Ayyukan Manzanni 27 – HCB & TNCV

Hausa Contemporary Bible

Ayyukan Manzanni 27:1-44

Bulus ya tafi Roma a jirgin ruwa

1Sa’ad da aka yanke shawara cewa za mu tashi a jirgin ruwa zuwa Italiya, sai aka danƙa Bulus da waɗansu ’yan kurkuku a hannun wani jarumin mai suna Juliyos, wanda yake na Bataliyar Babban Sarki. 2Muka shiga jirgin ruwa daga Andiramitiyum wanda yake shirin tashi zuwa tasoshin da suke bakin tekun lardin Asiya, sai muka kama tafiya. Aristarkus, mutumin Makidoniya daga Tessalonika, yana tare da mu.

3Kashegari muka sauka a Sidon; Juliyos kuwa, cikin alheri ga Bulus, ya bar shi yă je wajen abokansa domin su biya masa bukatunsa. 4Daga can kuma muka sāke kama tafiya muka zaga ta bayan tsibirin Saifurus saboda iska tana gāba da mu. 5Sa’ad da muka ƙetare tekun da yake sassan gaɓar Silisiya da Famfiliya sai muka sauka a Mira ta Lisiya. 6A can jarumin ya sami wani jirgin ruwan Alekzandariyan da za shi Italiya sai ya sa mu a ciki. 7Tafiyar ta ɗauki kwanaki da yawa muna yi kaɗan-kaɗan da ƙyar muka iso kusa da gaɓar Kinidus. Da iskar ta hana mu ci gaba, sai muka bi ta bayan tsibirin Kirit ɗaura da Salmone. 8Muka ci gaba a gefen gaɓar da ƙyar har muka iso wani wurin da ake kira Kyakkyawan Mafaka, kusa da garin Laseya.

9An riga an ɓata lokaci da yawa, tafiya kuwa ta riga ta zama da hatsari domin a lokacin Azumi27.9 Wato, da Ibraniyanci Ranar Kafara ke nan (Yom Kippur) ya riga ta wuce. Saboda haka Bulus ya gargaɗe su, 10ya ce, “Mutane, ina gani tafiyarmu za tă zama da masifa ta kuma kawo babbar hasara ga jirgin ruwan da kaya, da kuma ga rayukanmu ma.” 11Amma jarumin, a maimakon ya saurari abin da Bulus ya ce, sai ya bi shawarar matuƙi da kuma mai jirgin ruwan. 12Da yake tashar jirgin ruwan ba tă dace a ci damina a can ba, yawanci suka ba yanke shawara cewa mu ci gaba da tafiya, da bege za mu kai Funis mu ci damina a can. Wannan tashar jirgin ruwa ne a Kirit, tana fuskantar kudu maso yamma da kuma arewa maso yamma.

Hadari

13Da iska ta fara busowa daga kudu a hankali, sai suka yi tsammani sun sami abin da suke nema; saboda haka suka janye ƙugiyar jirgin ruwa suka bi ta gefen tsibirin Kirit. 14Ba a jima ba, sai ga wata guguwar iska mai ƙarfin da ake kira “’Yar arewa maso gabas,” ta buga daga tsibirin. 15Iskar ta ci ƙarfin jirgin ruwan har ya kāsa fuskantar iskar; saboda haka muka sallamar mata tă yi ta tura mu. 16Da muka bi ta bayan wani ɗan tsibirin da ake kira Kauda, da ƙyar muka jawo ɗan ƙaramin jirgin kusa da jirgin. 17Da mutanen suka jawo shi cikin babban jirgin ruwan, sai suka sa igiyoyi ta ƙarƙashin jirgin ruwan kanta don su ɗaɗɗaura shi. Don gudun kada a fyaɗa mu da yashin gaɓar Sirtis, sai suka saukar da ƙugiyar jirgin ruwan, suka bari aka yi ta tura jirgin haka. 18Haka muka yi ta shan bugun guguwar hadarin nan kashegari suka fara jajjefar da kayan da jirgin yake ɗauke da su a cikin teku. 19A rana ta uku, da hannuwansu suka jefar da kayan aikin jirgin ruwan a cikin teku. 20Da dai aka yi kwana da kwanaki ba a ga rana ko taurari ba guguwar iska kuma ta ci gaba da bugowa, a ƙarshe muka fid da zuciya za mu tsira.

21Bayan mutanen sun daɗe ba su ci abinci ba, Bulus ya miƙe tsaye a gabansu ya ce, “Mutane, da kun ji shawarata na kada ku tashi daga Kirit, da ba ku fāɗa wannan masifa da hasara ba. 22Amma yanzu ina ƙarfafa ku ku yi ƙarfin hali, domin ba ɗayanku da zai rasa ransa; jirgin ruwan ne kaɗai zai hallaka. 23Jiya da dare wani mala’ikan Allahn da nake nasa nake kuma bauta wa ya tsaya kusa da ni 24ya ce, ‘Kada ka ji tsoro, Bulus. Lalle za ka tsaya a gaban Kaisar a yi maka shari’a; Allah kuma cikin alherinsa ya ba ka dukan rayukan mutanen da suke tafiya tare da kai.’ 25Saboda haka ku yi ƙarfin hali, ku jama’a, gama gaskata Allah a kan cewa yadda aka faɗa mini ɗin nan, haka zai faru. 26Duk da haka, dole a fyaɗa mu a wani tsibiri.”

Jirgin ruwa ya yi hatsari

27A dare na goma sha huɗu iska dai tana ta korarmu a Tekun Adiriyatik, wajen tsakar dare sai masu tuƙin jirgin suka zaci sun yi kusa da ƙasa. 28Sai suka gwada zurfin ruwan suka ga ya kai ƙafa ɗari da ashirin. Bayan ɗan lokaci kaɗan suka sāke gwadawa suka ga zurfin ya kai ƙafa tasa’in. 29Don gudun kada a fyaɗa mu a kan duwatsu, sai suka saki ƙugiyoyin jirgin guda huɗu daga bayan jirgin suka yi fata gari ya waye. 30Cikin ƙoƙarin tserewa daga jirgin, sai masu tuƙin jirgin suka saukar da ɗan ƙaramin jirgin ruwan cikin tekun, suka yi kamar za su saki waɗansu ƙugiyoyi daga sashen gaba na babban jirgin ne. 31Sai Bulus ya ce wa jarumin da kuma sojojin, “In mutanen nan ba su tsaya a cikin jirgin nan ba, ba za ku tsira ba.” 32Sai sojojin suka yayyanke igiyoyin da suke riƙe da ɗan ƙaramin jirgin, suka bar shi ya bi ruwa.

33Kafin gari ya waye Bulus ya roƙe su duka su ci abinci. Ya ce, “Kwana goma sha huɗu ke nan, kuna zama cikin zulumi kun kuma kasance ba abinci, ba ku ci kome ba. 34Ina roƙonku yanzu ku ci abinci. Kuna bukatarsa don ku rayu. Ba ɗayanku da zai rasa ko gashin kansa guda ɗaya.” 35Bayan da ya faɗi haka, sai ya ɗauki burodi ya yi godiya ga Allah a gabansu duka. Sa’an nan ya gutsuttsura ya fara ci. 36Dukansu kuwa suka sami ƙarfafawa, suka kuma ci abinci. 37Dukanmu a jirgin kuwa mutane 276 ne. 38Sa’ad da suka ci iyakar abin da suke so, sai suka rage nauyin jirgin ta wurin zubar da hatsin a cikin tekun.

39Da gari ya waye, ba su gane ƙasar da suke ba, amma suka ga wani lungu da gaci mai yashi, sai suka yanke shawara su kai jirgin can in za su iya. 40Da suka yanke ƙugiyoyin, sai suka bar su a cikin teku a lokaci guda kuma suka ɓalle maɗaurin abin juya jirgin. Sai suka tā da filafilan gaban jirgin daidai yadda iska za tă tura shi gaba, sa’an nan suka nufi gaci. 41Amma jirgin ruwan ya shiga yashi ya kafe. Kan jirgin ya shiga cikin yashin ya kāsa motsi, sai jirgin ya fara farfashewa ta baya saboda haukan raƙuman ruwa.

42Sojojin suka yi niyya su kakkashe ’yan kurkukun don hana waninsu yă yi iyo yă tsere. 43Amma jarumin ya so yă ceci ran Bulus, sai ya hana su aiwatar da niyyarsu. Ya kuma yi umarni duk waɗanda suka iya ruwa su fara fāɗawa zuwa gaci. 44Sauran kuma su bi katakai zuwa can ko kuma a kan tarkacen jirgin ruwan. Ta haka kowa ya kai bakin teku lafiya.

Thai New Contemporary Bible

กิจการของอัครทูต 27:1-44

เปาโลลงเรือไปโรม

1เมื่อมีมติให้เราลงเรือไปยังอิตาลีเปาโลและนักโทษอื่นๆ บางคนจึงถูกส่งตัวให้นายร้อยยูเลียสจากกองจักรวรรดิ 2เรามาลงเรือลำหนึ่งจากเมืองอัดรามิททิยุมซึ่งกำลังจะแล่นไปยังท่าต่างๆ ตามชายฝั่งของแคว้นเอเชีย แล้วเรือก็ออกทะเลอาริสทารคัส ชาวมาซิโดเนียจากเมืองเธสะโลนิกาอยู่กับเราด้วย

3วันรุ่งขึ้นเราแวะที่เมืองไซดอน ฝ่ายยูเลียสมีความกรุณาต่อเปาโลจึงอนุญาตให้เขาไปหาเพื่อนฝูงเพื่อคนเหล่านั้นจะได้จัดหาสิ่งที่จำเป็นให้เขา 4จากที่นั่นเราออกทะเลอีกแล้วแล่นไปทางด้านปลอดลมของเกาะไซปรัสเนื่องจากเราแล่นทวนกระแสลม 5เมื่อแล่นข้ามทะเลนอกชายฝั่งแคว้นซิลีเซียกับปัมฟีเลียเราก็มาแวะที่เมืองมิราในแคว้นลีเซีย 6ที่นั่นนายร้อยพบเรือจากเมืองอเล็กซานเดรียกำลังจะไปอิตาลีจึงให้เราลงเรือลำนั้น 7เราแล่นช้าๆ อยู่หลายวันก็มาถึงเมืองคนีดัสอย่างยากลำบาก เมื่อลมไม่อำนวยเราจึงแล่นมาทางด้านปลอดลมของเกาะครีตตรงข้ามเมืองสัลโมเน 8เราแล่นเรือเลียบฝั่งอย่างยากเย็นและมาถึงที่แห่งหนึ่งเรียกกันว่าท่างามใกล้เมืองลาเซีย 9เมื่อเสียเวลาไปมากและการเดินเรือก็อันตรายเพราะบัดนี้เป็นช่วงหลังวันอดอาหาร27:9 คือ วันลบบาป (ยม คิปปูร์)แล้ว ดังนั้นเปาโลจึงเตือนว่า 10“ท่านทั้งหลาย ข้าพเจ้าเห็นว่าการเดินทางของเราจะประสบหายนะและเพิ่มความเสียหายอย่างใหญ่หลวงแก่ทั้งเรือและสินค้าตลอดจนชีวิตของเราเองด้วย” 11แต่นายร้อยไม่ฟังเปาโลกลับคล้อยตามคำแนะนำของต้นหนและเจ้าของเรือมากกว่า 12เนื่องจากท่างามนั้นไม่เหมาะที่จะจอดในฤดูหนาวคนส่วนใหญ่จึงตกลงให้เราแล่นเรือต่อไป หวังว่าจะไปถึงเมืองฟีนิกซ์และจอดพักในฤดูหนาวที่นั่น ฟีนิกซ์เป็นเมืองท่าของเกาะครีต หันหน้าไปทางตะวันตกเฉียงเหนือกับตะวันตกเฉียงใต้

พายุ

13เมื่อลมใต้พัดมาเบาๆ พวกเขาก็คิดว่าเป็นไปตามที่ปรารถนาแล้ว จึงถอนสมอแล้วแล่นเรือเลียบชายฝั่งเกาะครีต 14ไม่นานเรือก็ถูกลมซึ่งแรงพอๆ กับพายุหมุนที่เรียกกันว่า “ลมตะวันออกเฉียงเหนือ” ซัดออกจากเกาะ 15เรือติดอยู่ในพายุและต้านลมไม่ไหวดังนั้นเราจึงปล่อยเรือไปตามกระแสลม 16ขณะเรากำลังผ่านด้านปลอดลมของเกาะเล็กๆ ที่ชื่อว่าคาวดาเราก็แทบจะรักษาเรือชูชีพไว้ไม่ได้ 17เมื่อชักรอกเรือชูชีพขึ้นมาไว้บนเรือแล้วพวกเขาก็เอาเชือกลอดใต้เรือใหญ่เพื่อยึดเรือไว้ เนื่องจากเกรงว่าจะเกยสันดอนเสอร์ทิสจึงหย่อนสมอเรือและปล่อยเรือไปตามกระแสลม 18พายุซัดกระหน่ำเรืออย่างหนักจนวันรุ่งขึ้นเราต้องทยอยทิ้งสินค้าลงทะเล 19ในวันที่สามพวกเขาต้องทิ้งอุปกรณ์ประจำเรือด้วยมือของพวกเขาเอง 20เมื่อไม่เห็นแสงตะวันแสงดาวตลอดหลายวันและพายุยังพัดกระหน่ำไม่หยุด ในที่สุดเราก็ไม่เหลือความหวังที่จะรอดชีวิต

21หลังจากผู้คนอดอาหารมานานเปาโลก็ยืนขึ้นต่อหน้าพวกเขาและกล่าวว่า “ท่านทั้งหลาย ท่านน่าจะฟังคำแนะนำของข้าพเจ้าที่ไม่ให้แล่นเรือออกจากเกาะครีตจะได้ไม่เจอภยันตรายและการสูญเสียเช่นนี้ 22แต่บัดนี้ข้าพเจ้าขอให้พวกท่านทำใจเข้มแข็งไว้ เพราะจะไม่มีสักคนในพวกท่านต้องเสียชีวิต มีแต่เรือเท่านั้นที่จะอับปาง 23เมื่อคืนนี้เองทูตองค์หนึ่งของพระเจ้าผู้ทรงเป็นเจ้าของตัวข้าพเจ้าผู้ซึ่งข้าพเจ้ารับใช้อยู่มายืนข้างๆ ข้าพเจ้า 24และบอกว่า ‘เปาโลเอ๋ย อย่ากลัวเลย เจ้าต้องยืนให้การต่อหน้าซีซาร์และพระเจ้าทรงเมตตาเจ้าให้คนทั้งปวงที่อยู่ในเรือกับเจ้ารอดชีวิต’ 25ดังนั้นขอให้ท่านทั้งหลายเข้มแข็งไว้เถิดเพราะข้าพเจ้าเชื่อในพระเจ้าว่าจะเป็นตามที่พระองค์ตรัสบอกข้าพเจ้าไว้ 26อย่างไรก็ตามเราจะต้องเกยตื้นที่เกาะแห่งหนึ่ง”

เรืออับปาง

27คืนที่สิบสี่เรายังถูกพายุพัดข้ามทะเลอาเดรียติค27:27 ในสมัยโบราณชื่อนี้หมายถึงบริเวณที่แผ่ไปถึงทางใต้ของอิตาลี ราวๆ เที่ยงคืนพวกลูกเรือรู้สึกว่ามาใกล้แผ่นดินแล้ว 28พวกเขาจึงหยั่งระดับน้ำดู พบว่าลึกประมาณ 37 เมตร27:28 ภาษากรีกว่า20 ออร์กุยอัส หลังจากนั้นไม่นานพวกเขาก็หยั่งระดับน้ำดูอีกและพบว่าลึกประมาณ 27 เมตร27:28 ภาษากรีกว่า15 ออร์กุยอัส 29เรากลัวว่าเรือจะกระแทกกับหินโสโครกจึงทิ้งสมอท้ายเรือสี่ตัวและอธิษฐานขอให้ถึงรุ่งเช้าโดยเร็ว 30พวกลูกเรือหาทางหนีจากเรือใหญ่ จึงหย่อนเรือชูชีพลงทะเลทำทีว่าจะทอดสมอจากหัวเรือ 31เปาโลจึงบอกนายร้อยกับพวกทหารว่า “ถ้าคนเหล่านี้ไม่อยู่ในเรือพวกท่านก็จะไม่รอด” 32ดังนั้นพวกทหารจึงตัดเชือกที่ยึดเรือชูชีพอยู่และปล่อยให้หล่นลงน้ำไป

33จวนรุ่งสางเปาโลชักชวนคนทั้งปวงให้รับประทานอาหาร เขากล่าวว่า “ตลอดสิบสี่วันที่ผ่านมาพวกท่านเฝ้าแต่คอยและไม่มีอะไรตกถึงท้อง พวกท่านไม่ได้รับประทานอะไรเลย 34บัดนี้ข้าพเจ้าขอให้ท่านรับประทานอาหารบ้างจะได้ประทังชีวิตไว้จะไม่มีใครในพวกท่านต้องเสียผมสักเส้นบนศีรษะ” 35ว่าแล้วเปาโลก็หยิบขนมปัง ขอบพระคุณพระเจ้าต่อหน้าพวกเขาทั้งปวง แล้วหักรับประทาน 36ผู้คนได้รับกำลังใจและเริ่มรับประทานอาหาร 37เรามีด้วยกันทั้งหมด 276 คนบนเรือ 38เมื่อพวกเขารับประทานอาหารอิ่มแล้วก็โยนข้าวสาลีทิ้งลงทะเลเรือจะได้เบาขึ้น

39พอรุ่งเช้าพวกเขาจำไม่ได้ว่าเป็นที่ไหนแต่เห็นอ่าวมีหาดทราย จึงตัดสินใจว่าจะแล่นเรือให้เข้าเกยหาดถ้าทำได้ 40พวกเขาจึงตัดสมอเรือปล่อยลงทะเลและในเวลาเดียวกันก็แก้เชือกที่มัดหางเสือแล้วชักใบหัวเรือขึ้นให้กินลมแล่นตรงเข้าหาฝั่ง 41แต่เรือชนสันดอนและเกยตื้น หัวเรือติดแน่นขยับไม่ได้และท้ายเรือก็แตกเป็นชิ้นๆ เพราะแรงคลื่นซัด

42พวกทหารคิดจะฆ่านักโทษเพื่อป้องกันไม่ให้คนใดว่ายน้ำหนี 43แต่นายร้อยต้องการจะช่วยชีวิตเปาโลจึงไม่ให้พวกนั้นทำตามที่คิดและสั่งคนที่ว่ายน้ำเป็นให้กระโดดลงน้ำว่ายเข้าฝั่งก่อน 44ส่วนที่เหลือก็เกาะกระดานหรือชิ้นส่วนของเรือไป โดยวิธีนี้ทุกคนจึงขึ้นฝั่งอย่างปลอดภัย