Ayyukan Manzanni 1 – HCB & NUB

Hausa Contemporary Bible

Ayyukan Manzanni 1:1-26

An ɗauki Yesu zuwa sama

1A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar 2har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa. 3Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah. 4A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai. 5Gama Yohanna ya yi baftisma da1.5 Ko kuwa a cikin ruwa, amma a cikin ’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”

6Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”

7Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa. 8Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”

9Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.

10Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su. 11Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”

An zaɓi Mattiyas yă ɗauki matsayin Yahuda

12Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin. 13Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne,

Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus;

Filibus da Toma;

Bartolomeyu da Mattiyu;

Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.

14Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da ’yan’uwansa.

15A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin ’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin) 16ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu 17dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”

18(Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo. 19Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)

20Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa,

“ ‘Bari wurinsa yă zama babu kowa;

kada kowa ya zauna a cikinsa,’1.20 Zab 69.25

kuma,

“ ‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’1.20 Zab 109.8

21Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu, 22farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”

23Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas. 24Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa 25ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.” 26Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.

Swedish Contemporary Bible

Apostlagärningarna 1:1-26

Löftet om den heliga Anden – Jesus återvänder till himlen

1I min första bok1:1 Lukasevangeliet. berättade jag, ärade Theofilos, om allt som Jesus började göra och undervisa om 2ända fram till den dag då han togs upp till himlen, efter att han genom den heliga Anden gett sina befallningar till apostlarna1:2 Eller sändebuden. som han hade utvalt. 3Han visade sig för dem efter sitt lidande och bevisade på många sätt för dem att han levde. Under fyrtio dagar visade han sig för dem och talade om Guds rike.

4Vid ett av dessa tillfällen då han åt med dem, sa han till dem: ”Lämna inte Jerusalem, utan vänta på vad Fadern har utlovat och som ni har hört mig tala om! 5Johannes döpte er i vatten men om några få dagar ska ni bli döpta i den heliga Anden.”

6När de var samlade frågade de Jesus: ”Herre, är det nu du ska återupprätta Israel som kungarike?” 7Han svarade då: ”Det är inte er sak att veta tider och stunder som Fadern i sin makt har bestämt. 8Men när den heliga Anden kommer över er ska ni få kraft och ni ska vittna om mig, både i Jerusalem, i Judeen, i Samarien och över hela jorden.”

9Strax efter att han sagt detta, såg de honom lyftas upp och ett moln tog honom ur deras åsyn. 10De försökte titta upp mot himlen när han uppsteg, då plötsligt två vitklädda män stod bland dem 11och sa: ”Ni män från Galileen, varför står ni här och tittar upp mot himlen? Denne Jesus som har tagits upp från er till himlen ska komma tillbaka på samma sätt som ni såg honom fara upp på.”

Mattias blir vald att ersätta Judas

(Matt 10:2-4; Mark 3:16-19; Luk 6:14-16)

12De återvände då till Jerusalem från det berg som kallas Olivberget och som ligger en sabbatsväg1:12 Man fick färdas en knapp kilometer på sabbaten. från staden. 13När de kom fram, gick de upp till det rum på andra våningen där de brukade hålla till. Det var Petrus, Johannes, Jakob, Andreas, Filippos, Tomas, Bartolomaios, Matteus, Jakob, son till Alfaios, Simon seloten1:13 Selot betyder ivrare. Antingen var Simon ivrig till sin läggning eller så hade tillhört han ”seloterna”, ett politiskt parti som ville göra uppror mot romarna. Eller: den ivrige, och Judas, son till Jakob. 14Alla dessa höll ihop och bad ständigt tillsammans, så också flera kvinnor, Maria, Jesus mor och Jesus bröder.

15En gång under dessa dagar när omkring 120 troende var samlade, reste sig Petrus upp bland dem och sa: 16”Mina syskon, det som var förutsagt i Skriften skulle gå i uppfyllelse,1:16 Förutsägelsen är citerad i v. 20. som den heliga Anden meddelade genom David om Judas, han som vägledde dem som grep Jesus. 17Han var en av oss med samma uppdrag som vi. 18(Men för de pengar han fick för sitt brott köpte han en åker och där föll han framstupa så att hans kropp sprack och inälvorna rann ut. 19Hela Jerusalems invånare fick kännedom om det, och platsen kallades på deras eget språk Akeldamak som betyder ’Blodsåkern’.) 20Det står nämligen i Psaltaren:

’Låt hans hem stå öde

låt ingen mer bo där’,

och:

’Låt en annan ta hans tjänst.’ 1:20 Se Ps 69:26; 109:8; i det första citatet finns små skillnader till psaltartexten.

21Därför måste nu någon annan som har varit med oss under hela den tid då Herren Jesus kom och gick mitt ibland oss, 22från det att han döptes av Johannes till den dag då han togs upp till himlen, någon av dem måste tillsammans med oss vittna om hans uppståndelse.”

23Man föreslog då två män: Josef Barsabbas som också kallades Justus och Mattias. 24Sedan bad de: ”Herre, du känner allas hjärtan. Visa oss vilken av de här två som du har utvalt 25till denna tjänst som apostel istället för Judas som svek sitt uppdrag och har gått till den plats där han hör hemma.”

26Sedan kastade de lott som föll på Mattias och han blev vald till apostel tillsammans med de elva.