2 Tessalonikawa 1 – HCB & CRO

Hausa Contemporary Bible

2 Tessalonikawa 1:1-12

1Bulus, da Sila, da Timoti,

Zuwa ga ikkilisiya ta Tessalonikawa ta Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi.

2Alheri da salama daga Allah Uba da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.

Godiya da addu’a

3Dole kullum mu gode wa Allah saboda ku, ’yan’uwa, haka kuwa ya dace, domin bangaskiyarku tana girma gaba-gaba, ƙaunar da kowannenku yake yi wa juna kuwa tana ƙaruwa. 4Saboda haka, a cikin ikkilisiyoyin Allah muna taƙama game da daurewarku da kuma bangaskiyarku cikin dukan tsanani da gwaje-gwajen da kuke sha.

5Dukan wannan yana tabbatar cewa hukuncin Allah daidai ne, saboda haka kuma za a lissafta ku a kan kun cancanci mulkin Allah, wanda dominsa ne kuke shan wahala. 6Allah mai adalci ne, Zai sāka wa masu ba ku wahala da wahala 7yă kuma sauƙaƙa muku ku da kuke wahala, har ma da mu. Wannan zai faru sa’ad da aka bayyana Ubangiji Yesu daga sama cikin wuta mai ci tare da mala’ikunsa masu iko. 8Zai hukunta waɗanda ba su san Allah ba da kuma waɗanda ba su yi biyayya da bisharar Ubangijinmu Yesu ba. 9Za a hukunta su da madawwamiyar hallaka a kuma kau da su daga gaban Ubangiji da kuma daga ɗaukakar ikonsa 10a ranar da zai dawo don a ɗaukaka shi a cikin mutanensa masu tsarki, yă kuma zama abin banmamaki ga dukan waɗanda suka gaskata. Wannan ya haɗa har da ku, domin kun gaskata shaidar da muka yi muku.

11Sane da wannan, kullum muna addu’a saboda ku, don Allahnmu yă sa ku cancanci kiransa, ta wurin ikonsa kuma yă cika kowace manufarku mai kyau da kuma kowane aikin da bangaskiyarku ta iza. 12Muna wannan addu’a don sunan Ubangijinmu Yesu yă sami ɗaukaka a cikinku, ku kuma a cikinsa, bisa ga alherin Allahnmu da na Ubangiji Yesu Kiristi.1.12 Ko kuwa Allah da Ubangiji, Yesu Kiristi

Knijga O Kristu

2 Solunjanima 1:1-12

1Ovo je pismo od Pavla, Sile1:1 U grčkome: Silvana. i Timoteja solunskoj Crkvi koja je u Bogu, našemu Ocu, i u Gospodinu Isusu Kristu.

2Neka vam je milost i mir od Boga Oca i od Gospodina Isusa Krista.

Ohrabrenje u progonstvu

3Draga braćo i sestre, ne možemo a da uvijek ne zahvaljujemo Bogu za vas, za vašu vjeru koja jača i za vašu veliku međusobnu ljubav. 4Ponosno govorimo drugim Božjim crkvama o vašoj postojanoj vjeri u progonstvima i u nevoljama koje trpite.

5One su samo najava pravednoga Božjeg suda na kojemu će vas Bog proglasiti dostojnima svojega Kraljevstva za koje i trpite. 6Bog će pravedno kazniti vaše progonitelje patnjom, 7a vama progonjenima, kao i nama, dati spokoj kad se s neba objavi Gospodin Isus. On će doći s moćnim anđelima 8i s plamenim ognjem te donijeti osvetu onima koji ne priznaju Boga i ne žele se pokoriti Radosnoj vijesti o našemu Gospodinu Isusu Kristu. 9Bit će kažnjeni vječnom propašću, zauvijek odvojeni od Gospodnjega lica i od njegove silne slave 10na dan kada on dođe primiti slavu i čast od svojega svetog naroda, od svih vjernika. Među njima ste i vi jer ste povjerovali našemu svjedočanstvu o njemu.

11Zato se stalno molimo za vas, da vas Bog učini dostojnima života na koji vas je pozvao i da on svojom snagom dovrši svaku vašu dobru nakanu i svako dobro djelo— 12da bi zbog vas svi slavili ime našega Gospodina Isusa te da i vi budete proslavljeni u njemu po milosti našega Boga i Gospodina Isusa Krista.