Ubangiji zai zo yă yi mulki
1Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
2Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
3Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi. 4A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu. 5Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa14.5 Ko kuwa 5 Za a tare kwarin dutsena a kuma miƙe shi har zuwa Azel. Za a tare shi yadda aka tare saboda girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
6A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba. 7Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
8A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku14.8 Wato, Bahar Rum rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum,14.8 Wato, Bahar Maliya a damina da rani.
9Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
10Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki. 11Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
12Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu. 13A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari. 14Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi. 15Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
16Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul. 17In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. 18In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji14.18 Ko kuwa sashe, sai Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba. 19Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
20A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade. 21Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane14.21 Ko kuwa mai ciniki da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.
The Lord Comes and Reigns
1A day of the Lord is coming, Jerusalem, when your possessions will be plundered and divided up within your very walls.
2I will gather all the nations to Jerusalem to fight against it; the city will be captured, the houses ransacked, and the women raped. Half of the city will go into exile, but the rest of the people will not be taken from the city. 3Then the Lord will go out and fight against those nations, as he fights on a day of battle. 4On that day his feet will stand on the Mount of Olives, east of Jerusalem, and the Mount of Olives will be split in two from east to west, forming a great valley, with half of the mountain moving north and half moving south. 5You will flee by my mountain valley, for it will extend to Azel. You will flee as you fled from the earthquake14:5 Or 5 My mountain valley will be blocked and will extend to Azel. It will be blocked as it was blocked because of the earthquake in the days of Uzziah king of Judah. Then the Lord my God will come, and all the holy ones with him.
6On that day there will be neither sunlight nor cold, frosty darkness. 7It will be a unique day—a day known only to the Lord—with no distinction between day and night. When evening comes, there will be light.
8On that day living water will flow out from Jerusalem, half of it east to the Dead Sea and half of it west to the Mediterranean Sea, in summer and in winter.
9The Lord will be king over the whole earth. On that day there will be one Lord, and his name the only name.
10The whole land, from Geba to Rimmon, south of Jerusalem, will become like the Arabah. But Jerusalem will be raised up high from the Benjamin Gate to the site of the First Gate, to the Corner Gate, and from the Tower of Hananel to the royal winepresses, and will remain in its place. 11It will be inhabited; never again will it be destroyed. Jerusalem will be secure.
12This is the plague with which the Lord will strike all the nations that fought against Jerusalem: Their flesh will rot while they are still standing on their feet, their eyes will rot in their sockets, and their tongues will rot in their mouths. 13On that day people will be stricken by the Lord with great panic. They will seize each other by the hand and attack one another. 14Judah too will fight at Jerusalem. The wealth of all the surrounding nations will be collected—great quantities of gold and silver and clothing. 15A similar plague will strike the horses and mules, the camels and donkeys, and all the animals in those camps.
16Then the survivors from all the nations that have attacked Jerusalem will go up year after year to worship the King, the Lord Almighty, and to celebrate the Festival of Tabernacles. 17If any of the peoples of the earth do not go up to Jerusalem to worship the King, the Lord Almighty, they will have no rain. 18If the Egyptian people do not go up and take part, they will have no rain. The Lord14:18 Or part, then the Lord will bring on them the plague he inflicts on the nations that do not go up to celebrate the Festival of Tabernacles. 19This will be the punishment of Egypt and the punishment of all the nations that do not go up to celebrate the Festival of Tabernacles.
20On that day Holy to the Lord will be inscribed on the bells of the horses, and the cooking pots in the Lord’s house will be like the sacred bowls in front of the altar. 21Every pot in Jerusalem and Judah will be holy to the Lord Almighty, and all who come to sacrifice will take some of the pots and cook in them. And on that day there will no longer be a Canaanite14:21 Or merchant in the house of the Lord Almighty.