使徒行传 19 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

使徒行传 19:1-41

保罗在以弗所传道

1亚波罗哥林多时,保罗已取道内陆重回以弗所,在那里遇见几个门徒。 2保罗问他们:“你们信的时候有没有领受圣灵?”

他们说:“没有!我们从来没有听过圣灵的事。”

3保罗说:“那么,你们受的是什么洗礼呢?”

他们说:“是约翰的洗礼。”

4保罗说:“约翰的洗礼是悔改的洗礼,约翰告诉百姓要信在他以后来的那位——耶稣。”

5他们听后,立刻奉主耶稣的名受了洗。 6保罗把手按在他们身上时,圣灵便降在他们身上,他们就说方言,讲上帝的信息。 7这次共有十二个人。

8保罗一连三个月勇敢地在会堂里传道,与人辩论上帝国的事,劝导他们。 9可是有些人仍然顽固不信,还当众毁谤上帝的道。保罗便带着门徒离开他们,天天在推喇奴的学堂辩论。 10这样持续了两年,亚细亚全境的居民,无论是犹太人还是希腊人,都听见了主的道。 11上帝又借着保罗的手行了一些非凡的神迹, 12甚至只要将保罗身上的手帕或围裙放在病人身上,病人就痊愈了,邪灵也会离开所附的人。

13那时,有几个走江湖的犹太术士也想用耶稣的名赶鬼,他们向那些被邪灵附身的人说:“我奉保罗所传讲的耶稣之名,命令你们出来!” 14做这事的有犹太祭司长士基瓦的七个儿子。

15邪灵回答说:“耶稣,我认识;保罗,我也知道。但你们是谁?” 16被邪灵附身的人随即扑向他们,攻击他们,制服了他们,使他们赤着身子带着伤从屋里逃走了。

17以弗所犹太人和希腊人知道了这件事,都惊惧不已。主耶稣的名因此大受尊崇。 18许多已经信耶稣的人都前来认罪,公开承认自己的恶行。 19又有许多行邪术的人把他们的书堆在一起,当众焚烧。根据当时的估价,这些书约值五万银币。 20主的道就这样传开了,大大兴旺起来。

21这些事以后,保罗决定经过马其顿亚该亚回到耶路撒冷。他说:“到了那里之后,我必须去罗马看看。” 22于是,他派提摩太以拉都两位同工先去马其顿,自己暂时留在亚细亚

以弗所的骚乱

23就在这时,由于主的道,以弗所又起了很大的骚乱。 24一个名叫底米丢的银匠以制造亚底米女神银龛为业,使从事这门生意的工匠获利丰厚。 25他召集了工匠和同行的人,说:“各位都知道我们靠这一行发财, 26可是你们都看到了,也听见了,那个保罗以弗所亚细亚全境说服、误导了许多人,说什么人手所造的不是神。 27这样下去,不但我们的行业会遭人贬抑,连亚底米女神庙也会被人轻看,甚至全亚细亚及普世尊崇的女神也会威严扫地!”

28众人听后,怒气填胸,高声喊叫:“以弗所人的亚底米女神真伟大!” 29全城陷入一片混乱。众人抓住保罗的两个同伴——马其顿该犹亚里达古,拖着他们冲进戏院。 30保罗想进去,但门徒不许他去。 31他的好友——亚细亚的几位官员也派人劝他别冒险进入戏院。

32这时,戏院里面的人都在大喊大叫,混乱不堪。其实大部分人根本不知道自己为什么聚在那里。 33这时,人群中的犹太人把亚历山大推到前面,请他解释。亚历山大举手示意大家安静,听他发言。 34但众人认出他是个犹太人,便又开始一起高呼:“以弗所人的亚底米女神真伟大!”这样喊了两个小时。

35最后,城里的书记官出面调停,说:“各位以弗所市民,谁不知道以弗所城守护着亚底米女神庙和从宙斯那里掉下来的神像呢? 36既然这是无可否认的事实,你们就该安静,不可鲁莽行事。 37你们带来的这些人既没有偷庙里的东西,也没有亵渎我们的女神。 38如果底米丢和他的同行要控告谁,大可到法庭或总督那里提出诉讼。 39倘若你们还有其他的要求,也可以通过合法的会议解决。 40今天的骚乱实在没有道理,难免会被查问,到时候我们很难交代。” 41说完,便叫众人散去。

Hausa Contemporary Bible

Ayyukan Manzanni 19:1-41

Bulus a Afisa

1Lokacin da Afollos yake a Korint, Bulus ya bi hanyar da ta ratsa ta Asiya ya zo Afisa. A can ya sadu da waɗansu almajirai, 2sai ya tambaye, su ya ce, “Kun karɓi Ruhu Mai Tsarki sa’ad da kuka gaskata?”

Suka amsa suka ce, “A’a, ba mu ma san akwai Ruhu Mai Tsarki ba.”

3Saboda haka Bulus ya yi tambaya ya ce, “To, wace baftisma aka yi muku?”

Suka ce, “Baftismar Yohanna.”

4Bulus ya ce, “Ai, baftismar Yohanna, baftisma ce ta tuba. Ya ce wa mutane su gaskata a wani wanda yake zuwa bayansa, wato, Yesu.” 5Da ji wannan, sai aka yi musu baftisma a cikin sunan Ubangiji Yesu. 6Da Bulus ya ɗibiya musu hannuwansa, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauka musu, suka kuwa yi magana da harsuna, suka kuma yi annabci. 7Mutane kuwa su wajen mutum goma sha biyu ne.

8Bulus ya shiga majami’a ya yi magana gabagadi a can na watanni uku, yana muhawwara yana kuma rinjayarsu game da mulkin Allah. 9Amma waɗansunsu suka taurara; suka ƙi su gaskata kuma a gaban jama’a suka yi baƙar magana game da Hanyar. Bulus kuwa ya bar su. Ya tafi tare da almajirai ya dinga tattaunawa da su kullum a babban ɗakin jawabi na Tirannus. 10Wannan ya ci gaba har shekara biyu, sai da ya sa dukan Yahudawa da Hellenawa da suke zaune a lardin Asiya suka ji maganar Ubangiji.

11Allah ya yi ayyukan banmamakin da suka wuce misali ta hannu Bulus, 12har ma ana kai hankicif da adikan da suka taɓa jikinsa wa marasa lafiya, suka kuwa warke daga cututtukansu mugayen ruhohi kuma suka rabu da su.

13Waɗansu Yahudawa masu yawo gari-gari suna fitar da mugayen ruhohi suka yi ƙoƙari su yi amfani da sunan Ubangiji Yesu a kan waɗanda suke da aljanu. Suna cewa, “A cikin sunan Yesu wanda Bulus yake wa’azi, na umarce ku, ku fito.” 14’Ya’ya bakwai maza na Sikeba, wani babban firist na Yahudawa, suna yin haka. 15Wata rana mugun ruhu ya amsa musu ya ce, “Yesu kam na sani, Bulus kuma na sani, amma ku kuma su wane ne?” 16Sai mutumin da yake da mugun ruhun ya fāɗa musu ya sha ƙarfinsu duka. Ya yi musu dūkan tsiya har suka fita a guje daga gidan tsirara jini yana zuba.

17Da Yahudawa da Hellenawan da suke zama a Afisa suka ji wannan labari sai duk tsoro ya kama su, aka kuwa darjanta sunan Ubangiji Yesu ƙwarai. 18Da yawa cikin waɗanda suka gaskata yanzu suka zo a fili suka furta mugayen ayyukansu. 19Waɗansu masu yin sihiri suka kawo naɗaɗɗun littattafansu wuri ɗaya suka kuwa ƙone su a gaban jama’a. Sa’ad da aka lissafta yawan kuɗin naɗaɗɗun littattafan nan, sai jimillar ta kai darik dubu hamsin. 20Ta haka maganar Ubangiji ta bazu ko’ina ta kuma yi ƙarfi.

21Bayan dukan wannan ya faru, sai Bulus ya yanke shawara ya ratsa Makidoniya da Akayya in za shi Urushalima. Ya kuma ce, “Bayan na tafi can, dole in ziyarci Roma ita ma.” 22Sai ya aiki biyu daga cikin masu taimakonsa, Timoti da Erastus, zuwa Makidoniya, yayinda shi kuwa ya ɗan dakata a lardin Asiya.

Hargitsi a Afisa

23Kusan wannan lokaci sai aka yi wani babban hargitsi game da wannan Hanyar. 24Wani maƙerin azurfa, mai suna Demetiriyus wanda yake ƙera siffar ɗakunan tsafin Artemis da azurfa, ba ƙaramin ciniki yake kawo wa mutane masu sana’an nan ba. 25Sai ya tara su wuri ɗaya, tare da masu irin wannan sana’ar ya ce, “Ku jama’a, kun san muna samun kuɗin shiga sosai daga wannan sana’a. 26Kuma kuna ji kuna gani yadda Bulus ɗin nan ya shawo kan mutane da yawa ya kuma sa suka bauɗe a nan a Afisa da dukan lardin Asiya. Yana cewa alloli da mutum ya ƙera ba alloli ba ne ko kaɗan. 27Akwai hatsari, ba kawai cewa sana’armu za tă rasa sunanta mai daraja ba, amma za a yi banza da ɗakin tsafin Artemis alliyarmu mai girma, alliyar kanta wadda ake bauta a ko’ina a yankin Asiya da kuma duniya, za a raba ta da darajarta.”

28Da suka ji haka, sai suka yi fushi ƙwarai suka fara ihu suna cewa, “Girma ta tabbata ga Artemis ta Afisawa!” 29Jim kaɗan sai hayaniya ta tashi a dukan birnin. Sai mutane suka cafke Gayus da Aristarkus, abokan tafiyar Bulus daga Makidoniya, suka ruga da zuwa fili da nufi ɗaya. 30Bulus ya so ya bayyana a gaban taron, amma almajirai ba su bar shi ba. 31Har waɗansu shugabannin lardin ma, abokan Bulus, suka aika masa suna roƙonsa kada yă kuskura ya shiga filin nan.

32Taron kuwa ya ruɗe. Waɗansu suna ihu suna ce abu kaza, waɗansu kuma wani abu dabam. Yawancin mutane kuma ba su ma san abin da ya sa suke a wurin ba. 33Yahudawa suka tura Alekzanda gaba, sai waɗansu a taron suka riƙa yin masa ihu. Sai ya ɗaga hannu don a yi shiru don yă kāre kansa a gaban mutane. 34Amma sa’ad da suka gane shi mutumin Yahuda ne, sai duk suka yi ihu gaba ɗaya na kusa sa’a biyu, suna cewa, “Girma ta tabbata ga Artemis ta Afisawa!”

35Sai magatakardar birnin ya sa taron su yi shiru, sa’an nan ya ce, “Mutanen Afisa, ashe duk duniya ba tă san cewa birnin Afisa ce mai lura da haikalin Artemis mai girma da kuma siffarta da ya fāɗi daga sama ba? 36Saboda haka, da yake ba dama a yi mūsun wannan gaskiya, ya kamata ku natsu kada ku yi kome da garaje. 37Kun kawo mutanen nan a nan, gashi kuwa ba su yi fashin haikali ba, ba su kuwa saɓa wa alliyarmu ba. 38To, in haka ne, in Demetiriyus da abokan sana’arsa suna da wata magana game da wani ai, kotuna suna nan a buɗe, akwai kuma muƙaddasai. Suna iya kai ƙara. 39In kuma akwai wani abu har yanzu da kuke so ku kawo, dole a daidaita shi a majalisa. 40Yadda yake a yanzu, muna a hatsarin amsa zargin ta da hargitsi saboda abin da ya faru yau. Da yake ba za mu iya ba da dalilin da ya sa aka yi wannan hargitsi ba.” 41Bayan da ya faɗi haka, sai ya sallami taron.