1 Korintiyawa 2 – HCB & NSP

Hausa Contemporary Bible

1 Korintiyawa 2:1-16

1Da na zo wurinku ’yan’uwa, ban zo da iya magana ko wani mafificin hikima yayinda na yi muku shelar shaida game da Allah ba. 2Don na ƙudura a raina sa’ad da nake tare da ku cewa ba zan mai da hankali ga kome ba sai dai Yesu Kiristi wanda aka gicciye. 3Na zo wurinku cikin rashin ƙarfi da tsoro, da rawan jiki ƙwarai. 4Saƙona da wa’azina ba su zo cikin hikima da kalmomin lallashi ba, sai dai da nuna ikon Ruhu, 5domin kada bangaskiyarku ta dogara a kan hikimar mutane, sai dai a kan ikon Allah.

Hikima daga Ruhu

6Duk da haka, muna sanar da saƙon hikima cikin waɗanda suka balaga, amma ba hikima irin ta wannan zamani ba ne, ko kuwa irin ta masu mulkin zamanin nan, waɗanda za su shuɗe ba. 7A’a, muna magana ne a kan asirin hikimar Allah, hikimar da tun dā, take a ɓoye, wadda Allah ya ƙaddara domin ɗaukakarmu, tun kafin farkon zamanai. 8Ba ko ɗaya daga cikin masu mulkin wannan zamani da ya fahimce ta, gama da a ce sun fahimce ta, da ba su gicciye Ubangiji mai ɗaukaka ba. 9Duk da haka, kamar yadda yake a rubuce cewa,

“Ba idon da ya taɓa gani,

ba kunnen da ya taɓa ji,

ba kuma zuciyar da ta taɓa tunanin

abin da Allah ya shirya wa masu ƙaunarsa.”2.9 Ish 64.4

10Amma Allah ya bayyana mana shi ta wurin Ruhunsa.

Ruhu yana bincika dukan abubuwa, har ma da abubuwa masu zurfi na Allah. 11Wane ne a cikin mutane ya san tunanin mutum, in ba ruhun mutumin da yake cikinsa ba? Haka kuma ba wanda ya san tunanin Allah, sai dai Ruhun Allah. 12Ba mu karɓi ruhun duniya ba, sai dai Ruhun da yake daga Allah, domin mu fahimci abin da Allah ya ba mu hannu sake. 13Wannan shi ne abin da muke sanarwa, ba da kalmomin da muka koya ta wurin hikimar mutum ba, amma da kalmomin da Ruhu yake koyarwa, muna faɗin gaskiya ta ruhaniya da kalmomin ruhaniya. 14Mutumin da ba shi da Ruhu, ba ya yarda da abubuwan da suka fita daga Ruhun Allah, domin wauta ce a gare shi. Ba kuwa zai fahimce su ba, domin ta Ruhu ne ake fahimtarsu. 15Mutumin ruhaniya yakan gwada dukan abubuwa, amma shi kansa ba ya ƙarƙashin shari’ar mutum.

16“Wa ya taɓa sanin hankalin Ubangiji,

har da zai koya masa?”2.16 Ish 40.13

Amma muna da tunani iri na Kiristi ne.

New Serbian Translation

1. Коринћанима 2:1-16

Порука о разапетом Христу

1А када сам дошао к вама, браћо, нисам наступио са узвишеним говором или мудрошћу да вам навестим Божију тајну. 2Одлучио сам, наиме, да међу вама не знам ни за шта друго осим за Исуса Христа, и то разапетога. 3Тако сам се пред вама појавио у слабости, са страхом и великом тремом. 4Па и мој говор и моја проповед нису се заснивали на убедљивим речима људске мудрости, него на доказивању силе Духа, 5да се ваша вера не би темељила на људској мудрости, него на Божијој сили.

Божија мудрост

6Али мудрост навешћујемо међу зрелима, али не мудрост овога света, нити од владара овога света који пропадају. 7Напротив, ми навешћујемо Божију мудрост, тајну и скривену, коју је Бог пре свих векова предодредио за нашу славу. 8Ту мудрост ниједан од владара овога света није упознао, јер да су је упознали, не би разапели Господа славе. 9Него, као што је написано:

„Што око није видело,

и ухо није чуло,

и у људско срце није допрло,

то је Бог припремио за оне који га воле.“

10А нама је Бог то открио по Духу, јер Дух све истражује, па и дубине Божије. 11Јер ко други познаје човекове мисли, осим духа који је у њему самом? Исто тако, нико не познаје Божије мисли осим Духа Божијег. 12А ми нисмо примили духа овога света, него Духа који долази од Бога, да бисмо знали шта нам је Бог даровао. 13Ми говоримо о овим стварима, али не наученим речима људске мудрости, него онако како нас је научио Дух, тумачећи духовне истине онима који су духовни. 14Телесни човек, пак, не прихвата истине које долазе од Божијег Духа. За њега су оне лудост, те их не може разумети, јер о тим истинама треба расуђивати уз помоћ Божијег Духа. 15А онај који је примио Божијег Духа расуђује о свему, а сам не подлеже суду других. 16„Јер, ко је упознао ум Господњи да би га саветовао?“ А ми имамо ум Христов.