約翰福音 21 – CCBT & HCB

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

約翰福音 21:1-25

海邊顯現

1後來,耶穌在提比哩亞海邊又向門徒顯現。當時的情形是這樣的: 2西門·彼得、綽號「雙胞胎」的多馬加利利迦拿拿但業西庇太的兩個兒子以及其他兩個門徒都在一起。

3西門·彼得對他們說:「我要去打魚了!」

眾人說:「我們也跟你去。」於是他們就出去,上了船,但那一夜什麼也沒打到。 4天將破曉的時候,耶穌站在岸上,但門徒都不知道是耶穌。

5耶穌對他們說:「孩子們,打到魚沒有?」

他們回答說:「沒有!」

6耶穌說:「在船的右邊下網就會打到魚。」於是他們照著祂的話把網撒下去,網到的魚多到連網都拉不動。

7耶穌所愛的那個門徒對彼得說:「是主!」那時西門·彼得赤著身子,一聽見是主,立刻束上外衣,跳進海裡。 8其他門徒離岸不遠,約有一百米,他們隨後用船把那一網魚拖到岸邊。 9他們上岸後,看見有一堆炭火,上面有魚和餅。

10耶穌說:「拿幾條剛打的魚來。」 11西門·彼得就上船把網拉上岸。網裡一共有一百五十三條大魚!雖然魚這麼多,網卻沒有破。

12耶穌又說:「你們來吃早餐吧!」沒有一個門徒敢問祂是誰,他們都知道祂是主。 13耶穌就過來把餅和魚分給他們。

14這是耶穌從死裡復活後第三次向門徒顯現。

耶穌和彼得

15吃過早餐,耶穌對西門·彼得說:「約翰的兒子西門,你比這些人更愛我嗎?21·15 你比這些人更愛我嗎」或譯「你愛我比愛這些更深嗎」。

彼得說:「主啊!是的,你知道我愛你。」

耶穌對他說:「你要餵養我的小羊。」

16耶穌第二次問:「約翰的兒子西門,你愛我嗎?」

彼得說:「主啊!是的,你知道我愛你。」

耶穌說:「你要牧養我的羊。」

17耶穌第三次問:「約翰的兒子西門,你愛我嗎?」

彼得因為耶穌一連三次這樣問他,就難過起來,於是對耶穌說:「主啊!你是無所不知的,你知道我愛你。」

耶穌說:「你要餵養我的羊。 18我實實在在地告訴你,你年輕力壯的時候,自己穿上衣服,想去哪裡就去哪裡。但到你年老的時候,你將伸出手來,別人要把你綁起來帶你到你不願意去的地方。」 19這話是暗示彼得將要怎樣死來使上帝得榮耀。之後,耶穌又對他說:「你跟從我吧!」

20彼得轉身看見耶穌所愛的那個門徒跟在後面,就是吃最後的晚餐時靠在耶穌身邊問「主啊!是誰要出賣你?」的那個門徒。 21彼得問耶穌:「主啊!他將來會怎樣呢?」

22耶穌說:「如果我要他活到我再來,與你有什麼關係?你只管跟從我吧!」

23於是在信徒中間就傳說那個門徒不會死。其實耶穌並沒有說他不會死,只是說:「如果我要他活到我再來,與你有什麼關係?」

24為這些事做見證、記錄這些事的就是那個門徒,我們都知道他的見證是真實的。 25耶穌還做了許多其他的事,如果都寫成書,我想整個世界也容納不下。

Hausa Contemporary Bible

Yohanna 21:1-25

Yesu da kamun kifin banmamaki

1Daga baya Yesu ya sāke bayyana kansa ga almajiransa, a bakin Tekun Tibariya.21.1 Wato, Tekun Galili Ga yadda ya faru. 2Siman Bitrus, Toma (wanda ake kira Didaimus), Natanayel daga Kana ta Galili, ’ya’yan Zebedi maza, da kuma waɗansu almajirai guda biyu suna tare. 3Sai Siman Bitrus ya ce musu, “Za ni kamun kifi,” suka ce, “Za mu tafi tare da kai.” Saboda haka suka fita suka shiga jirgin ruwa, amma a daren nan ba su kama kome ba.

4Da sassafe, sai ga Yesu tsaye a gaci, amma almajiran ba su gane cewa Yesu ne ba.

5Sai ya ce musu, “Abokai, kuna da kifi kuwa?”

Suka amsa suka ce, “A’a.”

6Ya ce musu, “Ku jefa abin kamun kifinku dama da jirgin ruwan, za ku samu.” Da suka yi haka, sai suka kāsa jawo abin kamun kifin saboda yawan kifi.

7Sai almajirin da Yesu yake ƙauna ya ce wa Bitrus, “Ai, Ubangiji ne!” Nan da nan da Siman Bitrus ya ji ya ce, “Ai, Ubangiji ne,” sai ya yafa mayafinsa (don dā ma ya tuɓe shi), ya fāɗa cikin ruwan. 8Sauran almajiran kuwa suka bi shi cikin jirgin ruwan, janye da abin kamun kifin cike da kifi, don ba su da nisa daga gaci, wajen yadi ɗari ne. 9Da suka sauka, sai suka ga garwashin wuta a can da kifi a kai, da kuma ’yan burodi.

10Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifin da kuka kama yanzu.” 11Sai Siman Bitrus ya hau ya jawo abin kamun kifin gaci. Ya cika da manyan kifi, 153, amma duk da yawansun nan abin kamun kifin bai tsintsinke ba. 12Yesu ya ce musu, “Ku zo ku karya kumallo.” Ba wani daga cikin almajiran da ya yi karambanin tambayarsa, “Wane ne kai?” Sun san cewa Ubangiji ne. 13Yesu ya zo, ya ɗauki burodin ya ba su, haka kuma kifin. 14Wannan fa shi ne sau na uku da Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa bayan an tashe shi daga matattu.

Yesu ya sāke tabbatar da Bitrus

15Da suka gama ci, sai Yesu ya ce wa Siman Bitrus, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske fiye da waɗannan?”

Ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.”

Yesu ya ce, “Ciyar da ’ya’yan tumakina.”

16Har wa yau Yesu ya ce, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske?”

Ya amsa ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.”

Yesu ya ce, “Lura da tumakina.”

17Sau na uku ya ce masa, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata?”

Sai Bitrus ya ɓata rai saboda Yesu ya tambaye shi sau na uku, “Kana ƙaunata?” Ya ce, “Ubangiji ka san kome duka; ka san cewa, ina ƙaunarka.”

Yesu ya ce, “Ciyar da tumakina. 18Gaskiya nake faɗa maka, sa’ad da kake saurayi kakan yi wa kanka sutura ka tafi inda ka so; amma sa’ad da ka tsufa za ka miƙa hannuwanka, wani dabam yă yi maka sutura yă kai ka inda ba ka so.” 19Yesu ya faɗi wannan ne, don yă nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi yă ɗaukaka Allah. Sa’an nan ya ce masa, “Bi ni!”

20Bitrus ya juya ya ga cewa almajirin nan da Yesu yake ƙauna yana binsu. (Wannan ne ya jingina a jikin Yesu sa’ad da suke cin abincin yamman nan da ya ce, “Ubangiji wane ne zai bashe ka?”) 21Da Bitrus ya gan shi sai ya ce, “Ubangiji, wannan fa?”

22Yesu ya amsa ya ce, “Idan na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki? Kai dai bi ni.” 23Saboda wannan, jita-jita ta bazu a cikin ’yan’uwa cewa wannan almajirin ba zai mutu ba. Amma fa Yesu bai ce ba zai mutu ba; shi dai ya ce, “In na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki?”

24Wannan shi ne almajirin da ya ba da shaida a kan waɗannan abubuwa ya kuma rubuta su. Mun san cewa shaidarsa gaskiya ce.

25Yesu ya yi waɗansu abubuwa da yawa kuma. Da a ce an rubuta kowannensu, na tabbata ko duniya duka ba za tă sami wuri saboda littattafan da za a rubuta ba.