2 Korintiyawa 13 – HCB & NIVUK

Hausa Contemporary Bible

2 Korintiyawa 13:1-14

Gargaɗin ƙarshe

1Wannan za tă zama ziyarata ta uku a wurinku ke nan. “Dole a tabbatar da kowace magana ta bakin shaidu biyu ko uku.”13.1 M Sh 19.15 2Na riga na yi muku gargaɗi sa’ad da nake tare da ku a zuwana na biyu. Yanzu da ba na nan tare da ku, ina maimaita irin gargaɗin nan domin in na zo ba wanda zai kuɓuce wa horon nan, 3da yake kuna neman tabbaci cewa Kiristi yana magana ta wurina ne. To, ai, shi ba rarrauna ba ne a gare ku, amma ƙaƙƙarfa ne a cikinku. 4Ko da yake tabbatacce an gicciye shi cikin rashin ƙarfi, duk da haka, yana rayuwa bisa ga ikon Allah. Haka mu ma marasa ƙarfi ne a cikinsa, amma ta wurin ikon Allah za mu rayu tare da shi don mu yi muku hidima.

5Ku gwada kanku ku gani ko kuna cikin bangaskiya; ku auna kanku. Ashe, ba ku san cewa Kiristi Yesu yana cikinku ba? Sai ko in kun fāɗi gwajin. 6Ina fata za ku gane cewa ba mu fāɗi gwajin ba. 7Muna addu’a ga Allah kada ku aikata wani laifi. Ba don mutane su gani cewa mun ci gwajin ba ne, a’a, sai dai don ku yi abin da yake daidai, ko da yake zai zama kamar mun fāɗi gwajin ne. 8Kai, ba dama mu saɓa wa gaskiya, sai dai mu bi bayan gaskiyar. 9Murna muke sa’ad da ba mu da ƙarfi, ku kuwa kuna da ƙarfi. Addu’armu ita ce, ku zama cikakku. 10Shi ya sa nake rubuta waɗannan abubuwa, sa’ad da ba na nan tare da ku, domin sa’ad da na zo, kada yă zama mini tilas in yi muku tsanani a game da nuna ikon nan da Ubangiji ya ba ni saboda ingantawa, ba saboda rushewa ba.

Gaisuwa ta ƙarshe

11A ƙarshe ’yan’uwa, sai wata rana. Ku yi ƙoƙari ku zama cikakku. Ku saurari roƙona, ku zama da tunani ɗaya, ku yi zaman salama. Allah na ƙauna da salama kuwa zai kasance tare da ku.

12Ku gaggai da juna da sumba mai tsarki.

13Dukan tsarkaka suna gaishe ku.

14Alherin Ubangiji Yesu Kiristi, da ƙaunar Allah, da zumuntar Ruhu Mai Tsarki su kasance tare da ku duka.

New International Version – UK

2 Corinthians 13:1-14

Final warnings

1This will be my third visit to you. ‘Every matter must be established by the testimony of two or three witnesses.’13:1 Deut. 19:15 2I already gave you a warning when I was with you the second time. I now repeat it while absent: on my return I will not spare those who sinned earlier or any of the others, 3since you are demanding proof that Christ is speaking through me. He is not weak in dealing with you, but is powerful among you. 4For to be sure, he was crucified in weakness, yet he lives by God’s power. Likewise, we are weak in him, yet by God’s power we will live with him in our dealing with you.

5Examine yourselves to see whether you are in the faith; test yourselves. Do you not realise that Christ Jesus is in you – unless, of course, you fail the test? 6And I trust that you will discover that we have not failed the test. 7Now we pray to God that you will not do anything wrong – not so that people will see that we have stood the test but so that you will do what is right even though we may seem to have failed. 8For we cannot do anything against the truth, but only for the truth. 9We are glad whenever we are weak but you are strong; and our prayer is that you may be fully restored. 10This is why I write these things when I am absent, that when I come I may not have to be harsh in my use of authority – the authority the Lord gave me for building you up, not for tearing you down.

Final greetings

11Finally, brothers and sisters, rejoice! Strive for full restoration, encourage one another, be of one mind, live in peace. And the God of love and peace will be with you.

12Greet one another with a holy kiss.

13All God’s people here send their greetings.

14May the grace of the Lord Jesus Christ, and the love of God, and the fellowship of the Holy Spirit be with you all.