马太福音 2 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

马太福音 2:1-23

智者来朝拜

1希律王执政期间,耶稣降生在犹太伯利恒城。

当时有几位智者2:1 智者”或译“占星家”下同7节和16节。从东方来到耶路撒冷2问道:“那生来做犹太人之王的在哪里呢?我们在东方看见祂的星,特来朝拜祂。”

3希律王听后,心里不安,全城的人都感到不安。 4希律王就召来祭司长和律法教师,问他们:“基督在哪里降生呢?”

5他们回答说:“在犹太伯利恒,因为先知这样记载,

6“‘犹大地区的伯利恒啊!

你在犹大各城中并不是最小的,

因为有一位君王要从你那里出来,

牧养我的以色列子民。’”

7于是,希律暗中召见那几位智者,仔细查问那星出现的准确时间, 8然后派他们去伯利恒,并吩咐道:“你们去仔细寻访那个小孩,找到了,就回来报信,我也好去朝拜祂。”

9他们听了王的吩咐,就去了。忽然,那颗曾在东方出现的星又出现在他们前面,引领他们来到小孩耶稣所在的地方,便停下来。 10他们看见那颗星,喜出望外。

11他们进了屋子,看见孩子和祂母亲玛丽亚,就俯伏在地上拜祂,并打开盛宝物的盒子献上黄金、乳香和没药作礼物。 12他们在梦中得到指示不可回希律那里,便改道返回了家乡。

逃往埃及

13他们离开之后,主的天使在梦中向约瑟显现,说:“起来,带着小孩子和祂母亲逃往埃及,住在那里等候我的通知,因为希律要寻找这孩子,杀害祂。” 14于是,约瑟起来带着孩子和祂母亲连夜逃往埃及15并在那里一直住到希律死了。这就应验了主借着先知所说的话:“我把儿子从埃及召出来。”

16希律见自己被智者愚弄,大为恼怒,便照着智者所说的时间推算,下令把伯利恒附近两岁以下的男孩杀光。 17这正应验了耶利米先知的话:

18“在拉玛有痛哭哀号的声音,

拉结在为儿女哀痛,

不肯接受安慰,

因为他们都死了!”

定居拿撒勒

19希律死后,主的天使在梦中向在埃及约瑟显现,说: 20“起来,带着孩子和祂母亲回以色列去吧!因为要杀害孩子的人已经死了。” 21约瑟就起来,带着孩子和祂母亲返回以色列

22约瑟听闻亚基劳继承父亲希律的王位统治犹太,就不敢回犹太。这时,他在梦中得到主的指示,便前往加利利地区, 23定居在拿撒勒镇。这应验了先知的话:“祂将被称为拿撒勒人。”

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 2:1-23

Ziyarar Masana

1Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana,2.1 A al’adance Masu Hikima daga gabas suka zo Urushalima 2suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas2.2 Ko kuwa a tauraro sa’ad da ya taso mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”

3Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima. 4Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi. 5Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.

6“ ‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda,

ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba,

gama daga cikinki mai mulki zai zo,

wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’2.6 Mik 5.2

7Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana. 8Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”

9Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake. 10Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai. 11Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur. 12Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.

Tserewa zuwa Masar

13Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”

14Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar, 15inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”2.15 Hos 11.1

16Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan ’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan. 17Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,

18“An ji murya a Rama,

tana kuka da makoki mai tsanani,

Rahila ce take kuka domin ’ya’yanta,

an kāsa ta’azantar da ita,

don ba su.”2.18 Irm 31.15

Komowa zuwa Nazaret

19Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar, 20ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”

21Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila. 22Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili, 23ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”