Ruʼuya ta Yohanna 22 – HCB & SNC

Hausa Contemporary Bible

Ruʼuya ta Yohanna 22:1-21

An maido da Eden

1Sai mala’ikan ya nuna mini kogin ruwan rai, mai ƙyalli kamar madubi, yana gangarawa daga kursiyin Allah da na Ɗan Ragon, 2yana bin tsakiyar babban titi na birnin. A kowane gefen kogin akwai itacen rai mai ba da ’ya’ya goma sha biyu, yana ba da ’ya’yansa kowane wata. Ganyayen itacen kuwa saboda warkar da al’ummai ne. 3Ba za a ƙara samun la’ana ba. Kursiyin Allah da na Ɗan Ragon zai kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa hidima. 4Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu. 5Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin.

Yohanna da Mala’ikan

6Mala’ikan ya ce mini, “Waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa, ya aiki mala’ikansa, don yă nuna wa bayinsa abubuwan da za su faru nan ba da daɗewa ba.”

7“Ga shi! Ina zuwa da wuri! Mai albarka ne wanda yake kiyaye kalmomin annabcin da suke cikin wannan littafi.”

8Ni, Yohanna, na ji, na kuma ga abubuwan nan. Kuma sa’ad da na ji, na kuma gan su, sai na fāɗi a ƙasa a gaban mala’ikan da yake nuna mini su, don in yi sujada. 9Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da ’yan’uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye kalmomin wannan littafi. Allah za ka yi wa sujada!”

10Sa’an nan ya gaya mini cewa, “Kada ka rufe kalmomin annabcin littafin nan, domin lokaci ya yi kusa. 11Duk mai yin laifi yă ci gaba da yin laifi; duk mai aikata ƙazanta yă ci gaba da aikata ƙazanta. Duk mai aikata abin da yake daidai, yă ci gaba da aikata abin da yake daidai. Kuma duk wanda yake mai tsarki, yă ci gaba da yin abin da yake da tsarki.”

Maganar ƙarshe. Gayyata da gargaɗi

12“Ga shi, ina zuwa da wuri! Ladan da zan bayar yana tare da ni, kuma zan ba wa kowa gwargwadon abin da ya yi. 13Ni ne Alfa da kuma Omega, na Fari da kuma na Baya, Farko da kuma Ƙarshe.

14“Masu albarka ne waɗanda suka wanke tufafinsu, don su sami izinin ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta ƙofofi. 15Waɗanda suke waje kuwa karnuka ne, masu sihiri, masu fasikanci, masu kisankai, masu bautar gumaka, da duk wanda yake ƙaunar ƙarya yake kuma aikata ta.

16“Ni, Yesu, na aiko mala’ikana ya ba ka wannan shaida saboda ikkilisiyoyi. Ni ne Tushe da kuma Zuriyar Dawuda, da kuma Tauraron Asubahi mai haske.”

17Ruhu da kuma amarya suna cewa, “Zo!” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo!” Duk mai jin ƙishirwa, yă zo; duk mai bukata kuma, yă ɗibi ruwan rai kyauta.

18Ina yin wa duk wanda ya ji kalmomin annabcin wannan littafi gargaɗi. Duk wanda ya ƙara wani abu a kansu, Allah zai ƙara masa annoban da aka bayyana a littafin nan. 19Duk wanda kuma ya yi ragi a kalmomi daga littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai da kuma na birnin nan mai tsarki, waɗanda aka bayyana a littafin nan.

20Shi da ya shaida waɗannan abubuwa ya ce, “I, ina zuwa da wuri.”

Amin. Zo, Ubangiji Yesu!

21Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da mutanen Allah. Amin.

Slovo na cestu

Zjevení Janovo 22:1-21

1I ukázal mi potok čistý vody živé, světlý jako křišťál, tekoucí z trůnu Božího a Beránkova. 2Uprostřed pak rynku jeho a s obou stran potoka bylo dřevo života, přinášející dvanáctero ovoce, na každý měsíc vydávající ovoce své, a listí své k zdraví národů. 3A ničeho zlořečeného již více nebude, ale trůn Boží a Beránkův bude v něm, a služebníci jeho sloužiti jemu budou. 4A tvář jeho viděti budou, a jméno jeho budeť na čelích jejich. 5A noci tam nebude, aniž budou potřebovati svíce, ani světla slunečného; nebo Pán Bůh je osvěcuje, a kralovati budou na věky věků. 6I řekl mi: Slova tato jsouť věrná a pravá, a Pán, jenž jest Bůh svatých proroků, poslal anděla svého, aby ukázal služebníkům svým, co se díti musí brzo. 7Aj, přijduť rychle. Blahoslavený, kdož ostříhá slov proroctví knihy této. 8Já pak Jan viděl jsem a slyšel tyto věci. A když jsem slyšel a viděl, padl jsem, klaněti se chtěje před nohama anděla toho, kterýž mi tyto věci ukazoval. 9Ale řekl mi: Hleď, abys toho nečinil. Neboť jsem spoluslužebník tvůj a bratří tvých proroků, a těch, jenž ostříhají slov knihy této. Bohu se klaněj. 10Potom řekl mi: Nezapečeťuj slov proroctví knihy této; neboť jest blízko čas. 11Kdo škodí, škodiž ještě; a kdo smrdí, smrdiž ještě; a kdo jest spravedlivý, ospravedlniž se ještě; a svatý posvětiž se ještě. 12A aj, přijduť brzo, a odplata má se mnou, abych odplatil jednomu každému podle skutků jeho. 13Jáť jsem Alfa i Omega, počátek i konec, první i poslední. 14Blahoslavení, kteříž zachovávají přikázání jeho, aby měli právo k dřevu života a aby branami vešli do města. 15Vně pak budou psi a čarodějníci, a smilníci, a vražedlníci, a modláři, i každý, kdož miluje a činí lež. 16Já Ježíš poslal jsem anděla svého, aby vám svědčil o těchto věcech v církvích. Já jsem kořen a rod Davidův, a hvězda jasná a jitřní. 17A Duch i nevěsta řkou: Pojď. A kdož slyší, rciž: Přijď. A kdož žízní, přijdiž, a kdo chce, nabeř vody života darmo. 18Osvědčujiť pak každému, kdož by slyšel slova proroctví knihy této, jestliže by kdo přidal k těmto věcem, žeť jemu přidá Bůh ran napsaných v knize této. 19A jestliže by kdo ujal něco od slov proroctví tohoto, odejmeť Bůh díl jeho z knihy života, a z města svatého, a z těch věcí, kteréž jsou napsány v knize této. 20Takť praví ten, kterýž svědectví vydává o těchto věcech: Jistěť přijdu brzo. Amen. Přijdiž tedy, Pane Ježíši. 21Milost Pána našeho Jezukrista se všemi vámi. Amen.