啟示錄 22 – CCBT & HCB

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

啟示錄 22:1-21

1天使讓我看城內街道當中一道流淌著生命水的河,清澈如水晶,從上帝和羔羊的寶座那裡流出。 2河兩岸有結十二種果子的生命樹,每個月都結果子,葉子能醫治萬民。 3再也沒有咒詛,因為城裡有上帝和羔羊的寶座,祂的奴僕都要事奉祂。 4他們必見上帝的面,上帝的名字必印在他們的額上。 5再沒有黑夜,也不需要燈光和陽光,因為主上帝必作他們的光。他們要執掌王權直到永永遠遠。

基督的再來

6天使對我說:「這些話真實可靠。賜聖靈感動眾先知的主上帝已差遣祂的天使,將那些快要發生的事指示給祂的奴僕們。」

7「看啊,我快要來了。遵行這書中預言的人有福了!」

8以上都是我約翰親眼看見、親耳聽見的事。當我聽見、看見這些事後,就俯伏敬拜將這一切指示給我的天使。 9天使對我說:「千萬不可!我與你、你的眾先知弟兄和那些遵行這書上話語的人同是上帝的奴僕,你要敬拜上帝。」

10他又對我說:「不可封住這卷書上的預言,因為時候快到了。 11不義的,讓他繼續不義;污穢的,讓他繼續污穢;公義的,讓他保持公義;聖潔的,讓他保持聖潔。」

12「看啊,我快要來了,到時候我要按各人的行為施行賞罰。 13我是阿拉法,我是俄梅加;我是首先的,我是末後的;我是開始,我是終結。 14那些洗淨自己衣裳的人有福了!他們有權吃生命樹的果子,也可以從城門進入城中。 15那些如同惡犬的敗類、行邪術的、淫亂的、殺人的、拜偶像的和一切喜歡弄虛作假的,都要被拒之城外。 16我耶穌差遣我的天使到眾教會,向你們證明這些事。我是大衛的根,也是大衛的後裔,又是明亮的晨星。」

17聖靈和新娘都說:「來吧!」聽見的也要說:「來吧!」口渴的,讓他來吧!願意的,讓他白白享用生命水吧!

警告

18我鄭重警告所有聽見這書上預言的人:如果誰在這書上增添什麼,上帝必將這書上所記載的災禍加在他身上; 19如果有人從這預言書上刪減什麼,上帝必使他無份於這書上所記載的生命樹和聖城。

20那位證明這些事的說:「是的,我快要來了。」阿們!主耶穌啊,我願你來!

21願主耶穌的恩典與眾聖徒同在。阿們!

Hausa Contemporary Bible

Ruʼuya ta Yohanna 22:1-21

An maido da Eden

1Sai mala’ikan ya nuna mini kogin ruwan rai, mai ƙyalli kamar madubi, yana gangarawa daga kursiyin Allah da na Ɗan Ragon, 2yana bin tsakiyar babban titi na birnin. A kowane gefen kogin akwai itacen rai mai ba da ’ya’ya goma sha biyu, yana ba da ’ya’yansa kowane wata. Ganyayen itacen kuwa saboda warkar da al’ummai ne. 3Ba za a ƙara samun la’ana ba. Kursiyin Allah da na Ɗan Ragon zai kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa hidima. 4Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu. 5Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin.

Yohanna da Mala’ikan

6Mala’ikan ya ce mini, “Waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa, ya aiki mala’ikansa, don yă nuna wa bayinsa abubuwan da za su faru nan ba da daɗewa ba.”

7“Ga shi! Ina zuwa da wuri! Mai albarka ne wanda yake kiyaye kalmomin annabcin da suke cikin wannan littafi.”

8Ni, Yohanna, na ji, na kuma ga abubuwan nan. Kuma sa’ad da na ji, na kuma gan su, sai na fāɗi a ƙasa a gaban mala’ikan da yake nuna mini su, don in yi sujada. 9Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da ’yan’uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye kalmomin wannan littafi. Allah za ka yi wa sujada!”

10Sa’an nan ya gaya mini cewa, “Kada ka rufe kalmomin annabcin littafin nan, domin lokaci ya yi kusa. 11Duk mai yin laifi yă ci gaba da yin laifi; duk mai aikata ƙazanta yă ci gaba da aikata ƙazanta. Duk mai aikata abin da yake daidai, yă ci gaba da aikata abin da yake daidai. Kuma duk wanda yake mai tsarki, yă ci gaba da yin abin da yake da tsarki.”

Maganar ƙarshe. Gayyata da gargaɗi

12“Ga shi, ina zuwa da wuri! Ladan da zan bayar yana tare da ni, kuma zan ba wa kowa gwargwadon abin da ya yi. 13Ni ne Alfa da kuma Omega, na Fari da kuma na Baya, Farko da kuma Ƙarshe.

14“Masu albarka ne waɗanda suka wanke tufafinsu, don su sami izinin ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta ƙofofi. 15Waɗanda suke waje kuwa karnuka ne, masu sihiri, masu fasikanci, masu kisankai, masu bautar gumaka, da duk wanda yake ƙaunar ƙarya yake kuma aikata ta.

16“Ni, Yesu, na aiko mala’ikana ya ba ka wannan shaida saboda ikkilisiyoyi. Ni ne Tushe da kuma Zuriyar Dawuda, da kuma Tauraron Asubahi mai haske.”

17Ruhu da kuma amarya suna cewa, “Zo!” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo!” Duk mai jin ƙishirwa, yă zo; duk mai bukata kuma, yă ɗibi ruwan rai kyauta.

18Ina yin wa duk wanda ya ji kalmomin annabcin wannan littafi gargaɗi. Duk wanda ya ƙara wani abu a kansu, Allah zai ƙara masa annoban da aka bayyana a littafin nan. 19Duk wanda kuma ya yi ragi a kalmomi daga littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai da kuma na birnin nan mai tsarki, waɗanda aka bayyana a littafin nan.

20Shi da ya shaida waɗannan abubuwa ya ce, “I, ina zuwa da wuri.”

Amin. Zo, Ubangiji Yesu!

21Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da mutanen Allah. Amin.