马可福音 12 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

马可福音 12:1-44

凶狠的佃户

1耶稣用比喻对他们说:“有人开辟了一个葡萄园,在四周筑起篱笆,又在园中挖了一个榨酒池,建了一座瞭望台,然后把葡萄园租给佃户,就出远门了。

2“到葡萄成熟时,园主派一个奴仆去收取他该得的一份。 3那些佃户却捉住那个奴仆,打了他一顿,使他空手而归。

4“园主又差另一个奴仆去。这一次,佃户不但侮辱他,还把他打得头破血流。 5园主再派一个奴仆前往,他们却把他杀掉了。园主后来派去的人不是挨打,就是被杀。 6最后只剩下园主的爱子,园主就派他去,以为那些佃户会尊重他的儿子。 7这班佃户却彼此商量说,‘这个就是园主的继承人。来吧!我们杀掉他,产业就归我们了。’

8“于是他们抓住他,杀了他,把他抛到葡萄园外。 9那么,园主会采取什么行动呢?他必定会来杀掉这些佃户,把葡萄园转给别人。 10圣经上说,

“‘工匠丢弃的石头已成了房角石。

11这是主的作为,

在我们看来奇妙莫测。’

你们没有读过这经文吗?”

12他们听出这比喻是针对他们说的,就想逮捕耶稣,但又害怕百姓,只好先离开了。

纳税给凯撒的问题

13后来,他们派了几个法利赛人和希律党人到耶稣那里,企图利用祂所说的话设计陷害祂。

14他们上前对耶稣说:“老师,我们知道你诚实无伪,不看人的情面,因为你不以貌取人,而是按真理传上帝的道。那么,向凯撒纳税对不对呢? 15我们该不该纳呢?”耶稣看破他们的阴谋,就说:“你们为什么试探我呢?拿一个银币来给我看。”

16他们就拿来一个银币,耶稣问他们:“上面刻的是谁的像和名号?”

他们说:“凯撒的。”

17耶稣说:“属于凯撒的东西应该给凯撒,属于上帝的东西应该给上帝。”

他们听了这话,都很惊奇。

论复活

18撒都该人向来不相信有复活的事,他们来问耶稣: 19“老师,摩西为我们写下律例,如果一个人死了,遗下妻子,又没有儿女,他的兄弟就当娶嫂嫂,替哥哥传宗接代。 20有弟兄七人,老大结了婚,没有孩子就死了。 21二弟把大嫂娶过来,也没有生孩子就死了,三弟也是一样, 22七个人都没有留下孩子。最后,那女人也死了。 23那么,到复活的时候,她将是谁的妻子呢?因为七个人都娶过她。”

24耶稣说:“你们弄错了,因为你们不明白圣经,也不知道上帝的能力。 25死人复活之后,将不娶也不嫁,就像天上的天使一样。 26关于死人复活的事,你们没有读过摩西书有关火中荆棘的记载吗?上帝对摩西说,‘我是亚伯拉罕的上帝,以撒的上帝,雅各的上帝。’ 27上帝不是死人的上帝,而是活人的上帝。你们大错了!”

最大的诫命

28有一位律法教师听到他们的辩论,觉得耶稣的回答很精彩,就走过去问道:“诫命中哪一条最重要呢?”

29耶稣回答道:“最重要的诫命是,‘听啊,以色列!主——我们的上帝是独一的主。 30你要全心、全情、全意、全力爱主——你的上帝’; 31其次就是‘要爱邻如己’。再也没有任何诫命比这两条更重要了。”

32那位律法教师说:“老师,你说的对,上帝只有一位,除祂以外,别无他神。 33我们要全心、全意、全力爱祂,又要爱邻如己。这样做比献什么祭都好。”

34耶稣见他答得很有智慧,就告诉他:“你离上帝的国不远了。”此后,没人再敢问耶稣问题了。

基督的身份

35耶稣在圣殿里教导的时候,问道:“律法教师为什么说基督是大卫的后裔呢? 36大卫自己曾经受圣灵的感动,说,

“‘主对我主说,

你坐在我的右边,

等我使你的仇敌伏在你脚下。’

37既然大卫自己称基督为主,基督又怎能是大卫的后裔呢?”百姓听得津津有味。 38耶稣又教导他们,说:“你们要提防律法教师,他们爱穿着长袍招摇过市,喜欢人们在大街上问候他们, 39又喜欢会堂里的上座和宴席中的首位。 40他们侵吞寡妇的财产,还假意做冗长的祷告。这种人必受到更严厉的惩罚。”

穷寡妇的奉献

41然后,耶稣走到圣殿的奉献箱对面坐下,看大家怎样奉献。很多财主奉献了大量的钱。 42后来一个穷寡妇来了,投进了相当于一文钱的两个小铜钱。 43耶稣叫门徒来,说:“我实在告诉你们,这位穷寡妇比其他人奉献的都多, 44因为他们不过奉献了自己剩余的,但这穷寡妇却奉献了她赖以为生的。”

Hausa Contemporary Bible

Markus 12:1-44

Misalin ’yan haya

(Mattiyu 21.33-46; Luka 20.9-19)

1Sa’an nan ya fara yi musu magana da misalai ya ce, “Wani mutum ya shuka gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa rami domin matsin inabin, ya kuma gina ɗakin gadi. Sai ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, sa’an nan ya yi tafiya. 2Da lokacin girbi ya yi, sai ya aiki wani bawa wajen ’yan hayan, don yă karɓo masa ’ya’yan inabin daga wurinsu. 3Amma suka kama shi, suka yi masa dūka, suka kore shi hannun wofi. 4Sai ya sāke aikan wani bawa wurinsu, amma suka bugi wannan mutum a kai, suka wulaƙanta shi. 5Har yanzu ya sāke aikan wani. Wannan kuwa suka kashe. Ya aika waɗansu da yawa; suka bubbuge waɗansu, sauran kuwa suka kashe.

6“Sauran mutum ɗaya da ya rage ya aika, ɗa, da yake ƙauna. Daga ƙarshe sai ya aike shi, yana cewa, ‘Za su girmama ɗana.’

7“Amma ’yan hayan suka ce wa juna, ‘Aha! Wannan shi ne magājin. Ku zo mu kashe shi, gādon kuma yă zama namu.’ 8Sai suka kama shi suka kashe, suka jefa shi bayan gonar inabin.

9“To, me, mai gonar inabin zai yi ke nan? Zai zo yă karkashe dukan ’yan hayan nan, ya kuma ba wa waɗansu gonar inabin. 10Ba ku taɓa karanta wannan Nassi ba,

“ ‘Dutsen da magina suka ƙi,

shi ne kuwa ya zama dutsen kusurwan gini.

11Ubangiji ya yi wannan,

ya kuma yi kyau a idanunmu’?”12.11 Zab 118.22,23

12Sai manyan Firistoci da malaman dokoki da shugabanni suka nemi hanyar da za su kama shi, domin sun gane ya yi misalin a kansu ne. Amma suka ji tsoron taron, saboda haka suka bar shi suka yi tafiyarsu.

Biyan haraji ga Kaisar

(Mattiyu 22.15-22; Luka 20.20-26)

13Daga baya, sai suka tura waɗansu Farisiyawa da mutanen Hiridus zuwa wurin Yesu, domin su sa masa tarko a cikin maganarsa. 14Suka zo wurinsa suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci. Ba ka bin ra’ayin mutane, don ba ka nuna bambanci. Amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya. Daidai ne a biya wa Kaisar haraji, ko babu? 15Mu biya ko kada mu biya?”

Amma Yesu ya san munafuncinsu, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko? Ku kawo mini dinari in ga.” 16Suka kawo masa kuɗin, sai ya tambaye, su ya ce, “Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne wannan?”

Suka ce, “Na Kaisar.”

17Sai Yesu ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku ba wa Allah kuma abin da yake na Allah.”

Suka yi mamakinsa ƙwarai.

Aure a tashin matattu

(Mattiyu 22.23-33; Luka 20.27-40)

18Sa’an nan Sadukiyawa da suke cewa, babu tashin matattu, suka zo masa da tambaya. 19Suka ce, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa, in ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata babu ’ya’ya, dole mutumin ya auri gwauruwar, yă kuma samo wa ɗan’uwansa ’ya’ya. 20To, an yi waɗansu ’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu babu ’ya’ya. 21Na biyun ya auri gwauruwar, sai shi ma ya mutu, babu ’ya’ya. Haka kuma na ukun. 22A gaskiya, ba ko ɗaya daga cikin bakwai ɗin da ya bar ’ya’ya. Daga ƙarshe, macen ta mutu. 23To, a tashin matattu, matar wa za tă zama, don duk su bakwai nan sun aure ta?”

24Yesu ya ce, “Ashe, ba a cikin kuskure kuke ba saboda rashin sanin Nassi, ko ikon Allah? 25Sa’ad da matattu suka tashi, ba za su yi aure ba, ba kuwa za a ba da su ga aure ba. Za su zama kamar yadda mala’iku suke a cikin sama. 26Game da tashin matattu kuwa, ashe, ba ku karanta a cikin littafin Musa ba, game da labarin ɗan kurmin nan mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, yadda Allah ya yi magana da shi ya ce, ‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’?12.26 Fit 3.6 27Shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne. Kun yi mummunan kuskure!”

Dokar da ta fi girma duka

(Mattiyu 22.23-33; Luka 20.27-40)

28Wani daga cikin malaman dokoki ya zo ya ji suna muhawwara. Da ya lura cewa Yesu ya amsa musu daidai, sai ya tambaye shi ya ce, “A cikin dukan dokoki, wacce ta fi girma duka?”

29Yesu ya ce, “Wadda ta fi girma duka, ita ce wannan. ‘Ku saurara, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne. 30Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan hankalinka, da kuma dukan ƙarfinka.’12.30 M Sh 6.4,5 31Na biyun ita ce, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’12.31 Fir 19.18 Ba wata doka da ta fi waɗannan.”

32Mutumin ya ce, “Malam, ka faɗi daidai. Daidai ne da ka ce, Allah ɗaya ne, babu kuma wani sai shi. 33Nuna ƙauna ga Allah da dukan zuciyarka, da dukan ganewarka, da dukan ƙarfinka, da kuma nuna ƙauna ga maƙwabcinka kamar kanka, ya fi dukan hadayun ƙonawa da sadakoki.”

34Da Yesu ya ga ya amsa da hikima, sai ya ce masa, “Ba ka da nisa da mulkin Allah.” Daga lokacin, ba wanda ya yi karambani yin masa wata tambaya.

Kiristi ɗan wane ne?

(Mattiyu 22.41-46; Luka 20.41-44)

35Yayinda Yesu yake koyarwa a filin haikalin, sai ya yi tambaya ya ce, “Yaya malaman dokoki suke cewa Kiristi ɗan Dawuda ne? 36Dawuda da kansa ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce,

“ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,

“Zauna a hannun damana

sai na sa abokan gābanka

a ƙarƙashin sawunka.” ’12.36 Zab 110.1

37Dawuda da kansa ya kira shi ‘Ubangiji.’ To, ta yaya zai zama ɗansa?”

Taro mai yawa suka saurare shi da murna.

(Mattiyu 23.1-36; Luka 20.45-47)

38Sa’ad da Yesu yake koyarwa ya ce, “Ku lura da malaman dokoki. Sukan so yin tafiya a manyan riguna, a kuma dinga gaishe su a wuraren kasuwanci. 39Sukan kuma nemi wuraren zama mafi daraja a majami’u, da kuma wuraren zaman manya a bukukkuwa. 40Suna ƙwace gidajen gwauraye, kuma don nuna iyawa, sukan yi dogayen addu’o’i. Irin mutanen nan, za su sha hukunci mai tsanani sosai.”

Bayarwar gwauruwa

41Yesu ya zauna ɗaura da inda ake bayarwa, ya kuma dubi yadda taron suke sa kuɗinsu a cikin ɗakunan ajiya haikali. Masu arziki da yawa suka zuba kuɗaɗe masu yawa. 42Amma wata matalauciya gwauruwa, ta zo ta saka anini biyu, da suka yi daidai da rabin kobo.

43Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, abin da matalauciya gwauruwan nan ta zuba cikin ɗakunan ajiya nan ya fi na sauran dukan. 44Dukansu sun bayar ne daga cikin arzikinsu; ita kuwa, daga cikin talaucinta, ta ba da kome, duk abin da take da shi na rayuwa.”