以弗所书 2 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

以弗所书 2:1-22

靠恩典、凭信心

1你们从前死在过犯和罪恶之中。 2那时,你们随从今世的风俗,顺服在空中掌权的魔鬼,就是如今在一切叛逆上帝之人心中运行的邪灵。 3我们以前也在他们当中随从罪恶的本性2:3 罪恶的本性”希腊文是“肉体”。,放纵肉体和心中的私欲,与其他人一样本是惹上帝发怒的人。

4然而上帝有丰富的怜悯,祂深爱我们, 5尽管我们死在过犯之中,祂仍然使我们和基督一同活了过来。你们得救是因为上帝的恩典。 6在基督耶稣里,上帝使我们与基督一同复活,一同坐在天上, 7好借着祂在基督耶稣里向我们所施的恩慈,向后世显明祂无可比拟的丰富恩典。 8你们得救是靠恩典,凭信心。这不是出于你们自己,而是上帝的礼物; 9也不是由于你们的行为,以免有人自夸。 10我们是上帝的杰作,是在基督耶稣里创造的,为要叫我们做祂预先安排给我们的美善之事。

在基督里合而为一

11因此,你们要记住,从前按照肉体来说你们是外族人,那些肉体上受过人手所行割礼的以色列人称你们为“没有受过割礼的”。 12那时,你们与基督无关,又不是以色列人,在上帝应许的诸约上是局外人,你们活在世上没有盼望,没有上帝。 13但你们这些从前远离上帝的人,如今在基督耶稣里,靠着祂所流的血已经被带到上帝面前。 14因为基督耶稣亲自给我们带来了和平,以自己的身体拆毁了以色列人和外族人之间充满敌意的隔墙,使双方合而为一, 15并废除了以诫命和规条为内容的律法制度。祂这样做是为了在自己里面把双方造成一个新人,成就和平, 16并借着十字架消灭彼此间的敌意,使双方借着一个身体与上帝和好。 17祂来传扬这平安的福音给你们这些离上帝很远的外族人,也给我们这些离上帝很近的以色列人。 18我们双方都是靠着祂在同一位圣灵的引导下来到父上帝面前。

19从此,你们不再是外人或过客,你们与众圣徒一样是天国的子民,是上帝家里的人了。 20你们已被建立在众使徒和先知们的基础上,基督耶稣自己是房角石。 21整座建筑的各部分都靠祂巧妙地连接在一起,逐渐成为主的圣殿。 22你们也靠着祂被建造在一起,成为上帝借着圣灵居住的地方。

Hausa Contemporary Bible

Afisawa 2:1-22

An raya ku a cikin Kiristi

1Ku kam, a dā ku matattu ne saboda laifofinku da kuma zunubanku. 2Kun yi rayuwa kamar yadda sauran mutanen duniya suke yi, cike da zunubi, kuna biyayya ga sarki masu ikon sarari sama, wato, ruhun nan da yanzu yake aiki a cikin masu ƙin biyayya ga Allah. 3Dukanmu a dā mun yi irin rayuwan nan a cikinsu, muna bin kwaɗayi da sha’awace-sha’awacen jikunanmu da tunaninmu. Kamar sauran mutane, mun cancanci fushin Allah. 4Amma saboda yawan ƙaunar da yake mana, Allah, wanda yake mai yawan jinƙai, 5ya ba mu rai sa’ad da ya tashe Kiristi daga matattu. Ta wurin alherin Allah ne aka cece ku. 6Allah ya tashe mu tare da Kiristi, ya kuma ba mu wurin zama tare da shi a cikin mulkin samaniya. 7Allah ya yi haka domin a tsararraki masu zuwa yă nuna yalwar alherinsa da ya wuce misali, an bayyana alheransa da ya yi mana ta wurin Kiristi Yesu. 8Allah ya cece ku ta wurin alheri sa’ad da kuka ba da gaskiya. Wannan kuwa ba yinku ba ne, kyauta ce daga Allah. 9Ba kuwa saboda aikin lada ba, don kada wani yă ɗaga kai. 10Ai, mu aikinsa ne, an sāke halittarmu a cikin Kiristi Yesu musamman domin mu yi kyawawan ayyuka, waɗanda Allah ya tanadar mana tun da fari, mu yi.

An sulhunta Yahudawa da al’ummai su zama ɗaya ta wurin Kiristi

11Saboda haka, ku tuna dā ku Al’ummai ne bisa ga haihuwa, waɗanda kuma ake kira masu “kaciya” sukan kira ku “marasa kaciya” (ga shi kuwa, kaciyar nan ta jiki ce, wadda ake yi da hannu). 12Ku kuma tuna a lokacin ba ku san Kiristi ba. A ware kuke daga mutanen Isra’ila, ba ku kuma da dangantaka da alkawaran da Allah ya yi da su. Kun yi zama a duniyan nan babu bege kuma babu Allah. 13Amma yanzu a cikin Kiristi Yesu, ku da dā kuke can da nesa an kawo ku kusa ta wurin jinin Kiristi.

14Gama shi kansa shi ne salamarmu, shi ne ya kawo ƙungiyoyi biyu suka zama ɗaya, ya kuma rushe katangan nan ta ƙiyayya wadda ta raba mu. 15Kiristi ya ba da jikinsa don yă kawar da doka da dukan umarnanta da kuma ƙa’idodinta. Ya yi haka domin yă halicci sabuwar zuriya daga zuriyoyin nan biyu. Ta haka kuma ya kawo salama tsakaninsu. 16A kan gicciye, Kiristi ya kawar da ƙiyayyar da take tsakaninmu da juna. Ya kuma kawo sulhu tsakaninmu da Allah. 17Ya zo ya yi muku wa’azin salama; ku da kuke nesa da shi, ya kuma yi wa waɗanda suke kusa. 18Gama ta wurinsa dukanmu za mu iya zuwa gun Uba ta wurin Ruhu guda.

19Don haka, yanzu ku ba baƙi ba ne, ku kuma ba bare ba ne. Ku ’yan ƙasa ne tare da mutanen Allah, iyalin gidan Allah kuma. 20Ku gini ne wanda manzanni da annabawa suke tushensa, Kiristi kuma shi ne dutse mafi muhimmanci na ginin. 21Ta wurinsa ne dukan ginin yake a haɗe, shi ne kuma yake sa ginin yă yi girma, yă zama haikali mai tsarki domin Ubangiji. 22Ku ma sashe ne na wannan ginin da Kiristi ya yi inda Allah yake zaune ta wurin Ruhunsa.