Откровение 9 – CARS & HCB

Священное Писание

Откровение 9:1-21

1Затрубил пятый ангел, и я увидел звезду, упавшую с неба на землю. Звезде был дан ключ от колодца бездны. 2Когда звезда открыла колодец бездны, оттуда поднялся дым, как из огромной печи. От дыма из колодца потемнели даже солнце и небо. 3Из дыма вышла на землю саранча9:3 Ср. Исх. 10:12-14., которой дана была власть, какую имеют на земле скорпионы. 4Ей было запрещено причинять вред земной траве, любым зелёным растениям и любому дереву, но она могла вредить тем людям, у которых на лбу не было печати Всевышнего. 5Саранче не было разрешено убивать их, а только мучить пять месяцев. И люди мучились от боли, которая была как от укусов скорпиона. 6В те дни люди будут искать смерти и не смогут её найти, они захотят умереть, но сама смерть убежит от них.

7Саранча была похожа на боевых коней, готовых к сражению. На её головах было нечто вроде корон, как будто из золота, а её лица были похожи на человеческие. 8Её волосы напоминали женские, а зубы были похожи на клыки льва. 9На саранче была твёрдая, как железо, броня, и шум её крыльев напоминал шум коней и боевых колесниц, мчащихся на сражение9:7-9 См. Иоиль 1:6; 2:4-9.. 10У неё были хвосты, как у скорпионов, и жала, и в этих хвостах заключалась её власть вредить людям пять месяцев. 11Царём над ней был ангел бездны, его звали по-еврейски Абаддон, а по-гречески Аполлион («губитель»).

12Прошло первое горе, но ещё предстояли два других.

13Затрубил шестой ангел, и я услышал голос, раздававшийся от четырёх рогов золотого жертвенника, находящегося перед Всевышним9:13 См. Исх. 30:1-3.. 14Этот голос сказал шестому ангелу, держащему трубу:

– Освободи четырёх ангелов, которые связаны у великой реки Евфрат.

15И четыре ангела, которые были приготовлены для этого часа, дня, месяца и года, были освобождены, чтобы погубить третью часть человечества. 16Конное войско насчитывало двести миллионов всадников: я слышал их число.

17Я видел в моём видении этих коней и всадников: на них огненно-красная, тёмно-синяя и жёлтая, как сера, броня. Головы коней похожи на головы львов, и из их пасти выходят огонь, дым и сера. 18Этими тремя губительными силами – огнём, дымом и серой, выходившими из их пастей, была погублена третья часть людей. 19Сила коней заключается в их пастях и в их хвостах. Хвосты эти похожи на змей: у них есть головы, которыми они и жалят.

20Те, кто не был погублен этими бедствиями, так и не раскаялись в своих делах. Они по-прежнему поклонялись демонам и идолам из золота, серебра, бронзы, камня и дерева – идолам, которые не могут ни видеть, ни слышать, ни ходить9:20 См. Заб. 113:12-15; 134:15-17; Дан. 5:23.. 21Они не раскаялись ни в убийствах своих, ни в колдовстве, ни в разврате, ни в воровстве.

Hausa Contemporary Bible

Ruʼuya ta Yohanna 9:1-21

1Mala’ika na biyar ya busa ƙahonsa, sai na ga tauraron da ya fāɗo duniya daga sararin sama. Aka ba wa tauraron mabuɗin ramin Abis. 2Da ya buɗe Abis ɗin, sai hayaƙi ya taso daga cikin kamar hayaƙin matoya mai girma. Hayaƙin nan daga Abis ya duhunta rana da sararin sama. 3Daga cikin hayaƙin kuwa fāri suka fito zuwa cikin duniya aka kuma ba su iko irin na kunaman duniya. 4Aka faɗa musu kada su yi wa ciyawa na duniya lahani ko wani tsiro ko itace, sai dai su yi wa mutanen da ba su da hatimin Allah a goshinsu kaɗai lahani. 5Ba a ba su iko su kashe su ba, sai dai su ba su azaba na watanni biyar. Azabar da suka sha kuwa ya yi kamar ta harbin kunama sa’ad da ta harbi mutum. 6Cikin waɗannan kwanakin mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su samu ba; za su yi marmarin mutuwa, amma mutuwa za tă ɓace musu.

7Kamannin fārin nan kuwa yana kama da dawakan da aka shirya don yaƙi. A kawunansu kuwa da wani abu da ya yi kamar rawanin zinariya, fuskokinsu kuma sun yi kamar fuskokin mutane. 8Gashin kansu ya yi kamar gashin kan mata, haƙoransu kuma sun yi kamar haƙoran zakoki. 9Suna da sulkuna kamar sulkunan ƙarfe, ƙarar fikafikansu kuma ta yi kamar motsin dawakai da kekunan yaƙi masu yawa da suke rugawa zuwa yaƙi. 10Suna da wutsiyoyi da ƙari kamar kunamai, kuma a wutsiyoyinsu suna da iko su ba wa mutane azaba na wata biyar. 11Suna da sarkin da yake mulki a bisansu wanda yake mala’ikan Abis, wanda sunansa a harshen Yahudawa shi ne Abaddon, da harshen Hellenawa kuwa shi ne, Afolliyon.9.11 Abaddon da kuma Afolliyon suna nufin Maihallakarwa.

12Bala’i na fari ya wuce, sauran bala’i biyu suna nan zuwa.

13Mala’ika na shida ya busa ƙahonsa, sai na ji murya tana fitowa daga ƙahonin bagaden zinariya da suke a gaban Allah. 14Ta ce wa mala’ika na shida da yake da ƙahon, “Ka saki mala’iku huɗun nan da suke a daure a babban kogin Yuferites.” 15Mala’iku huɗun nan kuwa da aka shirya musamman don wannan sa’a da kuma don wannan rana da wata da kuma shekara aka sake su domin su kashe kashi ɗaya bisa uku na ’yan Adam. 16Yawan rundunan masu hawan dawakan nan mutum miliyon ɗari biyu ne. Na ji adadinsu.

17Dawakai da masu hawansu da na gani cikin wahayina sun yi kamar. Sulkunansu ja wur ne, baƙin shuɗi, da kuma rawaya kamar farar wuta. Kawunan dawakan sun yi kamar kawunan zakoki, daga bakunansu kuwa wuta, hayaƙi, da farar wuta suna fitowa. 18Aka kashe kashi ɗaya bisa uku na ’yan Adam da annobai uku na wuta, hayaƙi da farar wuta da suka fito daga bakunansu. 19Ƙarfin dawakan nan kuwa yana a bakunansu da wutsiyoyinsu; gama wutsiyoyinsu suna kama da macizai masu kawuna, da wutsiyoyin ne kuma suke yi wa mutane rauni.

20Sauran ’yan Adam da ba a kashe ta wajen waɗannan annobai ba kuwa har wa yau ba su tuba daga aikin hannuwansu ba; ba su daina bauta wa aljanu, da gumakan zinariya, azurfa, tagulla, dutse da na itace, gumakan da ba sa iya gani ko ji ko tafiya ba. 21Ba su kuma tuba daga kisankansu, sihirinsu, fasikancinsu ko kuma daga sace-sacensu ba.