Židům 1 – SNC & HCB

Slovo na cestu

Židům 1:1-14

Ježíš Kristus je rovný Otci

1Bůh mluvil odedávna k otcům mnoha různými způsoby prostřednictvím proroků a odhaloval jim postupně své plány. 2V tomto posledním čase k nám promluvil ve svém Synu.

Boží Syn je podivuhodná bytost. Bůh mu vše dal a skrze něho stvořil svět a vše, co je v něm. 3On vyzařuje Boží lásku. Každý jeho čin a každé jeho slovo dosvědčuje, že je Bůh. Řídí vesmír podmanivou silou svého rozkazu. Zemřel, aby očistil naše svědomí od všech hříchů, vstal z mrtvých a pak se posadil na čestné místo u Boha.

Boží Syn je vyšší než andělé

4Boží Syn převyšuje i Boží posly – anděly. Jeho jméno to dokazuje. 5Vždyť Bůh nikdy neřekl andělu:

„Ty jsi můj Syn,

kterého jsem dnes zplodil.“

Ani:

„Budu mu otcem a on mi bude synem.“

6Ale když uvádí svého prvorozeného Syna na zem, říká:

„Ať se mu klanějí všichni Boží andělé.“

7Bůh mluví o svých andělích jako o vanutí větru a plamenech ohně, 8ale o svém Synu říká:

„Ty budeš, Bože, vládnout navzdory všem změnám

a tvoje vláda bude spravedlivá.

9Miluješ spravedlnost a nenávidíš svévoli.

Proto ti Bůh učinil radost a vyvýšil tě nad tvé druhy.“

10„Ty jsi, Pane, na počátku učinil zemi

a nebesa jsou dílo tvých rukou.

11Nebesa se rozplynou, ale ty zůstaneš.

12Obnosí se jako plášť a jednou je odložíš a vyměníš.

Ty však nezestárneš a nezahyneš.“

13Bůh nikdy nevyzval žádného anděla,

aby se posadil na čestné místo nedaleko něho,

dokud mu nepodrobí všechny nepřátele.

14Andělé jsou jen duchovní poslové, kteří jsou vysíláni, aby pečovali o ty, kterým se má dostat spásy jako dědictví.

Hausa Contemporary Bible

Ibraniyawa 1:1-14

1A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri, 2amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. 3Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama. 4Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.

Ɗan ya fi Mala’iku

5Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa,

“Kai Ɗana ne;

yau na zama Uba a gare ka”1.5 Zab 2.7?

Ko kuwa,

“Zan zama Ubansa,

shi kuma zai zama Ɗana”1.5 2Sam 7.14; 1Tar 17.13?

6Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce,

“Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”

7Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce,

“Ya mai da mala’ikunsa iska,

bayinsa kuma harsunan wuta.”1.7 Zab 104.4

8Amma game da Ɗan ya ce,

“Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin,

adalci kuma zai zama sandan mulkinka.

9Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta;

saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka,

ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”1.9 Zab 45.6,7

10Ya kuma ce,

“Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya,

sammai kuma aikin hannuwanka ne.

11Su za su hallaka, amma kai kana nan;

dukansu za su tsufa kamar riga.

12Za ka naɗe su kamar mayafi,

kamar riga za su sauya.

Amma kai ba za ka canja ba,

shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”1.12 Zab 102.25-27

13Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa,

“Zauna a hannun damana,

sai na sa abokan gābanka

su zama matashin sawunka”1.13 Zab 110.1?

14Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?