התגלות 2 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

התגלות 2:1-29

1”את המכתב הראשון כתוב אל ראש2‏.1 ב 1 מילולית: מלאך; כך נכון גם בפרק ב׳ פסוקים 8 & 12 ובפרק ג׳ פסוקים 1, 7 & 14. קהילת אפסוס.

אלה דבריו של האוחז ביד ימינו את שבעת הכוכבים, והמתהלך בין שבע מנורות הזהב:

2’אני יודע את כל מעשיך הטובים; ראיתי את עמלך הקשה, את כוח סבלך ואני יודע שאינך סובל אנשים רשעים. בחנת בזהירות את דברי אלה שטוענים שהם שליחי האדון, וגילית שלא היו דברים מעולם – הם אינם שליחים, אלא שקרנים! 3בסבלנות ובאורך־רוח סבלת רבות למעני.

4אך דבר אחד יש לי נגדך: עזבת את אהבתך הראשונה! 5חשוב לרגע עד היכן הידרדרת! חזור בתשובה ונהג כפי שנהגת לראשונה. אם לא תחזור בתשובה, אבוא ואסיר את מנורתך ממקומה. 6לזכותך ייאמר שאתה מתעב את מעשי הניקולסים2‏.6 ב 6 לפי דעה אחת היו הניקולסים כת בקהילה הקדומה, על שם ניקולס מאנטיוכיה (מעשי השליחים ו 5) אשר שאפה להתפשר עם עובדי האלילים, על־מנת לאפשר למאמינים השתתפות בפעילויות חברתיות ודתיות של החברה שבה היו. הניקולסים כמו בלעם (במדבר כב לא 16) הפיצו תורת שקר המתירה זנות ואכילת זבחים שהוקרבו לאלילים. כשם שאני מתעב אותם.

7מי שמסוגל לשמוע – שיקשיב לדברי הרוח אל הקהילות.

למנצח אתן לאכול מפרי עץ החיים שנמצא בגן־העדן של אלוהים.‘

8”את המכתב השני כתוב אל ראש קהילת זמירנא.

אלה דברי הראשון והאחרון אשר מת וקם לתחייה:

9’אני יודע שאתה סובל קשות בגלל אמונתך, ואני יודע על העוני שלך, אך דע שמצפה לך עושר רב בשמים! אני גם יודע שמתנגדיך לועגים לך ומקללים אותך – הם קוראים לעצמם ”יהודים“, אך למעשה הם קהילתו של השטן! 10אני מזהיר אותך מראש: אל תפחד מפני הסבל שעומד לבוא עליך! בקרוב ישליך השטן אחדים מכם לכלא, כדי לנסותכם, וסבלכם יימשך עשרה ימים. היה נאמן עד מוות ואעניק לך את כתר החיים.

11מי שמסוגל לשמוע – שיקשיב לדברי הרוח אל הקהילות.

המנצח לא ימות במוות השני.‘

12”את המכתב השלישי כתוב אל ראש קהילת פרגמוס.

אלה דבריו של המחזיק בחרב החדה בעלת הלהב הכפול:

13’אני מכיר את עיר מגוריך – עיר שמרבית תושביה משרתים את השטן! למרות זאת שמרת על נאמנותך ולא התכחשת לי גם כאשר אנטיפס, עדי הנאמן, נרצח בעירכם על־ידי משרתי השטן.

14אף־על־פי־כן יש לי נגדך כמה דברים: יש ביניכם כאלה שדבקים בתורת בלעם, אשר לימד את בלק כיצד להשחית את עם־ישראל; לאכול זבחים שהוקרבו לאלילים, לזנות ולנאוף. 15מלבד זאת יש ביניכם כאלה שדבקים בתורת הניקולסים אשר תיעבתי. 16חזור בתשובה! אם תסרב, אבוא אליך בשעה בלתי צפויה ואלחם באנשים האלה בחרב פי.

17מי שמסוגל לשמוע – שיקשיב לדברי הרוח אל הקהילות.

את המנצח אאכיל מן נסתר, ואתן לו אבן לבנה שעליה חרוט שם חדש שידוע אך ורק למקבל האבן.‘

18”את המכתב הרביעי כתוב אל ראש קהילת תיאטירא.

אלה דברי בן־האלוהים אשר עיניו כלהבת אש ורגליו כנחושת נוצצת:

19’אני יודע את מעשיך הטובים, את אהבתך, אמונתך, עבודתך וכוח סבלך, ואני שמח לראות כיצד אתה הולך ומרבה את מעשיך הטובים.

20בכל זאת, יש לי נגדך דבר אחד: אתה מניח לאישה הזאת איזבל, שקוראת לעצמה נביאה, להסית את המאמינים לזנות ולנאוף. היא מסיתה אותם לנהל חיים בלתי־מוסריים ולאכול זבחים שהוקרבו לאלילים. 21נתתי לה הזדמנות לחדול ממעשיה המושחתים ולחזור בתשובה, אך היא סירבה. 22שים לב למה שאעשה לה: ארתק אותה למיטתה, ואם אלה שמנאפים איתה לא יחזרו בתשובה, אגרום להם צער וסבל נורא. 23גם את בניה אהרוג, וכל הקהילות תדענה שאני, האלוהים, בוחן כליות ולב ומשלם לכל איש כמעשיו.

24‏-25אני פונה אל שאר המאמינים בתיאטירא – אל אלה שלא הלכו בעקבות איזבל ולא למדו את ”האמת העמוקה“ של תורת השטן – ואומר: לא אכביד עליכם בעול נוסף, אולם שימרו היטב על מה שיש לכם עד שובי.

26למנצח ששומר על מעשי עד הסוף אתן שלטון על הגויים. 27הוא ינהיגם בשבט ברזל, וינפצם לרסיסים ככלי ביד היוצר. 28אכן, סמכותו תהיה כסמכות שקיבלתי אני מאבי. גם את כוכב השחר אתן למנצח.

29מי שמסוגל לשמוע – שיקשיב לדברי הרוח אל הקהילות.‘

Hausa Contemporary Bible

Ruʼuya ta Yohanna 2:1-29

Zuwa ga ikkilisiya a Afisa

1“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Afisa, ka rubuta,

Waɗannan su ne kalmomi na wannan wanda yake riƙe da taurari bakwai a hannunsa na dama yana kuma tafiya a tsakanin alkukan fitilu bakwai na zinariya.

2Na san ayyukanka, faman aikinka da daurewarka. Na san cewa ba ka iya haƙuri da mugayen mutane, ka gwada waɗanda suke cewa su manzanni ne, alhali kuwa ba haka ba ne, ka kuwa tarar cewa su na ƙarya ne. 3Kai kam ka daure ka kuma jimre da wahala saboda sunana, ba ka kuwa gaji ba.

4Duk da haka ina riƙe da wannan game da kai. Ka watsar da ƙaunarka ta farko. 5Ka tuna da matsayinka a dā kafin ka fāɗi! Ka tuba ka kuma yi ayyukan da ka yi da fari. In ba ka tuba ba, zan zo wajenka in ɗauke wurin ajiye fitilanka daga inda yake. 6Sai dai kana da wannan abu mai kyau. Ka ƙi ayyukan Nikolaitawa da ni ma nake ƙi.

7Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi ikon ci daga itacen rai, da yake cikin aljannar Allah.

Zuwa ga ikkilisiya a Simirna

8“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Simirna, ka rubuta,

Waɗannan su ne kalmomin wannan da yake na Farko da na Ƙarshe, wanda ya mutu ya kuma sāke tashi da rai.

9Na san wahalarka da kuma talaucinka, duk da haka kai mai arziki ne! Na san ɓata suna da waɗannan suke yi maka waɗannan da suke cewa su Yahudawa ne alhali kuwa ba haka ba ne, su dai majami’ar Shaiɗan ne. 10Kada ka ji tsoron wahalar da kake gab da sha. Ina gaya maka, Iblis zai sa waɗansunku a kurkuku don yă gwada ku. Za ku sha tsanani na kwana goma. Ka yi aminci ko da za a kashe ka, ni kuwa zan ba ka rawanin rai.

11Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara mutuwa ta biyu ba za tă cuce shi ba ko kaɗan.

Zuwa ga ikkilisiya a Fergamum

12“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Fergamum, ka rubuta,

Waɗannan su ne kalmomin wannan wanda yake da takobi mai kaifi biyu.

13Na san inda kake da zama, inda Shaiɗan yana da gadon sarautarsa. Duk da haka ka riƙe sunana da gaske. Ba ka yi mūsun bangaskiyarka gare ni ba, har ma a kwanakin Antifas, amintaccen mashaidina, wanda aka kashe a birninku, inda Shaiɗan yake zama.

14Duk da haka, ina da abubuwa kima game da kai. Kana da mutane a can waɗanda suke riƙe da koyarwar Bala’am, wanda ya koya wa Balak yă ja hankalin Isra’ilawa su yi zunubi ta wurin cin abincin da aka miƙa wa gumaka hadaya, su kuma yi fasikanci. 15Haka ma kana da waɗanda suke riƙe da koyarwar Nikolaitawa. 16Saboda haka ka tuba! In ba haka ba, zan zo wajenka ba da daɗewa ba in yaƙe su da takobin bakina.

17Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara zan ba shi kaɗan daga cikin ɓoyayyiyar Manna. Zan kuma ba shi farin dutse tare da sabon suna a rubuce a bisansa, sananne kawai ga mai karɓan dutsen.

Zuwa ga ikkilisiya a Tiyatira

18“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Tiyatira, ka rubuta,

Waɗannan su ne kalmomin Ɗan Allah, wanda idanunsa suna kama da harshen wuta wanda kuma ƙafafunsa suna kama da tagullar da aka goge.

19Na san ayyukanka, ƙaunarka da bangaskiyarka, hidimarka da daurewarka, kuma cewa kana yin abubuwa a yanzu fiye da abin da ka yi da farko.

20Duk da haka, ina da wannan game da kai. Kana haƙuri da matan nan Yezebel, wadda take kira kanta annabiya. Ta wurin koyarwarta tana ɓad da bayina ga yin fasikanci suka kuma ci abincin da aka miƙa wa gumaka. 21Na ba ta lokaci tă tuba daga fasikancinta, amma ba ta da niyya. 22Don haka zan jefa ta a kan gadon wahala, zan kuma sa waɗanda suke zina da ita, su sha azaba ƙwarai, sai dai in sun tuba daga hanyoyinta. 23Zan kashe ’ya’yanta. Sa’an nan dukan ikkilisiyoyi za su san cewa ni ne mai bincika zukata da tunani, zan kuwa sāka wa kowannenku gwargwadon ayyukansa.

24Yanzu, ina ce wa sauranku da kuke a Tiyatira, ku da ba ku riƙe da koyarwarta ba kuma ba ku koyi abin da suke kira zurfafan asiran Shaiɗan, ‘Ba zan ƙara muku wani nauyi ba. 25Sai dai ku riƙe abin da kuke da shi har sai na zo.’

26Gare shi wanda ya ci nasara ya kuma aikata nufina har ƙarshe, zan ba shi iko a kan al’ummai. 27‘Zai yi mulki a kansu da sandar sarauta ta ƙarfe, zai farfashe su, kamar tukwanen yumɓu’2.27 Zab 2.9 kamar yadda na karɓi iko daga Ubana. 28Zan kuma ba shi tauraron asubahi. 29Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.