彼得前書 1 – CCBT & HCB

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

彼得前書 1:1-25

1我是耶穌基督的使徒彼得,寫信給蒙上帝揀選,寄居在本都加拉太加帕多迦亞細亞庇推尼各地的人。 2你們蒙揀選是按照父上帝預先定好的旨意,藉著聖靈得以聖潔,好順服耶穌基督,並靠祂的血得到潔淨。

願上帝賜給你們豐豐富富的恩典和平安!

活潑的盼望

3願頌讚歸於我們主耶穌基督的父上帝!祂有無窮的憐憫,藉著耶穌基督從死裡復活使我們獲得重生,有活潑的盼望, 4可以承受那不會朽壞、沒有污點、不會衰殘、為你們存留在天上的產業。 5你們這些因信而蒙上帝用大能保守的人,必能得到那已經預備好、在末世要顯明的救恩。

6為此,即使現今你們必須暫時在百般試煉中忍受痛苦,也要滿懷喜樂。 7這樣,你們的信心經過試驗便顯明是真實的,比那經過火煉仍會壞掉的金子更加寶貴,使你們可以在耶穌基督顯現時得到稱讚、榮耀和尊貴。 8你們雖然沒有見過基督,卻愛祂;雖然現在看不見祂,卻信祂,並且有無法形容、充滿榮耀的喜樂。 9因為你們得到了信心帶來的果效,就是你們的靈魂得救。

10有關這救恩,那些預言恩典要臨到你們的眾先知早已詳細尋求查考了。 11基督的靈曾在他們心中指示他們,預言基督要受苦,然後得榮耀。他們便詳細查考這些事會在什麼時候、什麼情況下發生。 12他們得到啟示,知道他們傳講這些事不是為了自己,而是為了你們。現在,那些靠著從天上差來的聖靈向你們傳福音的人,已經將這些事傳給你們了。連天使也想把這些事看個明白。

要聖潔像主

13所以,要預備好你們的心,謹慎自律,專心盼望耶穌基督顯現時要帶給你們的恩典。 14你們既是順服的兒女,就不要再像從前無知的時候那樣放縱私慾。 15那呼召你們的是聖潔的,你們在一切事上也要聖潔。 16因為聖經上說:「你們要聖潔,因為我是聖潔的。」

17既然你們稱呼那位按各人的行為公正無私地審判人的上帝為父,就應該存著敬畏的心過你們在世上寄居的日子。 18要知道,你們從傳統的、沒有意義的生活中被救贖出來,不是靠金銀等會朽壞的東西, 19而是靠無瑕無疵的代罪羔羊——基督的寶血。 20基督是上帝在創世以前預先揀選的,卻在這末世為你們顯現。 21你們藉著基督信了使祂從死裡復活、賜祂榮耀的上帝,所以,你們的信心和盼望都在於上帝。

22你們既因順服真理,潔淨了自己的心,能夠真誠地愛弟兄姊妹,就當以清潔的心彼此切實相愛。 23你們獲得重生,不是藉著會腐爛的種子,而是藉著不會腐爛的種子——上帝活潑永存的道。 24因為

「芸芸眾生盡如草,

榮華不過草上花;

草必枯乾花必殘,

25唯有主道永長存。」

這道就是傳給你們的福音。

Hausa Contemporary Bible

1 Bitrus 1:1-25

1Bitrus, manzon Yesu Kiristi,

Zuwa ga zaɓaɓɓu na Allah, baƙi a duniya, da suke a warwatse ko’ina a Fontus, Galatiya, Kaffadokiya, Asiya da kuma Bitiniya, 2waɗanda aka zaɓa bisa ga rigyasanin Allah Uba, ta wurin aikin tsarkakewar Ruhu, don biyayya ga Yesu Kiristi, su kuma sami yayyafan jininsa.

Alheri da salama su zama naku a yalwace.

Yabo ga Allah domin bege mai rai

3Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi! Cikin jinƙansa mai girma ya ba mu sabuwar haihuwa cikin bege mai rai ta wurin tashin Yesu Kiristi daga matattu, 4da kuma cikin gādon da ba zai taɓa lalacewa, ɓacewa ko koɗewa ba, ajiyayye a sama dominku, 5ku waɗanda ta wurin bangaskiya ake kiyayewa ta wurin ikon Allah har yă zuwa ceton da yake a shirye da za a bayyana a ƙarshen lokaci. 6A kan wannan kuke cike da farin ciki ƙwarai, ko da yake yanzu na ɗan lokaci kuna fuskantar baƙin ciki daga gwaje-gwaje iri-iri. 7Wannan kuwa domin a tabbatar da sahihancin bangaskiyarku ne, wadda ta fi zinariya daraja nesa, ita zinariya kuwa, ko da yake mai ƙarewa ce, akan gwada ta da wuta, domin bangaskiyan nan taku ta jawo muku yabo da girma da ɗaukaka a bayyanar Yesu Kiristi. 8Ko da yake ba ku taɓa ganinsa ba, kuna ƙaunarsa; kuma ko da yake ba kwa ganinsa yanzu, kun gaskata shi, kun kuma cika da farin ciki ƙwarai, wanda ya fi gaban faɗi, 9gama kuna samun sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku ke nan.

10Game da ceton nan, annabawa, waɗanda suka yi maganar alherin da za tă zo gare ku, sun yi bincike mai zurfi, a natse, 11suna ƙoƙari su san lokaci da kuma yanayin da Ruhun Kiristi da yake cikinsu yana nunawa sa’ad da ya yi faɗi a kan wahalolin Kiristi da kuma ɗaukaka da za tă bi. 12Aka bayyana musu cewa ba kansu ne suke bauta wa ba sai ku, sa’ad da suka yi maganar abubuwan da aka faɗa muku ta wurin waɗanda suka yi muku wa’azin bishara, ta wurin Ruhu Mai Tsarki wanda aka aika daga sama. Ko mala’iku ma suna marmari su ga waɗannan abubuwa.

Ku zama masu tsarki

13Saboda haka, ku shirya kanku don aiki; ku zama masu kamunkai; ku kafa begenku duka a kan alherin da za a ba ku sa’ad da aka bayyana Yesu Kiristi. 14Kamar ’ya’ya masu biyayya, kada ku bi mugayen sha’awace-sha’awacen da dā kuke da su sa’ad da kuke rayuwa a cikin jahilci. 15Amma kamar yadda wanda ya kira ku yake mai tsarki, haka ku ma sai ku kasance masu tsarki cikin dukan abubuwan da kuke yi; 16gama a rubuce yake cewa, “Ku zama masu tsarki, domin ni mai tsarki ne.”1.16 Fir 11.44,45; Fir 19.2; Fir 20.7

17Tun da yake kuna kira ga Uba wanda yake yin wa kowane mutum shari’a bisa ga ayyukansa ba bambanci, sai ku yi rayuwarku a nan kamar baƙi cikin tsoro mai bangirma. 18Gama kun san cewa ba da abubuwa masu lalacewa kamar azurfa ko zinariya ce aka fanshe ku daga rayuwar banza da kuka karɓa daga kakanni-kakanninku ba, 19sai dai an fanshe ku da jini mai daraja na Kiristi, ɗan rago marar aibi ko lahani. 20An zaɓe shi kafin halittar duniya, amma an bayyana shi a zamanin ƙarshe saboda ku. 21Ta gare shi ne kuka gaskata da Allah, wanda ya tā da shi daga matattu, aka kuma ɗaukaka shi, ta haka bari bangaskiyarku da begenku su kasance ga Allah.

22Yanzu da kuka tsarkake kanku ta wurin yin biyayya ga gaskiyan nan, don ku kasance da ƙauna mai gaskiya wa ’yan’uwanku, sai ku ƙaunaci juna ƙwarai, daga zuciya. 23Gama an sāke haihuwarku, ba da iri da yake lalacewa ba, sai dai marar lalacewa, ta wurin rayayyiya da kuma madawwamiyar maganar Allah. 24Gama,

“Dukan mutane kamar ciyawa suke,

darajarsu kuma kamar furannin jeji ne;

ciyawa takan yanƙwane furannin kuma su kakkaɓe,

25amma maganar Ubangiji tana nan har abada.”1.25 Ish 40.6-8

Wannan kuwa ita ce kalmar da aka yi muku wa’azi.