1 Bitrus 3 – HCB & OL

Hausa Contemporary Bible

1 Bitrus 3:1-22

Matan aure da mazan Aure

1Haka ma, ku matan aure, ku yi biyayya ga mazanku, domin in waɗansunsu ba su gaskata maganar ba, wataƙila a shawo kansu ba tare da magana ba 2sa’ad da suka ga rayuwarku mai tsabta da kuma na ladabi. 3Kyanku bai kamata yă zama na adon jiki ba, kamar kitso da sa kayan ado na zinariya da kuma sa kaya masu tsada. 4Maimakon haka, kyanku ya kamata yă zama ainihi na halinku na ciki, kyan da ba ya koɗewa na tawali’u da kuma na natsattsen ruhu, wanda yake mai daraja a gaban Allah. 5Gama haka matan masu tsarki na dā waɗanda suka sa begensu ga Allah suka yi wa kansu ado. Sun yi wa mazansu biyayya, 6kamar Saratu, wadda ta yi biyayya ga Ibrahim, har ta kira shi maigidanta. Ku ’ya’yanta ne mata in kun aikata abin da yake daidai, ba ku kuma ba tsoro dama ba.

7Mazan aure, ku ma, ku yi zaman sanin ya kamata yayinda kuke zama da matanku, ku girmama su a matsayin abokan zama marasa ƙarfi da kuma a matsayin magādan kyautar rai na alheri tare da ku, don kada wani abu yă hana addu’o’inku.

Shan wahala saboda yin ayyuka alheri

8A ƙarshe, dukanku ku zauna lafiya da juna; ku zama masu juyayi, kuna ƙaunar juna kamar ’yan’uwa, ku zama masu tausayi da kuma tawali’u. 9Kada ku rama mugunta da mugunta ko zagi da zagi, sai dai ku sa albarka, gama ga wannan ne aka kira ku, ku kuma gāji albarka. 10Gama,

“Duk wanda yake so yă ji daɗin rayuwa,

yă kuma ga kwanaki masu kyau

dole yă ƙame harshensa daga mugunta

leɓunansa kuma daga maganar yaudara.

11Dole yă juye daga mugunta, ya aikata nagarta;

dole yă nemi salama yă kuma bi ta.

12Gama idanun Ubangiji suna a kan masu adalci

kunnuwansa kuma suna jin addu’arsu,

amma fuskar Ubangiji tana gāba da masu mugunta.”3.12 Zab 34.12-16

13Wa zai yi muku lahani in kun himmantu ga yin nagarta? 14Amma ko da za ku sha wahala saboda abin da yake daidai, ku masu albarka ne. “Kada ku ji tsoron abin da suke tsoro; kada kuma ku firgita.”3.14 Ish 8.12 15Sai dai a cikin zukatanku ku keɓe Kiristi a matsayin Ubangiji. A kullum, ku kasance a shirye ku ba da amsa ga duk wanda yake neman ku ba da dalilin wannan begen da kuke da shi. Amma ku yi wannan cikin tawali’u da ladabi, 16tare da lamiri mai kyau, saboda waɗanda suke maganganun banza a kan kyawawan ayyukanku cikin Kiristi su ji kunya da irin ɓata suna da suke yi. 17Ya fi kyau, in nufin Allah ne, a sha wahala don yin nagarta fiye da yin mugunta. 18Gama Kiristi ya mutu domin zunubi sau ɗaya tak, mai adalci saboda marasa adalci, don yă kawo ku ga Allah. An kashe shi a cikin jiki, amma an rayar da shi a Ruhu, 19ta wurin wanda kuma ya tafi ya yi wa ruhohin da suke a kurkuku wa’azi 20waɗanda dā ba su yi biyayya ba sa’ad da Allah ya jira da haƙuri a kwanaki Nuhu yayinda ake sassaƙa jirgi. A cikinsa mutane kima ne kawai, su takwas, aka kuɓutar ta ruwa, 21ruwan nan kuwa kwatancin baftisma ne da yanzu ya cece ku ku ma, ba kawar da dauda daga jiki ba, sai dai yin alkawari na lamiri mai kyau ga Allah. Ya cece ku ta wurin tashin Yesu Kiristi daga matattu, 22wanda ya tafi sama, yana kuma a hannun dama na Allah, mala’iku, mulkoki da kuma masu iko suna masa biyayya.

O Livro

1 Pedro 3:1-22

Esposas e maridos

1Quanto às esposas, aceitem a autoridade dos seus maridos. Porque se alguns recusarem ouvir a palavra do Senhor, serão ganhos pelo comportamento digno das suas mulheres, ainda que sem palavras, 2considerando a vossa conduta pura e reverente.

3Não estejam preocupadas quanto à beleza exterior que consiste no arranjo dos cabelos, nas modas de vestuário ou no ouro. 4Que a vossa beleza seja sobretudo interior, feita do encanto permanente de um carácter terno e sossegado, o que é precioso diante de Deus. 5Esse era o tipo de beleza das santas mulheres que confiavam em Deus e que eram submissas aos seus maridos. 6Sara, por exemplo, sujeitava-se a Abraão, respeitando-o como chefe da casa. Se fizerem o mesmo, estão a ser verdadeiramente suas filhas, e não terão de temer nenhuma intimidação.

7Vocês, maridos, devem tratar as vossas mulheres igualmente com consideração e respeito, tendo em conta a sua condição feminina. Lembrem-se que partilharão com elas o privilégio da vida eterna. Caso contrário, as vossas orações não serão eficazes.

8Finalmente, sejam todos unânimes, tendo os mesmos sentimentos, fraternos, cheios de compaixão e de humildade. 9Não paguem o mal com o mal, nem a injúria com a injúria. Pelo contrário, peçam que Deus abençoe esses que vos ferem, pois fomos chamados a sermos bons para os outros, e Deus nos abençoará com o que nos prometeu.

10“Se alguém ama a vida

e pretende ter muitos anos para ser feliz,

então evite dizer más palavras,

e que se guarde da mentira;

11que se afaste do mal, que pratique o bem,

que procure a paz e que seja constante nesse caminho.

12Porque os olhos do Senhor estão sempre a vigiar

para proteger a vida dos que se conduzem com justiça;

os seus ouvidos estão atentos quando chamam por ele.

Mas o Senhor vira a sua cara aos que praticam o mal.”3.12 Ver Sl 34.12-16.

Fazendo o bem, ainda que sofrendo

13Que mal vos poderá ser feito, se forem zelosos na prática do bem? 14Mesmo que sofram por causa da justiça, isso tornar-vos-á felizes. Portanto não tenham medo desses tais, nem se perturbem. 15Deixem Cristo ser o Senhor exclusivo dos vossos corações. E se alguém vos perguntar a razão da vossa esperança, estejam sempre preparados para responder, 16com delicadeza e respeito. Tenham uma boa consciência. Se os homens falarem mal de vocês, virão eles próprios a ficar envergonhados por vos terem acusado falsamente, ao verificarem a vossa boa conduta em Cristo. 17Lembrem-se que, se Deus quiser que sofram, é melhor sofrer fazendo o bem do que fazendo o mal.

18Cristo também sofreu. Ele morreu uma vez pelos pecados, o justo pelos pecadores, para levar-nos a Deus. Foi morto fisicamente e tornou a viver pelo Espírito.

19E foi no Espírito que visitou e pregou aos espíritos em prisão, 20daqueles que já antes recusaram obedecer a Deus, apesar da paciência com que Deus esperava, enquanto Noé construía a arca, na qual apenas oito pessoas se salvaram da morte no dilúvio. 21Isto é uma figura do batismo que agora vos salva pelo poder da ressurreição de Jesus Cristo. Não se trata de uma lavagem física do corpo pela água, mas sim voltarmo-nos para Deus, pedindo-lhe que limpe as nossas consciências do pecado.

22Portanto, agora Cristo está sentado no céu, no lugar de honra à direita de Deus, onde todos os anjos, autoridades e poderes celestiais lhe estão sujeitos.