哥林多後書 2 – CCBT & HCB

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

哥林多後書 2:1-17

愛之深責之切

1我已經決定了,下次到你們那裡時不再使大家憂傷。 2如果我使你們憂傷,那麼除了因我而憂傷的你們,還有誰能使我喜樂呢? 3我曾為這事寫信給你們,免得我到你們那裡時,那些本該使我喜樂的人反而使我憂傷。我也深信你們會以我的喜樂為你們的喜樂。 4我萬分難過、淚流滿面地給你們寫了前一封信,並非要使你們憂傷,而是要你們明白我是多麼疼愛你們。

要饒恕犯罪的人

5那個令人痛心的人與其說使我憂傷,倒不如說使你們大家都有幾分憂傷。我只說幾分憂傷,是怕說得太重,他受不了。 6這樣的人受了眾人的譴責也就夠了。 7你們現在要饒恕他、安慰他,免得他憂傷過度而一蹶不振。 8我勸你們要讓他確實知道你們仍然愛他。 9為此,我也曾寫信給你們,想知道你們是否凡事順服。 10你們饒恕誰,我也饒恕誰。我若饒恕,是為了你們的緣故在基督面前饒恕的, 11免得撒旦乘虛而入,因為我們並非不知道牠的詭計。

基督的香氣

12我前往特羅亞傳揚基督的福音時,主為我打開了傳福音的大門。 13那時,因為沒有找到提多弟兄,我心裡不安,便辭別眾人來到馬其頓

14感謝上帝!祂常常在基督裡率領我們走在凱旋的行列中,又藉著我們到處散發那因認識基督而有的香氣。 15不論是在得救的人當中還是在滅亡的人當中,對上帝來說,我們都是基督的馨香之氣。 16對滅亡的人而言,這香氣是叫人死亡的香氣;對得救的人來說,這香氣卻是叫人得生命的香氣。誰能擔當這樣的重任呢? 17我們並不像許多人為了謀利而出賣上帝的道。我們是上帝差遣的,在上帝面前靠著基督誠誠實實地講道。

Hausa Contemporary Bible

2 Korintiyawa 2:1-17

1Saboda haka na yanke shawara ba zan sāke kawo muku ziyara ta ɓacin rai ba. 2Gama in na sa ku baƙin ciki, wa ya rage yă faranta mini zuciya, in ba ku waɗanda na sa baƙin cikin ba? 3Na rubuta yadda na yi ne saboda sa’ad da na iso kada waɗanda ya kamata su faranta mini rai, su sa ni baƙin ciki. Na amince da ku duka a kan farin cikina naku ne ku duka. 4Gama na rubuta muku ne cikin baƙin ciki mai yawa da ɓacin zuciya har ma da hawaye mai yawa, ba don in sa ku baƙin ciki ba ne, a’a, sai dai domin in nuna muku zurfin ƙaunar da nake yi muku.

Gafara don mai zunubi

5In wani ya jawo baƙin ciki, ba ni kaɗai ya jawo wa ba, amma a wani fanni, sai in ce dukanku ne ya jawo wa, ba na faɗa haka don in matsa muku lamba ba ne. 6Irin wannan mutum, horon da yawancin mutane suka yi masa ya isa haka. 7Yanzu fa, a maimako, gara ku yafe masa, ku kuma ta’azantar da shi, don kada baƙin ciki mai yawa yă sha kansa. 8Saboda haka, ina roƙonku, ku sāke nuna masa ƙaunarku. 9Abin da ya sa na rubuta muku shi ne don in ga ko za ku jimre da gwajin nan, kuna kuma yin biyayya ta kowace hanya. 10In kuka gafarta wa wani, ni ma na gafarta masa. Abin da na gafarta kuwa, in har ma da abin gafartawa, saboda ku ne na gafarta masa, albarkacin Kiristi, 11don kada Shaiɗan yă rinjaye mu. Da yake muna sane da dabarunsa.

Masu hidimar sabon alkawari

12To, sa’ad da na tafi Toruwas don in yi wa’azin bisharar Kiristi, ko da yake na tarar cewa Ubangiji ya buɗe mini ƙofa, 13duk da haka, ban sami salama a zuciyata ba domin ban sami ɗan’uwana Titus a can ba. Sai na yi bankwana da su na wuce zuwa Makidoniya.

14Amma godiya ga Allah, wanda kullum yake bi da mu da nasara cikin Kiristi, kuma ta wurinmu, yana baza ƙanshin nan na sanin Kiristi a ko’ina. 15Don kuwa, a wurin Allah mu ƙanshin Kiristi ne cikin waɗanda ake ceto, da kuma waɗanda suke hanyar hallaka. 16Ga wani, mu warin mutuwa ne, amma ga wani kuwa, mu ƙanshin rai ne. Wa ya isa yă yi irin wannan aikin? 17Ba ma tallar maganar Allah don riba yadda waɗansu mutane da yawa suke yi. A maimakon haka, muna magana cikin Kiristi a gaban Allah da gaskiya, kamar mutanen da aka aika daga Allah.