Yahuda 1 – HCB & CARSA

Hausa Contemporary Bible

Yahuda 1:1-25

1Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub,

Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.

2Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.

Zunubi da hallakar marasa tsoron Allah

3Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak. 4Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.

5Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba. 6Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. 7Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta.

8Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama. 9Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!” 10Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.

11Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.

12Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa ’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus. 13Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada.

14Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa 15don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.” 16Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.

Kira don jimiri

17Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā. 18Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.” 19Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.

20Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki. 21Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami.

22Ku ji tausayin waɗanda suke shakka; 23ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.

Yabo

24To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki. 25Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin.

Священное Писание (Восточный перевод), версия с «Аллахом»

Иуда 1:1-25

Приветствие

1От Иуды, раба Исы аль-Масиха1:1 Аль-Масих (переводится как «Помазанник») – праведный Царь и Освободитель, Спаситель, обещанный Аллахом ещё в Таурате, Забуре и Книге Пророков. Аль (также передаётся в русской транскрипции как эль, الـ‎) — определённый артикль в арабском языке. и брата Якуба, всем призванным и любимым Небесным Отцом и хранимым Исой аль-Масихом.

2Пусть умножатся для вас милость, мир и любовь.

Всех лжеучителей ожидает Суд

3Возлюбленные, при всём моём желании написать вам о нашем общем спасении, я счёл нужным напомнить вам о необходимости отстаивать веру, раз и навсегда доверенную святому народу Аллаха. 4Потому что в вашу среду проникли люди, которые уже давно определены на осуждение. Эти безбожные люди превратили милость нашего Бога в повод продолжать заниматься развратом. Они отвергают нашего единственного Владыку и Повелителя Ису аль-Масиха.

5Хотя вы уже и знаете обо всём этом, я всё же хочу напомнить ещё раз, что Вечный1:5 Вечный – греческим словом «кюриос», стоящим здесь в оригинальном тексте, в Инджиле переведено еврейское «Яхве». А так как в данном издании Священного Писания «Яхве» переведено как «Вечный», то и его греческий эквивалент переведён так же. Под именем «Яхве» Всевышний открылся Мусе и народу Исраила (см. Исх. 3:13-15). См. пояснительный словарь. спас Свой народ из Египта, но тех, кто Ему не поверил, Он погубил1:5 См. Исх. 12:31-41; 13:17-22; 14; Чис. 14:20-38; 1 Кор. 10:1-5.. 6И ангелов, которые не сохранили своего положения и оставили своё жилище, Он содержит в вечных цепях, во тьме, на Суд великого дня. 7Также и жители Содома, Гоморры и окружавших их городов, подобно им предававшиеся разврату и половым извращениям, служат примером, подвергшись наказанию вечным огнём1:7 См. Нач. 19:1-29..

8Так и эти люди, основываясь на своих видениях, оскверняют свои тела, отвергают власть1:8 Это может быть земная власть или власть Аллаха. и злословят небесные силы1:8 Букв.: «славных» – это, по всей вероятности, ангелы.. 9Но даже когда архангел1:9 Архангел – один из высших ангельских чинов. Микаил спорил с Иблисом о теле пророка Мусы, он не позволил себе с оскорблениями осуждать его. Он лишь сказал: «Пусть Вечный запретит тебе». 10Эти же люди клевещут на то, чего не знают, а что они знают от природы, как неразумные животные, тем они себя и разрушают.

11Горе им! Они пошли по пути Каина1:11 Каин – старший сын Адама и Хавы (см. Нач. 4:1-16)., и, гонимые жаждой наживы, повторяют заблуждение Валаама1:11 См. Чис. 22:1-21; 31:16., и в восстании погибают как Корах1:11 См. Чис. 16..

12Такие люди – как подводные рифы1:12 Или: «как тёмные пятна». на ваших ужинах любви1:12 Ужин любви – верующие часто собирались для совместной трапезы, во время которой совершалось хлебопреломление в воспоминание о жертвенной смерти Исы аль-Масиха за наши грехи согласно Его повелению (см. Лк. 22:14-19; 1 Кор. 11:23-26).. Пиршествуя с вами, они бесстыдно заботятся лишь о себе. Это тучи без дождя, носимые ветром, деревья, бесплодные даже осенью, дважды мёртвые, вырванные с корнем. 13Они как свирепые морские волны, пенящиеся своим позором, как блуждающие звёзды, обречённые на вечную беспросветную тьму.

14Енох1:14 Енох – на Востоке также известен как Идрис., потомок Адама в седьмом поколении, пророчествовал о них:

«Вот идёт Повелитель с многими тысячами святых1:14 Святых – включает в себя ангелов Аллаха и, возможно, последователей Исы аль-Масиха, которые к тому времени уже будут с Ним на небесах. Своих. 15Он идёт, чтобы судить всех и обличить всех нечестивцев во всех их нечестивых делах, которые они нечестиво совершили, и во всех ужасных словах, которые сказали против Него нечестивые грешники»1:14-15 Цитата взята из 1 Енох 1:9 – книги, которая была широко известна среди иудеев в I веке..

16Эти люди всегда жалуются и недовольны жизнью. Они идут на поводу у своих низменных желаний, они произносят напыщенные речи и льстят ради выгоды.

Предостережение и наставления

17Но вы, возлюбленные, помните о том, что предсказывали посланники нашего Повелителя Исы аль-Масиха. 18Они говорили вам: «В последнее время появятся наглые люди, идущие на поводу у своих низменных желаний». 19Эти люди производят разделения; они следуют только своим природным инстинктам, а Духа не имеют.

20Но вы, возлюбленные, созидайте себя на своей святейшей вере, молясь под водительством Святого Духа. 21Оставайтесь в любви Аллаха, ожидая милости Повелителя нашего Исы аль-Масиха, дающей вечную жизнь.

22Будьте милостивы к тем, кто колеблется. 23Других спасайте, выхватывая их из огня1:23 См. Зак. 3:2.; к третьим проявляйте милосердие, но будьте осторожны, гнушаясь даже одеждой, осквернённой греховной плотью.

Заключение

24Тому, Кто в силе сохранить вас от падения и ввести в Свою славу радостными и беспорочными, 25единому Богу, Спасителю нашему через Ису аль-Масиха, нашего Повелителя, слава, величие, сила и власть и до начала времени, и сейчас, и во все века! Аминь.