1 Korintiyawa 2 – HCB & NEN

Hausa Contemporary Bible

1 Korintiyawa 2:1-16

1Da na zo wurinku ’yan’uwa, ban zo da iya magana ko wani mafificin hikima yayinda na yi muku shelar shaida game da Allah ba. 2Don na ƙudura a raina sa’ad da nake tare da ku cewa ba zan mai da hankali ga kome ba sai dai Yesu Kiristi wanda aka gicciye. 3Na zo wurinku cikin rashin ƙarfi da tsoro, da rawan jiki ƙwarai. 4Saƙona da wa’azina ba su zo cikin hikima da kalmomin lallashi ba, sai dai da nuna ikon Ruhu, 5domin kada bangaskiyarku ta dogara a kan hikimar mutane, sai dai a kan ikon Allah.

Hikima daga Ruhu

6Duk da haka, muna sanar da saƙon hikima cikin waɗanda suka balaga, amma ba hikima irin ta wannan zamani ba ne, ko kuwa irin ta masu mulkin zamanin nan, waɗanda za su shuɗe ba. 7A’a, muna magana ne a kan asirin hikimar Allah, hikimar da tun dā, take a ɓoye, wadda Allah ya ƙaddara domin ɗaukakarmu, tun kafin farkon zamanai. 8Ba ko ɗaya daga cikin masu mulkin wannan zamani da ya fahimce ta, gama da a ce sun fahimce ta, da ba su gicciye Ubangiji mai ɗaukaka ba. 9Duk da haka, kamar yadda yake a rubuce cewa,

“Ba idon da ya taɓa gani,

ba kunnen da ya taɓa ji,

ba kuma zuciyar da ta taɓa tunanin

abin da Allah ya shirya wa masu ƙaunarsa.”2.9 Ish 64.4

10Amma Allah ya bayyana mana shi ta wurin Ruhunsa.

Ruhu yana bincika dukan abubuwa, har ma da abubuwa masu zurfi na Allah. 11Wane ne a cikin mutane ya san tunanin mutum, in ba ruhun mutumin da yake cikinsa ba? Haka kuma ba wanda ya san tunanin Allah, sai dai Ruhun Allah. 12Ba mu karɓi ruhun duniya ba, sai dai Ruhun da yake daga Allah, domin mu fahimci abin da Allah ya ba mu hannu sake. 13Wannan shi ne abin da muke sanarwa, ba da kalmomin da muka koya ta wurin hikimar mutum ba, amma da kalmomin da Ruhu yake koyarwa, muna faɗin gaskiya ta ruhaniya da kalmomin ruhaniya. 14Mutumin da ba shi da Ruhu, ba ya yarda da abubuwan da suka fita daga Ruhun Allah, domin wauta ce a gare shi. Ba kuwa zai fahimce su ba, domin ta Ruhu ne ake fahimtarsu. 15Mutumin ruhaniya yakan gwada dukan abubuwa, amma shi kansa ba ya ƙarƙashin shari’ar mutum.

16“Wa ya taɓa sanin hankalin Ubangiji,

har da zai koya masa?”2.16 Ish 40.13

Amma muna da tunani iri na Kiristi ne.

Kiswahili Contemporary Version (Neno: Bibilia Takatifu)

1 Wakorintho 2:1-16

Kumtangaza Kristo Aliyesulubiwa

12:1 1Kor 1:17; 2:4; 13; 2Kor 10:10; 11; 1Kor 1:6Ndugu zangu nilipokuja kwenu, sikuja na maneno ya ushawishi wala hekima ya hali ya juu nilipowahubiria siri ya Mungu. 22:2 Gal 6:14; 1Kor 1:23Kwa kuwa niliamua kutokujua kitu chochote wakati nikiwa nanyi isipokuwa Yesu Kristo aliyesulubiwa. 32:3 Mdo 18:1-18; 1Kor 4:10; 9:22; 2Kor 11:29-30; 12:5-10; 13:9; 7:15Mimi nilikuja kwenu nikiwa dhaifu na mwenye hofu na kwa kutetemeka sana. 42:4 Rum 15:13; 1Kor 2:1; 1:17; 2Pet 1:16Kuhubiri kwangu na ujumbe wangu haukuwa kwa hekima na maneno ya ushawishi bali kwa madhihirisho ya nguvu za Roho 5ili imani yenu isiwe imejengwa katika hekima ya wanadamu bali katika nguvu za Mungu.

Hekima Ya Kweli Itokayo Kwa Mungu

62:6 Efe 4:13; Flp 3:15; Kol 4:12; Ebr 5:14; 6:1; Yak 1:4; 1Kor 1:20; Za 146:4Lakini miongoni mwa watu waliokomaa twanena hekima, wala si hekima ya ulimwengu huu au ya watawala wa dunia hii wanaobatilika. 72:7 Rum 16:25; Efe 3:5, 9; Kol 1:26; 2Tim 1:9Sisi tunanena hekima ya Mungu ambayo ni siri, tena iliyofichika, ambayo Mungu aliikusudia kabla ya ulimwengu kuwepo, kwa ajili ya utukufu wetu. 82:8 1Kor 1:20; Za 24:7; Mdo 7:2; Yak 2:1Hakuna hata mtawala mmoja wa nyakati hizi aliyeelewa jambo hili. Kwa maana kama wangelielewa, wasingemsulubisha Bwana wa utukufu. 92:9 Isa 64:4; 65:17Lakini ni kama ilivyoandikwa:

“Hakuna jicho limepata kuona,

wala sikio limepata kusikia,

wala hayakuingia moyoni wowote,

yale Mungu amewaandalia

wale wampendao”:

102:10 Mt 13:11; 2Kor 12:1-7; Gal 1:12; 2:2; Efe 3:3-5; Yn 14:26Lakini mambo haya Mungu ametufunulia kwa Roho wake.

Roho huchunguza kila kitu, hata mambo ya ndani sana ya Mungu. 112:11 Yer 17:9; Mit 20:27Kwa maana ni nani anayejua mawazo ya mtu isipokuwa roho iliyo ndani ya huyo mtu? Vivyo hivyo hakuna mtu ajuaye mawazo ya Mungu isipokuwa Roho wa Mungu. 122:12 Rum 8:15; 1Kor 1:20-27; Yak 2:5Basi hatukupokea roho ya dunia bali Roho atokaye kwa Mungu, ili tuweze kuelewa kile kipawa ambacho Mungu ametupatia bure. 132:13 1Kor 1:17Haya ndiyo tusemayo, si kwa maneno tuliyofundishwa kwa hekima ya wanadamu bali kwa maneno tuliyofundishwa na Roho, tukifafanua kweli za kiroho kwa maneno ya kiroho. 142:14 Yn 14:17; 1Kor 3:1Mtu ambaye hana Roho hawezi kupokea mambo yatokayo kwa Roho wa Mungu, kwa kuwa ni upuzi kwake, naye hawezi kuyaelewa kwa sababu hayo yanaeleweka tu kwa upambanuzi wa rohoni. 152:15 1Kor 3:1; Gal 6:1Mtu wa kiroho hubainisha mambo yote, lakini yeye mwenyewe habainishwi na mtu yeyote.

162:16 Isa 40:13; Rum 11:34; Yn 15:15“Kwa maana ni nani aliyefahamu mawazo ya Bwana

ili apate kumfundisha?”

Lakini sisi tunayo mawazo ya Kristo.