帖撒羅尼迦前書 4 – CCBT & HCB

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

帖撒羅尼迦前書 4:1-18

上帝喜悅的生活

1最後,弟兄姊妹,既然你們領受了我們的教導,知道怎樣行才能討上帝的喜悅,如你們現在所行的,我們靠著主耶穌懇求、勸勉你們要更加努力。 2你們都知道我們靠著主耶穌傳給你們的誡命。 3上帝的旨意是要你們聖潔,遠避淫亂的事, 4要你們人人都知道持守身體的聖潔和尊貴, 5不可荒淫縱慾,像那些不認識上帝的外族人一樣。 6你們在這種事上不可越軌,虧負弟兄姊妹。我們曾經對你們說過,並且鄭重地警告過你們,主必懲治犯這種罪的人。 7因為上帝呼召我們不是要我們沾染污穢,而是要我們聖潔。 8所以,人若拒絕遵行這命令,他不是拒絕人,而是拒絕賜聖靈給你們的上帝。

9關於弟兄姊妹彼此相愛的事,我就不必多寫了,因為你們自己從上帝那裡領受了要彼此相愛的教導。 10你們對馬其頓全境的弟兄姊妹已經做到了這一點。不過,我勸各位要再接再厲。 11你們要立志過安分守己的生活,親手做工,正如我們以前吩咐你們的。 12這樣,你們可以得到外人的尊敬,不必依賴任何人。

復活的盼望

13弟兄姊妹,關於安息的信徒4·13 安息的信徒」希臘文是「睡了的人」,聖經常用「睡了」作為「死了」的委婉說法,參見約翰福音十一章11—14節。,我不願意你們一無所知,免得你們像那些沒有盼望的人一樣悲傷。 14我們既然相信耶穌死了,又復活了,也要相信上帝必把那些安息的信徒和耶穌一同帶來。

15我們把主耶穌的話告訴你們:主再來的那天,我們還活著的人不會比已安息的信徒先見到主。 16因為主必在號令聲、天使長的呼喊聲和上帝的號角聲中親自從天降臨,已經離世的基督徒必先復活。 17然後,我們還活著的人要和他們一起被提到雲裡,在空中與主相會,永遠和主在一起。 18所以你們要用這些話彼此鼓勵。

Hausa Contemporary Bible

1 Tessalonikawa 4:1-18

Rayuwa don a gamshi Allah

1A ƙarshe, ’yan’uwa, mun umarce ku yadda za ku yi rayuwa domin ku gamshi Allah, kamar yadda kuke yi. Yanzu muna roƙonku muna kuma gargaɗe ku a cikin Ubangiji Yesu ku yi haka sau da sau. 2Gama kun san umarnan da muka ba ku ta wurin ikon Ubangiji Yesu.

3Nufin Allah ne a tsarkake ku, cewa ku guje wa fasikanci; 4don kowannenku yă koya yadda zai ƙame kansa a hanyar da take mai tsarki, mai mutunci kuma, 5ba cikin muguwar sha’awa kamar ta marasa bangaskiya, waɗanda ba su san Allah ba; 6cikin wannan al’amari kuwa kada wani yă yi wa ɗan’uwansa laifi ko yă cuce shi. Ubangiji zai hukunta mutane saboda dukan irin waɗannan zunubai, kamar yadda muka riga muka gaya muku, muka kuma yi muku gargaɗi. 7Gama Allah bai kira mu ga zaman marasa tsarki ba, sai dai ga zaman tsarki. 8Saboda haka, duk wanda ya ƙi wannan umarni ba mutum ne ya ƙi ba sai ko Allah, wanda ya ba ku Ruhunsa Mai Tsarki.

9Yanzu kuwa game da ƙaunar ’yan’uwa, ba ma bukata mu rubuta muku, gama ku kanku Allah ya riga ya koya muku ku ƙaunaci juna. 10Gaskiyar kuwa ita ce, kuna ƙaunar dukan ’yan’uwa ko’ina a Makidoniya. Duk da haka muna ƙara gargaɗe ku, ’yan’uwa, ku yi haka sau da sau. 11Ku mai da wannan burinku na yi natsattsiyar rayuwa, kuna mai da hankali ga sha’anin da yake gabanku, kuna kuma yin aiki da hannuwanku, kamar dai yadda muka gaya muku, 12don rayuwanku ta kullum ta zama da mutunci ga waɗanda suke na waje don kuma kada ku dogara a kan kowa.

Zuwan Ubangiji

13’Yan’uwa, ba ma so ku kasance cikin jahilci game da waɗanda suka yi barci, ko kuwa ku yi baƙin ciki kamar sauran mutanen da ba su da bege. 14Mun gaskata cewa Yesu ya mutu ya tashi kuma daga matattu, ta haka muka gaskata cewa Allah zai kawo waɗanda suka yi barci a cikinsa tare da Yesu. 15Bisa ga maganar Ubangiji kansa, muna gaya muku cewa mu da muke raye har yanzu, waɗanda aka bari har dawowar Ubangiji, tabbatacce ba za mu riga waɗanda suka yi barci tashi ba. 16Gama Ubangiji kansa zai sauko daga sama, da umarni mai ƙarfi, da muryar babban mala’ika da kuma busar ƙahon Allah, waɗanda suka mutu kuwa cikin Kiristi za su tashi da farko. 17Bayan haka, mu da muke da rai da aka bari, za a ɗauke mu tare da su a cikin gizagizai don mu sadu da Ubangiji a sararin sama. Ta haka za mu kasance tare da Ubangiji har abada. 18Saboda haka ku ƙarfafa juna da waɗannan kalmomi.