Ruʼuya ta Yohanna 22 – HCB & CARS

Hausa Contemporary Bible

Ruʼuya ta Yohanna 22:1-21

An maido da Eden

1Sai mala’ikan ya nuna mini kogin ruwan rai, mai ƙyalli kamar madubi, yana gangarawa daga kursiyin Allah da na Ɗan Ragon, 2yana bin tsakiyar babban titi na birnin. A kowane gefen kogin akwai itacen rai mai ba da ’ya’ya goma sha biyu, yana ba da ’ya’yansa kowane wata. Ganyayen itacen kuwa saboda warkar da al’ummai ne. 3Ba za a ƙara samun la’ana ba. Kursiyin Allah da na Ɗan Ragon zai kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa hidima. 4Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu. 5Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin.

Yohanna da Mala’ikan

6Mala’ikan ya ce mini, “Waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa, ya aiki mala’ikansa, don yă nuna wa bayinsa abubuwan da za su faru nan ba da daɗewa ba.”

7“Ga shi! Ina zuwa da wuri! Mai albarka ne wanda yake kiyaye kalmomin annabcin da suke cikin wannan littafi.”

8Ni, Yohanna, na ji, na kuma ga abubuwan nan. Kuma sa’ad da na ji, na kuma gan su, sai na fāɗi a ƙasa a gaban mala’ikan da yake nuna mini su, don in yi sujada. 9Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da ’yan’uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye kalmomin wannan littafi. Allah za ka yi wa sujada!”

10Sa’an nan ya gaya mini cewa, “Kada ka rufe kalmomin annabcin littafin nan, domin lokaci ya yi kusa. 11Duk mai yin laifi yă ci gaba da yin laifi; duk mai aikata ƙazanta yă ci gaba da aikata ƙazanta. Duk mai aikata abin da yake daidai, yă ci gaba da aikata abin da yake daidai. Kuma duk wanda yake mai tsarki, yă ci gaba da yin abin da yake da tsarki.”

Maganar ƙarshe. Gayyata da gargaɗi

12“Ga shi, ina zuwa da wuri! Ladan da zan bayar yana tare da ni, kuma zan ba wa kowa gwargwadon abin da ya yi. 13Ni ne Alfa da kuma Omega, na Fari da kuma na Baya, Farko da kuma Ƙarshe.

14“Masu albarka ne waɗanda suka wanke tufafinsu, don su sami izinin ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta ƙofofi. 15Waɗanda suke waje kuwa karnuka ne, masu sihiri, masu fasikanci, masu kisankai, masu bautar gumaka, da duk wanda yake ƙaunar ƙarya yake kuma aikata ta.

16“Ni, Yesu, na aiko mala’ikana ya ba ka wannan shaida saboda ikkilisiyoyi. Ni ne Tushe da kuma Zuriyar Dawuda, da kuma Tauraron Asubahi mai haske.”

17Ruhu da kuma amarya suna cewa, “Zo!” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo!” Duk mai jin ƙishirwa, yă zo; duk mai bukata kuma, yă ɗibi ruwan rai kyauta.

18Ina yin wa duk wanda ya ji kalmomin annabcin wannan littafi gargaɗi. Duk wanda ya ƙara wani abu a kansu, Allah zai ƙara masa annoban da aka bayyana a littafin nan. 19Duk wanda kuma ya yi ragi a kalmomi daga littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai da kuma na birnin nan mai tsarki, waɗanda aka bayyana a littafin nan.

20Shi da ya shaida waɗannan abubuwa ya ce, “I, ina zuwa da wuri.”

Amin. Zo, Ubangiji Yesu!

21Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da mutanen Allah. Amin.

Священное Писание

Откровение 22:1-21

Река жизни

1Затем ангел показал мне реку воды жизни, блестящую, как кристалл, и текущую от трона Всевышнего и Ягнёнка 2посредине центральной улицы города. По обе стороны реки растут деревья жизни. Они плодоносят двенадцать раз в год, давая каждый месяц свой плод, а листья деревьев предназначены для исцеления народов22:2 См. Езек. 47:12; ср. Нач. 2:9-10.. 3И там уже больше не будет ничего проклятого22:3 См. Нач. 3:14-19; ср. Зак. 14:11.. В городе будет находиться трон Всевышнего и Ягнёнка, и Его рабы будут служить Ему. 4Они будут видеть Его лицо22:4 Ср. Исх. 33:20., и на лбу у них будет написано Его имя. 5Ночи больше не будет. Им уже не нужен будет свет ламп или свет солнца, потому что Вечный Бог будет светить над ними. И они будут царствовать вовеки22:5 См. Дан. 7:18, 27..

6Ангел сказал мне:

– Это верные и истинные слова. Вечный Бог, вдохновляющий дух пророков, послал Своего ангела, чтобы показать Своим рабам то, что должно произойти вскоре.

Пришествие Исы Масиха

7– Вот Я скоро приду! Благословен тот, кто соблюдает слова пророчества, записанные в этом свитке.

8Я, Иохан, всё это слышал и видел. И, услышав и увидев, я пал к ногам ангела, показывающего мне всё это, чтобы поклониться ему.

9Но ангел говорит мне:

– Не делай этого! Я такой же раб, как и ты, как твои братья пророки и как те, кто соблюдает слова, записанные в этом свитке. Поклонись Всевышнему!

10Потом он говорит мне:

– Не запечатывай слов пророчества, записанных в этом свитке22:10 Ср. Дан. 12:4, 9., потому что время уже близко. 11Кто поступает несправедливо, тот и будет продолжать поступать несправедливо. Кто ведёт скверную жизнь, тот и будет продолжать вести скверную жизнь. Но тот, кто живёт праведной жизнью, будет продолжать жить праведно, и тот, кто свят, будет продолжать жить свято22:11 См. Дан. 12:10; 2 Тим. 3:13..

12– Вот Я скоро приду! Я несу воздаяние каждому, и каждый получит по своим делам. 13Я – Владыка всего: от А до Я, Первый и Последний22:13 См. Ис. 44:6; 48:12. Здесь Иса говорит о Себе так, как говорил о Себе Сам Всевышний., Начало и Конец. 14Благословенны те, кто омывает свои одежды, чтобы им иметь право питаться от дерева жизни и войти в город через ворота. 15А снаружи останутся псы22:15 Священное Писание часто называет псами тех, кто делает неугодное в глазах Всевышнего (см. Втор. 23:17-18; Заб. 21:17; Флп. 3:2)., колдуны, развратники, убийцы, идолопоклонники и все любящие и творящие неправду.

16Я, Иса, послал Моего ангела, чтобы передать вам это свидетельство для общин верующих. Я – Корень22:16 Или: «Росток». и Потомок Давуда, Я – яркая Утренняя Звезда22:16 См. Чис. 24:17; Ис. 11:1, 10..

17Дух Всевышнего и невеста говорят Исе:

– Приди!

И каждый, кто это слышит, пусть тоже скажет:

– Приди!

Пусть приходит мучимый жаждой! Кто хочет, пусть берёт воду жизни даром!22:17 См. Ис. 55:1; Ин. 7:37.

18И я предупреждаю каждого, кто слышит слова пророчества, записанные в этом свитке: кто добавит что-либо к этим словам, тому Всевышний добавит и бедствия, о которых написано в этом свитке. 19И если кто отнимет что-либо из слов пророчества, записанных в этом свитке, у того и Всевышний отнимет право питаться от дерева жизни и жить в святом городе, которые описаны в этом свитке22:18-19 См. Втор. 4:2; 12:32; Мудр. 30:6..

20Свидетельствующий об этом говорит:

– Да, Я скоро приду!

Да будет так! Приди, Повелитель Иса!

21Пусть благодать Повелителя Исы будет со всеми.

Аминь.