马可福音 7 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

马可福音 7:1-37

传统与诫命

1有法利赛人和一些律法教师从耶路撒冷来见耶稣。 2他们看到祂的门徒有些吃饭前没有照礼仪洗手。 3因为法利赛人和所有的犹太人都拘守祖先的传统,总是先照礼仪洗手之后才吃饭; 4从市场回来也要先洁净自己,然后才吃饭。他们还拘守许多其他规矩,如洗杯、罐、铜器等。

5他们质问耶稣:“为什么你的门徒违背祖先的传统,竟用不洁净的手吃饭呢?”

6耶稣回答说:“以赛亚先知针对你们这些伪君子所说的预言一点不错,正如圣经上说,

“‘这些人嘴上尊崇我,

心却远离我。

7他们的教导无非是人的规条,

他们敬拜我也是枉然。’

8你们只知拘守人的传统,却无视上帝的诫命。” 9耶稣又对他们说:“你们为了拘守自己的传统,竟巧妙地废除了上帝的诫命。 10摩西说,‘要孝敬父母’,又说,‘咒骂父母的,必被处死。’ 11你们却认为人若对父母说,‘我把供养你们的钱财已经全部奉献给上帝了’, 12他就可以不奉养父母。 13你们就是这样为了拘守传统而废除上帝的道,类似的情形还有很多。”

内心的污秽

14耶稣又召集众人,教导他们说:“我的话,你们要听明白, 15从外面进去的不会使人污秽,只有从人里面发出来的才会使人污秽。 16有耳可听的,都应当听!”

17耶稣离开众人,进了屋子,门徒问祂这比喻的意思。 18耶稣说:“你们也不明白吗?你们不知道吗?从外面进去的,不会使人污秽, 19因为不能进入他的心,只能进他的肠胃,最后会排出来,也就是说所有的食物都是洁净的。 20从人里面发出来的才使人污秽, 21因为从里面,就是从人的心里能够生出恶念、苟合、偷盗、谋杀、 22通奸、贪婪、邪恶、诡诈、放荡、嫉妒、毁谤、骄傲、狂妄。 23这一切恶事都是从里面生出来的,能使人污秽。”

外族妇人的信心

24耶稣从那里启程去泰尔西顿地区。祂进了一户人家,原本不想让人知道,却无法避开人们的注意。 25-26当时有一个妇人的小女儿被污鬼附身,她听见耶稣的事,就来俯伏在祂脚前,恳求祂赶出她女儿身上的鬼。这妇人是希腊人,来自叙利亚腓尼基

27耶稣对她说:“要先让儿女们吃饱,因为把儿女的食物丢给狗吃不合适。”

28妇人说:“主啊,你说的对,但桌子下的狗也吃孩子们掉下来的碎渣呀!”

29耶稣说:“因为你这句话,你回去吧,鬼已经离开你的女儿了。”

30她回到家里,见女儿躺在床上,鬼已经离开了。

医治聋哑的人

31耶稣离开泰尔地区,经过西顿,来到低加坡里地区的加利利湖。 32有人带着一个又聋又哑的人来见耶稣,恳求祂把手按在这个人身上。 33耶稣就带他离开众人走到一边,用指头伸进他的耳朵,又吐唾沫抹他的舌头, 34望天长叹,对他说:“以法大!”意思是“开了吧!” 35他的耳朵立刻开了,舌头灵活了,说话也清楚了。 36耶稣吩咐他们不要将这事告诉人。可是耶稣越是这样吩咐,他们越是极力宣扬, 37听见的人都十分惊奇,说:“祂做的事好极了,甚至叫聋子听见,哑巴说话!”

Hausa Contemporary Bible

Markus 7:1-37

Mai tsabta da marar tsabta

(Mattiyu 15.1-9)

1Farisiyawa da waɗansu malaman dokoki waɗanda suka zo daga Urushalima, suka taru kewaye da Yesu. 2Sai suka ga waɗansu daga cikin almajiransa suna cin abinci da hannuwa marasa tsabta, wato, da ba a wanke ba. 3(Farisiyawa da dukan Yahudawa ba sa cin abinci, sai sun wanke hannuwa sarai tukuna, yadda al’adun dattawa suka ce. 4Sa’ad da suka dawo daga wurin kasuwanci, dole su wanke hannu kafin su ci abinci. Sukan kuma kiyaye waɗansu al’adu da yawa, kamar wanken kwafuna, tuluna da butoci.7.4 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na farko-farko suna da tuluna, butoci da kujeru)

5Saboda haka, Farisiyawa da malaman dokoki suka tambayi Yesu, suka ce, “Don me almajiranka ba sa bin al’adun dattawa, a maimakon haka suna cin abinci da hannuwa marasa tsabta?”

6Ya amsa ya ce, “Daidai ne Ishaya ya yi annabci game da ku munafukai; kamar yadda yake a rubuce cewa,

“ ‘Waɗannan mutane da baki suke girmama ni,

amma zukatansu sun yi nesa da ni.

7A banza suke mini sujada,

koyarwarsu, dokokin mutane ne kawai.’7.7 Ish 29.13

8Kun yar da umarnan Allah, kuna bin al’adun mutane.”

9Ya kuma ce musu, “Kuna da hanya mai sauƙi na ajiye umarnan Allah a gefe ɗaya, don ku kiyaye al’adunku! 10Gama Musa ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’7.10 Fit 20.12; M Sh 5.16 kuma, ‘Duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.’7.10 Fit 21.17; Fir 20.9 11Amma ku, kukan ce, in mutum ya ce wa mahaifinsa, ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da ya kamata ku samu daga wurina, Korban ne,’ (wato, abin da aka keɓe wa Allah), 12sa’an nan haka ba kwa ƙara barinsa yă yi wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa wani abu. 13Ta haka kuke rushe maganar Allah ta wurin al’adun da kuke miƙa wa ’ya’yanku. Haka kuma kuke yin abubuwa da yawa.”

(Mattiyu 15.10-20)

14Sai Yesu ya sāke kiran taron wurinsa ya ce, “Ku saurare ni dukanku, ku kuma fahimci wannan. 15Ba abin da yake shiga mutum daga waje ba ne yake ƙazantar da shi. Sai dai abin da ya fita daga cikin mutum ne, yake ƙazantar da shi.”7.15 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na farko-farko suna da “marar tsabta.” 16 Duk mai kunnuwan ji, yă ji

17Bayan ya bar taron, ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali. 18Ya ce, “Ashe, ba ku da saurin ganewa? Ba ku gane cewa ba abin da yake shiga mutum daga waje ba ne yake ƙazantar da shi. 19Gama ba ya shiga cikin zuciyarsa, sai dai cikin tumbinsa, sa’an nan kuma yă fita daga jikinsa.” (Da faɗin haka, Yesu ya nuna tsabtar kowane irin abinci.)

20Ya ci gaba, “Abin da yake fitowa daga mutum ne yake ƙazantar da shi. 21Gama daga ciki, daga zuciyar mutane, mugayen tunani suke fitowa, fasikanci, sata, kisankai, zina, 22kwaɗayi, ƙeta, ruɗu, ƙazantaccen sha’awa, kishi, ɓata suna, girman kai da kuma wauta. 23Duk waɗannan mugayen abubuwa daga cikin suke fitowa, suna kuma ƙazantar da mutum.”

Bangaskiyar Baheleniya

(Mattiyu 15.21-28)

24Sai Yesu ya bar wurin, ya kuma tafi wajajen Taya. Ya shiga wani gida, bai kuwa so kowa yă sani ba. Duk da haka, bai iya ɓoye kasancewarsa ba. 25Da jin labarinsa, sai wata mace wadda ƙaramar diyarta tana da mugun ruhu, ta zo ta durƙusa a gabansa. 26Macen kuwa mutuniyar Hellenawa ce, an haife ta a Funisiya a Suriya. Ta roƙi Yesu yă fitar da aljani da yake jikin diyarta.

27Yesu ya ce mata, “Da farko, bari ’ya’ya su ci su ƙoshi tukuna, gama ba daidai ba ne, a ɗauki burodin yara a jefa wa karnukansu.”

28Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, ko karnuka ma da suke ƙarƙashin tebur, sukan ci burbuɗin da suke fāɗuwa daga abincin yara.”

29Sai ya ce mata, “Saboda irin wannan amsa, ki tafi, aljanin ya rabu da diyarki.”

30Ta tafi gida, ta tarar da diyarta kwance a gado, aljanin kuwa ya fita.

Warkar da kurma wanda yake kuma bebe

31Sai Yesu ya bar wajajen Taya, ya bi ta Sidon har zuwa Tekun Galili da kuma cikin yankin Dekafolis.7.31 Wato, Birane Goma 32A can ne waɗansu mutane suka kawo masa wani kurma, wanda da ƙyar yake magana. Sai suka roƙe shi yă ɗibiya hannunsa a kan mutumin.

33Bayan da ya jawo shi gefe, sai Yesu ya sa yatsotsinsa a kunnuwan mutumin, ya tofa miyau ya kuma taɓa harshen mutumin. 34Ya ɗaga kai sama, ya ja numfashi mai zurfi, sa’an nan ya ce masa,“Effata!” (Wato, “Buɗe!”). 35Bayan ya faɗa haka, sai kunnuwan mutumin suka buɗe, harshensa kuma ya kunce, sai ya fara magana sarai.

36Yesu ya umarce su, kada su gaya wa kowa. Amma ƙara yawan kwaɓarsu ƙara yawan yaɗa labarin suke ta yi. 37Mutane suka cika da mamaki, suka ce, “Kai, ya yi kome daidai. Har ma yana sa kurame su ji, bebaye kuma su yi magana.”