Afisawa 6 – HCB & OL

Hausa Contemporary Bible

Afisawa 6:1-24

’Ya’ya da iyaye

1Ku ’ya’ya, ku yi biyayya ga iyayenku, gama ku na Ubangiji, abin da ya dace ku yi ke nan. 2Doka ta farko wadda aka haɗa da alkawari ita ce, “Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, 3don ka zauna lafiya, ka kuma yi tsawon rai a duniya.”6.3 M Sh 5.16

4Ku kuma iyaye, kada ku tsokane ’ya’yanku. Ku yi musu reno mai kyau. Ku koyar da su, ku kuma gargaɗe su game da Ubangiji.

Bayi da iyayengiji

5Ku bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku na duniya. Ku nuna musu halin bangirma, kuna kuma yin musu biyayya cikin dukan abu, da zuciya ɗaya kamar ga Kiristi kuke yi. 6Ku yi aiki sosai, ba don kawai ku gamshe su sa’ad da suke kallonku ba. Da yake ku bayin Kiristi ne, ku aikata nufin Allah da dukan zuciyarku. 7Ku yi aikinku da kyakkyawar niyya, sai ka ce ga Ubangiji kuke yi, ba mutane ba. 8Gama kun san cewa Ubangiji zai ba da lada ga kowa gwargwadon kowane aiki nagarin da ya yi, ko shi bawa ne, ko ’yantacce.

9Ku kuma masu bayi, dole ku bi da bayinku da kyau. Ku daina ba su tsoro. Ku tuna, ku da su, Maigida ɗaya kuke da shi a sama, kuma ba ya nuna bambanci.

Kayan yaƙi na Allah

10A ƙarshe, bari ƙarfin ikon Ubangiji yă ba ku ƙarfi. 11Ku yafa dukan kayan yaƙin da Allah yake bayarwa, don ku iya kāre kanku daga dabarun Shaiɗan. 12Gama ba da mutane da suke nama da jini ne muke yaƙi ba. Muna yaƙi ne da ikoki, da hukumomi, da masu mulkin duhu, da kuma a ikokin da suke cikin a sararin sama. 13Saboda haka sai ku yafa dukan kayan yaƙi na Allah, domin sa’ad da ranar mugun nan ta zo, ku iya yin tsayin daka, bayan kuma kuka gama kome, ku dāge. 14Saboda haka fa ku dāge, ku sa gaskiya tă zama ɗamararku, adalci yă zama sulkenku, 15shirin kai bisharar salama yă zama kamar takalmi a ƙafafunku. 16Ban da waɗannan kuma, ku ɗauki garkuwar bangaskiya, wadda za ku iya kashe dukan kibiyoyin wutar Mugun nan da ita. 17Ku kuma ɗauki hular kwano na ceto, da takobin Ruhu, wato, Maganar Allah.

18A koyaushe ku kasance kuna addu’a da roƙo ta wurin ikon Ruhu ba fasawa. A kan wannan manufa ku zauna a faɗake da matuƙar naci, kuna yin wa dukan mutanen Ubangiji addu’a. 19Ku kuma yi addu’a domina, don duk sa’ad da na buɗe bakina, in sami kalmomi babu tsoro, don in sanar da asirin bishara, 20wadda nake jakadanta cikin sarƙoƙi. Ku yi addu’a don in iya yin shelarta babu tsoro, yadda ya kamata in yi.

Gaisuwar ƙarshe

21Tikikus, ƙaunataccen ɗan’uwa da kuma amintaccen bawa cikin Ubangiji, zai faɗa muku kome, domin ku ma ku san yadda nake, da kuma abin da nake yi. 22Na aike shi gare ku musamman don wannan, domin ku san yadda muke, yă kuma ƙarfafa ku.

23’Yan’uwa, salama tare da ƙauna da kuma bangaskiya daga Allah Uba da Ubangiji Yesu Kiristi su kasance tare da ku.

24Alheri yă tabbata ga dukan masu ƙaunar Ubangiji Yesu Kiristi da ƙauna marar ƙarewa.

O Livro

Efésios 6:1-24

Filhos e pais

1Vocês, filhos, porque são do Senhor, obedeçam aos vossos pais, pois essa é a atitude correta. 2“Honra o teu pai e a tua mãe.” Dos dez mandamentos de Deus este é o primeiro que tem uma promessa: 3“Para que tenhas uma longa vida na Terra.”6.3 Dt 5.16.

4Vocês, os pais, não exasperem os vossos filhos. Antes eduquem-nos seguindo os conselhos e a doutrina do Senhor.

Trabalhadores e patrões

5E vocês, escravos, obedeçam aos vossos senhores aqui na Terra, executando conscienciosamente as vossas tarefas, com respeito e temor, como se fosse para Cristo. 6Trabalhem bem; não o façam só para agradar aos patrões, quando estes vos estão a ver, 7mas antes como trabalhando para Cristo e como quem está a executar de coração a vontade de Deus; 8sabendo também que cada um receberá do Senhor a recompensa por todo o bem que fizer, quer se trate de escravo ou livre.

9Quanto a vocês, os patrões, façam a mesma coisa, segundo o mesmo princípio, sem abusar da vossa autoridade, pois lembrem-se de que Deus no céu é Senhor tanto deles como vosso, e que não faz distinção entre pessoas.

A armadura de Deus

10Por último, quero recomendar-vos que procurem fortalecer-se através da comunhão com o Senhor e com a energia do seu poder. 11Estejam equipados com todas as armas de Deus para que possam permanecer firmes sem cair nas astutas ciladas do Diabo. 12Pois na verdade o nosso combate não é contra seres humanos, mas sim contra governos e autoridades, contra ditaduras que atuam nas trevas, contra verdadeiros exércitos de espíritos do mal nos domínios celestiais.

13Por isso, utilizem todas as armas de Deus para que possam resistir, no dia em que algo de maligno vier à vossa vida, e para que depois de terem vencido tudo continuem firmes. 14Mantenham-se pois firmes, cingidos com o cinturão da verdade e protegidos com o colete da justiça de Deus. 15Que os vossos pés estejam firmados no solo do evangelho da paz. 16Tenham sobretudo a fé, pois é um escudo que vos protege contra as flechas incendiárias disparadas pelo Maligno sobre as vossas vidas. 17Também vos é necessário o capacete da salvação, assim como a espada do Espírito, que é a palavra de Deus. 18Orem a Deus com toda a perseverança, em toda a ocasião, de acordo com o Espírito Santo. Sejam vigilantes no emprego persistente desta arma da oração, apresentando também a Deus as necessidades dos outros crentes.

19O mesmo peço que façam por mim, para que Deus, quando falo em seu nome, me dê a possibilidade de o fazer ousadamente, a fim de tornar claro o sentido mais profundo do evangelho. 20E é por pregar esta mensagem, pela qual sou como um embaixador, que me encontro aqui nesta prisão. Mas peçam a Deus que eu possa continuar a falar corajosamente, pois convém que ela seja conhecida.

Saudações finais

21Tíquico, nosso querido irmão na fé e fiel companheiro no serviço do Senhor, vos porá ao corrente da minha situação, da minha saúde, dos meus projetos. 22Ele vai aí para que saibam como nós vamos, para vos dar notícias e assim fiquem mais animados.

23Que a paz de Deus habite no vosso meio, assim como o amor cristão e a fé comunicada por Deus Pai e pelo Senhor Jesus Cristo. 24Que a graça do Senhor esteja com aqueles que amam o nosso Senhor Jesus Cristo perseverantemente. Amém!