马太福音 19 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

马太福音 19:1-30

论休妻

1耶稣说完这番话,就离开加利利来到约旦河对岸的犹太地区。 2有一大群人跟着祂,祂就在那里医好了他们的病。

3有几个法利赛人到耶稣那里想试探祂,便问祂:“丈夫可以用任何理由休妻吗?”

4耶稣回答说:“你们没有读过吗?太初,造物主造了男人和女人,并且说, 5‘因此,人要离开父母,与妻子结合,二人成为一体。’ 6这样,夫妻不再是两个人,而是一体了。因此,上帝配合的,人不可分开。”

7他们追问:“那么,为什么摩西说,只要给妻子休书,就可以休她呢?”

8耶稣说:“因为摩西知道你们铁石心肠,所以才准你们休妻。但起初并不是这样。 9我告诉你们,除非是妻子不贞,否则,任何人休妻另娶,就是犯通奸罪19:9 有古卷在此处有“娶被休女子的人也犯了通奸罪”。。”

10门徒对耶稣说:“如果夫妻关系是这样,还不如不结婚。”

11耶稣说:“这话不是每个人都能接受的,只有那些得到这种恩赐的人才能接受。 12人不结婚的原因很多,有些是因为先天的缺陷,有些是被人阉了,也有些是为了天国而自己放弃结婚的权利。谁能接受,就让他接受吧。”

耶稣为小孩子祝福

13有人带着小孩子来见耶稣,请求耶稣为他们按手祷告,却受到门徒的责备。

14耶稣说:“让小孩子到我这里来,不要阻止他们,因为天国属于这样的人。” 15于是祂为他们按手祷告,然后才离开那里。

有钱的青年

16有一个人来请教耶稣:“老师,我该做什么善事才能获得永生呢?”

17耶稣说:“你为什么问我做什么善事?只有上帝是善的,你要得永生,就必须遵守祂的诫命。”

18那人问:“什么诫命呢?”

耶稣答道:“不可杀人,不可通奸,不可偷盗,不可作伪证, 19要孝敬父母,并且爱邻如己。”

20那青年说:“这些我早已遵守了,还缺什么呢?”

21耶稣告诉他:“如果你想做到纯全,就去变卖所有的产业,送给穷人,你就必有财宝存在天上,然后你来跟从我。” 22那青年听后,便忧伤地走了,因为他有许多产业。

23事后,耶稣对门徒说:“我实在告诉你们,有钱人进天国很困难。 24我再告诉你们,骆驼穿过针眼比有钱人进上帝的国还容易呢!”

25门徒听了,惊奇地问:“这样,谁能得救呢?”

26耶稣看着他们说:“对人而言,这不可能;但对上帝而言,凡事都可能。”

27彼得问道:“你看,我们已经撇下一切来跟从你了,将来会有什么奖赏呢?”

28耶稣说:“我实在告诉你们,到万物更新、人子坐在祂荣耀的宝座上时,你们这些跟从我的人也要坐在十二个宝座上,审判以色列的十二个支派。 29无论谁为我的名而撇下房屋、弟兄、姊妹、父母、儿女或田地,都要得到百倍的赏赐,而且承受永生。 30然而,许多为首的将要殿后,殿后的将要为首。”

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 19:1-30

Kashen aure

(Markus 10.1-12)

1Sa’ad da Yesu ya gama faɗin waɗannan abubuwa, sai ya bar Galili, ya tafi yankin Yahudiya a ɗaya gefen Urdun. 2Taron mutane mai yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da su a can.

3Waɗansu Farisiyawa suka zo wurinsa don su gwada shi. Suka yi tambaya suka ce, “Daidai ne mutum yă saki matarsa saboda wani dalili da kuma a kan kowane dalili?”

4Ya amsa ya ce, “Ba ku taɓa karantawa ba ne cewa, a farkon halitta, Mahalicci ‘ya yi su namiji da ta mace,’19.4 Far 1.27 5ya kuma ce, ‘Saboda wannan dalili, namiji zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa yă manne wa matarsa, biyun kuwa su zama jiki guda’?19.5 Far 2.24 6Ta haka, ba sa ƙara zama biyu, sai dai ɗaya. Saboda haka abin da Allah ya haɗa fa, kada mutum yă raba.”

7Suka yi tambaya, suka ce, “To, me ya sa Musa ya umarta cewa mutum yă ba wa matarsa takardar saki, yă kuma kore ta?”

8Yesu ya amsa ya ce, “Musa ya ba ku izini ku saki matanku saboda taurin zuciyarku ne. Amma ba haka yake ba daga farko. 9Ina faɗa muku cewa duk wanda ya saki matarsa, sai dai a kan rashin aminci a cikin aure, ya kuwa auri wata, ya yi zina ke nan.”

10Almajiran suka ce masa, “In haka yake tsakanin miji da mata, ashe, ya ma fi kyau kada a yi aure.”

11Yesu ya ce, “Ba kowa ba ne zai yarda da wannan magana, sai dai waɗanda aka yarda musu. 12Gama waɗansu bābānni ne domin haka aka haife su; waɗansu kuwa mutane ne suka mai da su haka; waɗansu kuma sun ƙi aure ne saboda mulkin sama. Duk mai iya ɗaukar wannan yă ɗauka.”

Yesu da ƙananan yara

(Markus 10.13-16; Luka 18.15-17)

13Sa’an nan aka kawo yara ƙanana wurin Yesu don yă ɗibiya musu hannuwansa, yă kuma yi musu addu’a. Amma almajirai suka tsawata wa waɗanda suka kawo su.

14Yesu ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin sama na irin waɗannan ne.” 15Sa’ad da ya ɗibiya musu hannuwansa, sai ya tafi abinsa.

Saurayi mai arziki

(Markus 10.17-31; Luka 18.18-30)

16To, fa, sai ga wani ya zo wurin Yesu ya tambaye shi ya ce, “Malam, wane abu mai kyau ne ya zama mini dole in yi don in sami rai madawwami?”

17Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake tambayata game da abin da yake mai kyau? Akwai Mai kyau Ɗaya kaɗai. In kana so ka sami rai madawwami, ka kiyaye dokokin nan.”

18Mutumin ya yi tambaya ya ce, “Waɗanne?”

Yesu ya amsa ya ce, “ ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar ƙarya, 19ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’19.19 Fit 20.12-16; M Sh 5.16-20 ka kuma ‘ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’19.19 Fir 19.18

20Saurayin ya ce, “Duk waɗannan na kiyaye. Me kuma ya rage mini?”

21Yesu ya amsa ya ce, “In kana so ka zama cikakke, ka je, ka sayar da dukan dukiyarka ka kuma ba matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo, ka bi ni.”

22Da saurayin ya ji haka, sai ya tafi rai a ɓace, don yana da arziki sosai.

23Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Gaskiya nake gaya muku, yana da wuya mai arziki yă shiga mulkin sama. 24Har wa yau ina gaya muku, zai fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”

25Sa’ad da almajiran suka ji wannan, sai suka yi mamaki ƙwarai. Suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai sami ceto ke nan?”

26Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba ya yiwuwa, amma ga Allah kuwa, dukan abubuwa masu yiwuwa ne.”

27Sai Bitrus ya amsa masa, “Ga shi mun bar kome don mu bi ka! Me za mu samu ke nan?”

28Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, a lokacin sabunta dukan kome, sa’ad da Ɗan Mutum ya zauna a kan kursiyinsa mai daraja, ku da kuka bi ni, ku ma za ku zauna a kan kursiyoyi goma sha biyu, kuna yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a. 29Duk kuma wanda ya bar gidaje ko ’yan’uwa maza ko ’yan’uwa mata ko mahaifi ko mahaifiya ko yara ko gonaki, saboda ni, zai sami abin da ya fi haka riɓi ɗari, yă kuma gāji rai madawwami. 30Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, da yawa kuma da suke na ƙarshe, za su zama na farko.