Afisawa 1 – HCB & BDS

Hausa Contemporary Bible

Afisawa 1:1-23

1Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu,

Zuwa ga tsarkaka da suke a Afisa,1.1 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā ba su da a Afisa. da kuma suke amintattu1.1 Ko kuwa masu bi waɗanda cikin Kiristi Yesu.

2Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.

Albarkun ruhaniya a cikin Kiristi

3Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ya kawo mana kowace albarka ta ruhaniya daga sama. 4Gama ya zaɓe mu a cikin Kiristi tun dā can, kafin ma a halicci duniya don mu zama masu tsarki da kuma marasa aibi a gabansa. 5A cikin ƙauna, ya1.4,5 Ko kuwa gani cikin ƙauna. 5 Ya ƙaddara mu zama ’ya’yansa na riƙo ta wurin Kiristi Yesu, bisa ga nufinsa na alheri. 6Ya yi haka don mu yabi Allah saboda alherin da ya yi mana saboda mu na ƙaunataccen Ɗansa ne. 7A cikinsa muka sami fansa ta wurin jininsa, wato, yafewar zunubanmu. Kiristi ya yi wannan saboda yawan alherin Allah 8wanda ya ba mu babu iyaka tare da dukan hikima da fahimta. 9Allah ya yi abin da ya nufa, ya kuma sanar mana shirin asirin da ya riga ya shirya yă cika ta wurin Kiristi. 10Nufinsa ke nan, idan lokaci ya cika, yă harhaɗa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikon Kiristi, wato, dukan abubuwan da suke sama da abubuwan da suke ƙasa.

11A cikinsa ne kuma aka zaɓe mu mu sami gādo daga Allah,1.11 Ko kuwa mun zama abin gādon Allah an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi. 12Manufar Allah ita ce cewa mu da muka fara sa bege a cikin Kiristi, mu yi zaman yabon ɗaukakar Allah. 13An kuma haɗa ku a cikin Kiristi lokacin da kuka ji saƙon nan na gaskiya, wanda yake labari mai daɗi na cetonku. Da kuka ba da gaskiya, sai aka yi muku alamar shaida a cikinsa da Ruhu Mai Tsarki. 14Ruhu Mai Tsarkin nan shi ne tabbacin da Allah ya yi na cewa zai ba mu kome da ya yi alkawari, har ya sa muka sani nan gaba Allah zai ceci waɗanda suke nasa. Wannan kuwa domin yabon ɗaukakarsa ne.

Godiya da addu’a

15Saboda haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kuma ƙaunar da kuke yi wa dukan mutanen Allah, 16ban fasa yin godiya saboda ku ba, ina tuna da ku cikin addu’o’ina. 17Ina ta roƙo cewa Allah na Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba Maɗaukaki, yă ba ku Ruhun hikima da na ganewa, domin ku san shi da kyau. 18Ina kuma addu’a cewa zuciyarku tă waye don ku gane ko mene ne sa zuciyan nan da ya kira ku a kansa, ku kuma san darajar dukiyan nan wadda take ta mutanen Allah, wato, albarkunsa. 19Ina addu’a ku san girman ikon Allah wanda ya wuce misali, wanda yake namu. Ikon da yake aiki a cikinmu, ɗaya ne da ikon nan 20da ya tā da Kiristi daga matattu, ya kuma sa ya zauna a hannun damansa a cikin mulkin samaniya. 21Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. 22Allah ya sa kome a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma ba shi iko a kan kome don amfanin ikkilisiya. 23Kuma ikkilisiya ce jikinsa; ta kuma cika da Kiristi, wanda ya cika kome ta kowace hanya.

La Bible du Semeur

Ephésiens 1:1-23

Salutation

1Paul, apôtre de Jésus-Christ par la volonté de Dieu, salue ceux qui [à Ephèse1.1 Les mots : à Ephèse sont absents de plusieurs manuscrits.] font partie du peuple saint, et croient en Jésus-Christ.

2Que la grâce et la paix vous soient accordées par Dieu notre Père et par le Seigneur Jésus-Christ.

Le salut en Christ

La grâce de Dieu en Christ

3Béni soit Dieu,

le Père de notre Seigneur

Jésus-Christ,

car il nous a comblés

de toute bénédiction de l’Esprit

dans le monde céleste

en raison de notre union avec Christ.

4En lui,

bien avant de poser

les fondations du monde,

il nous avait choisis

pour que nous soyons saints

et sans reproche devant lui.

Puisqu’il nous a aimés,

5il nous a destinés d’avance

à être ses enfants

qu’il voulait adopter

par Jésus-Christ.

Voilà ce que, dans sa bonté,

il a voulu pour nous

6afin que nous célébrions

la gloire de sa grâce

qu’il nous a accordée

en son Fils bien-aimé.

7En Christ,

parce qu’il s’est offert en sacrifice,

nous avons obtenu la délivrance,

le pardon de nos fautes.

Dieu a ainsi manifesté sa grâce

dans toute sa richesse,

8et il l’a répandue sur nous

avec surabondance,

en nous donnant pleine sagesse

et pleine intelligence,

9nous ayant fait connaître

le secret de son plan.

Ce plan, il l’a fixé d’avance,

dans sa bonté,

en Christ,

10pour conduire les temps

vers l’accomplissement.

Selon ce plan,

tout ce qui est au ciel

et tout ce qui est sur la terre

doit être harmonieusement réuni1.10 Paul emploie ici un verbe qui signifie résumer, récapituler. Il est difficile de savoir ce qu’il voulait dire exactement. Certains traduisent : doit être restauré. D’autres comprennent : doit être réuni sous le gouvernement de Christ.

en Christ.

11Et c’est aussi en Christ

qu’il nous a accordé

notre part d’héritage1.11 Autre traduction : que nous sommes devenus sa possession.

conformément à ce qu’avait fixé

celui qui met en œuvre toutes choses,

selon l’intention qui inspire

sa décision.

Ainsi, nous avons été destinés d’avance

12à célébrer sa gloire

nous qui, les tout premiers,

avons placé notre espérance

dans le Messie.

13Et en Christ, vous aussi,

vous avez entendu

le message de vérité,

cet Evangile

qui vous apportait le salut ;

oui, c’est aussi en Christ

que vous qui avez cru,

vous avez obtenu de Dieu

l’Esprit Saint qu’il avait promis

et par lequel

il vous a marqués de son sceau1.13 Le sceau apposé sur une marchandise marquait le changement de propriétaire.

en signe que vous lui appartenez.

14Cet Esprit constitue

l’acompte de notre héritage

en attendant la délivrance

du peuple que Dieu s’est acquis1.14 Autre traduction : la délivrance par laquelle nous entrerons en possession de notre héritage..

Ainsi tout aboutit

à célébrer sa gloire.

Prière de Paul pour les Ephésiens

15Pour toutes ces raisons, moi aussi, après avoir entendu parler de votre foi au Seigneur Jésus et de votre amour pour tous les membres du peuple saint, 16je ne cesse de dire ma reconnaissance à Dieu à votre sujet quand je fais mention de vous dans mes prières.

17Je demande que le Dieu de notre Seigneur Jésus-Christ, le Père qui possède la gloire, vous donne, par son Esprit, sagesse et révélation, pour que vous le connaissiez ; 18qu’il illumine ainsi votre intelligence afin que vous compreniez en quoi consiste l’espérance à laquelle vous avez été appelés, quelle est la glorieuse richesse de l’héritage que Dieu vous fera partager avec les membres du peuple saint, 19et quelle est l’extraordinaire grandeur de la puissance qu’il met en œuvre en notre faveur, à nous qui plaçons notre confiance en lui. Cette puissance, en effet, il l’a déployée dans toute sa force 20en la faisant agir en Christ lorsqu’il l’a ressuscité et l’a fait siéger à sa droite1.20 Ps 110.1., dans le monde céleste. 21Là, Christ est placé bien au-dessus de toute Autorité, de toute Puissance, de toute Domination et de toute Souveraineté1.21 Ces expressions se rapportent à des êtres surnaturels (angéliques ou démoniaques) auxquels les erreurs que certains répandaient dans les Eglises d’Asie Mineure donnaient une grande importance (voir 3.10 ; Col 1.16 ; 2.15). : au-dessus de tout nom qui puisse être cité, non seulement dans le monde présent, mais aussi dans le monde à venir. 22Dieu a tout placé sous ses pieds1.22 Voir Ps 8.7., et Christ qui domine toutes choses, il l’a donné pour chef à l’Eglise 23qui est son corps, lui en qui habite la plénitude du Dieu qui remplit tout en tous1.23 Autre traduction : à l’Eglise 23 qui est son corps, où se manifeste pleinement celui qui remplit tout en tous (cf. 3.19)..