Then you will be pure and without blame for the day that Christ returns. 11You will be filled with the fruit of right living produced by Jesus Christ. All these things bring glory and praise to God.

Paul Spreads the Good News While in Prison

12Brothers and sisters, here is what I want you to know. What has happened to me has actually helped to spread the good news. 13One thing has become clear. I am being held by chains because I am a witness for Christ. All the palace guards and everyone else know it. 14And because I am a prisoner, most of the believers have become bolder in the Lord. They now dare even more to preach the good news without fear.

15It’s true that some preach about Christ because they are jealous. But others preach about Christ to help me in my work. 16The last group acts out of love. They know I have been put here to be a witness for the good news. 17But the others preach about Christ only to get ahead. They preach Christ for the wrong reasons. They think they can stir up trouble for me while I am being held by chains. 18But what does it matter? Here is the important thing. Whether for right or wrong reasons, Christ is being preached about. That makes me very glad.

And I will continue to be glad. 19I know that you are praying for me. I also know that God will give me the Spirit of Jesus Christ to help me. So no matter what happens, I’m sure I will still be set free. 20I completely expect and hope that I won’t be ashamed in any way. I’m sure I will be brave enough. Now as always Christ will receive glory because of what happens to me. He will receive glory whether I live or die. 21For me, life finds all its meaning in Christ. Death also has its benefits. 22Suppose I go on living in my body. Then I will be able to carry on my work. It will bear a lot of fruit. But what should I choose? I don’t know! 23I can’t decide between the two. I long to leave this world and be with Christ. That is better by far. 24But it is more important for you that I stay alive. 25I’m sure of this. So I know I will remain with you. And I will continue with all of you to help you grow in your faith. I will also continue to help you be joyful in what you have been taught. 26I’m sure I will be with you again. Then you will be able to boast in Christ Jesus even more because of me.

Living to Honor the Good News

27No matter what happens, live in a way that brings honor to the good news about Christ. Then I will know that you remain strong together in the one Spirit. I will know this if I come and see you or only hear about you. I will know that you work together as one person. I will know that you work to spread the teachings about the good news. 28So don’t be afraid in any way of those who oppose you. This will show them that they will be destroyed and that you will be saved. That’s what God will do. 29Here is what he has given you to do for Christ. You must not only believe in him. You must also suffer for him. 30You are going through the same struggle you saw me go through. As you have heard, I am still struggling.