Mattiyu 8 – HCB & BDS

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 8:1-34

Mutum mai kuturta

(Markus 1.40-45; Luka 5.12-16)

1Da ya sauko daga dutsen, sai taron mutane mai yawan gaske suka bi shi. 2Wani mutum mai kuturta ya zo ya durƙusa a gabansa ya ce, “Ubangiji, in kana so, kana iya tsabtacce ni.”

3Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin. Ya ce, “Ina so, ka tsabtacce!” Nan da nan aka warkar8.3 Girik aka tsabtacce da shi daga kuturtarsa. 4Sai Yesu ya ce masa, “Ka lura kada ka gaya wa kowa. Sai dai ka tafi, ka nuna kanka ga firist ka kuma yi bayarwar da Musa ya umarta, a matsayin shaida gare su.”

Bangaskiyar jarumi

(Luka 7.1-10; Yohanna 4.43-54)

5Da Yesu ya shiga Kafarnahum, sai wani jarumi ya zo wurinsa, yana neman taimako. 6Ya ce, “Ubangiji, bawana yana kwance a gida shanyayye, yana kuma shan azaba ƙwarai.”

7Yesu ya ce masa, “Zan je in warkar da shi.”

8Jarumin ya amsa, “Ubangiji, ban cancanci in sa ka zo gidana ba, ka dai yi magana kawai, bawana zai warke. 9Gama ni kaina mutum ne a ƙarƙashin iko, da kuma sojoji a ƙarƙashina. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi; wancan kuma, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan ce wa bawana, ‘Yi wannan,’ sai kuwa yă yi.”

10Da Yesu ya ji wannan, sai ya yi mamaki ya kuma ce wa waɗanda suke binsa, “Gaskiya nake gaya muku, ban taɓa samun wani a Isra’ila da bangaskiya mai girma haka ba. 11Ina kuma gaya muku da yawa za su zo daga gabas da kuma yamma, su ɗauki wuraren zamansu a biki tare da Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub a cikin mulkin sama. 12Amma za a jefar da ’ya’yan mulki waje, zuwa cikin baƙin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”

13Sa’an nan Yesu ya ce wa jarumin, “Je ka! Za a yi bisa ga bangaskiyarka.” A daidai wannan lokaci bawansa kuwa ya warke.

Yesu ya warkar da mutane da yawa

(Markus 1.29-34; Luka 4.38-41)

14Da Yesu ya zo cikin gidan Bitrus, sai ya ga surukar Bitrus tana kwance a gado tana da zazzaɓi. 15Ya taɓa hannunta sai zazzaɓin ya sake ta, ta kuwa tashi ta fara yin masa hidima.

16Da yamma ta yi, aka kawo masa masu aljanu da yawa, ya kuwa fitar da ruhohin ta wurin magana, ya kuma warkar da dukan marasa lafiya. 17Wannan ya faru ne domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa,

“Ya ɗebi rashin lafiyarmu,

ya kuma ɗauki cututtukanmu.”8.17 Ish 53.4

Wahalar bin Yesu

(Luka 9.57-62)

18Da Yesu ya ga taron mutane kewaye da shi, sai ya ba da umarni a ƙetare zuwa ɗayan hayin tafkin. 19Sai wani malamin dokoki ya zo wurinsa ya ce, “Malam, zan bi ka duk inda za ka.”

20Sai Yesu ya amsa ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”

21Sai wani almajiri ya ce masa, “Ubangiji, da farko bari in je in binne mahaifina.”

22Amma Yesu ya ce masa, “Ka bi ni, ka bar matattu su binne matattunsu.”

Yesu ya kwantar da hadari

(Markus 4.35-41; Luka 8.22-25)

23Sai ya shiga jirgin ruwa, almajiransa kuwa suka bi shi. 24Ba zato ba tsammani, sai wani babban hadari ya taso a tafkin, har raƙuman ruwan suka sha kan jirgin. Amma Yesu yana barci. 25Almajiran suka je suka tashe shi, suna cewa, “Ubangiji, ka cece mu! Za mu nutse!”

26Ya amsa ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, me ya sa kuke tsoro haka?” Sa’an nan ya tashi ya tsawata wa iskar da kuma raƙuman ruwan, sai wuri ya yi tsit gaba ɗaya.

27Mutanen suka yi mamaki suka ce, “Wane irin mutum ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa suna masa biyayya!”

Warkar da mutum biyu masu aljanu

(Markus 5.1-20; Luka 8.26-39)

28Da ya isa ɗayan gefen a yankin Gadarenawa8.28 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā suna da Gergesenawa; waɗansu kuma Gerasenawa ne a nan (ko kuwa Gerasenawa), sai ga mutum biyu masu aljanu suna fitowa daga kaburbura suka tarye shi. Su abin tsoro ne ƙwarai, har ba mai iya bin wannan hanya. 29Suka yi ihu suka ce, “Me ya haɗa ka da mu, Ɗan Allah?” Ka zo ne nan don ka ji mana kafin lokaci yă yi?

30Nesa kaɗan da su kuwa akwai babban garken aladu da yake kiwo. 31Aljanun suka roƙi Yesu suka ce, “In ka fitar da mu, tura mu cikin garken aladun nan.”

32Ya ce musu, “Ku tafi!” Sai suka fita suka shiga cikin aladun, dukan garken kuwa ya gangara a guje daga kan tudun zuwa cikin tafkin aladun kuma suka mutu a cikin ruwa. 33Masu kiwon aladun suka ruga, suka je cikin gari suka ba da labarin dukan wannan, haɗe da abin da ya faru da mutanen nan masu aljanu. 34Sai dukan garin suka fito don su taryi Yesu. Da suka kuwa gan shi, sai suka roƙe shi yă bar musu yanki.

La Bible du Semeur

Matthieu 8:1-34

L’Évangile et l’autorité de Jésus

Jésus guérit les malades

(Mc 1.40-45 ; Lc 5.12-16)

1Quand Jésus descendit de la montagne, une foule nombreuse le suivit. 2Et voici qu’un lépreux s’approcha et se prosterna devant lui en disant : Seigneur, si tu le veux, tu peux me rendre pur8.2 C’est-à-dire tu peux me guérir. La lèpre rendait rituellement impur ; demander à être purifié équivalait à demander la guérison..

3Jésus tendit la main et le toucha en disant : Je le veux, sois pur.

Aussitôt, il fut purifié de sa lèpre.

4– Attention, lui dit Jésus, ne le dis à personne ; mais va te faire examiner par le prêtre et apporte l’offrande prescrite par Moïse. Cela leur servira de témoignage8.4 Autres traductions : cela leur prouvera qui je suis ou cela prouvera à tous que tu es guéri ou cela prouvera à tous mon respect de la Loi..

(Lc 7.1-10)

5Jésus entrait à Capernaüm, quand un officier romain l’aborda. 6Il le supplia : Seigneur, mon serviteur est couché chez moi, il est paralysé, il souffre terriblement.

7– Je vais chez toi, lui répondit Jésus, et je le guérirai.

8– Seigneur, dit alors l’officier, je ne remplis pas les conditions8.8 Ou : je ne suis pas digne (voir 3.11). L’officier romain savait sans doute que la tradition ne permettait pas aux Juifs de pénétrer dans la maison d’un non-Juif. pour te recevoir dans ma maison, mais tu n’as qu’un mot à dire et mon serviteur sera guéri. 9Car, moi-même, je suis un officier subalterne, mais j’ai des soldats sous mes ordres, et quand je dis à l’un : « Va ! », il va. Quand je dis à un autre : « Viens ! », il vient. Quand je dis à mon esclave : « Fais ceci ! », il le fait.

10En entendant cela, Jésus fut rempli d’admiration et, s’adressant à ceux qui le suivaient, il dit : Vraiment, je vous l’assure : chez personne, en Israël, je n’ai trouvé une telle foi ! 11Je vous le déclare : beaucoup viendront de l’Orient et de l’Occident et prendront place à table auprès d’Abraham, d’Isaac et de Jacob, dans le royaume des cieux. 12Mais ceux qui devaient hériter du royaume, ceux-là seront jetés dans les ténèbres du dehors. Là, il y aura des pleurs et d’amers regrets.

13Puis Jésus dit à l’officier : Rentre chez toi et qu’il te soit fait selon ce que tu as cru. Et, à l’heure même, son serviteur fut guéri.

Il a porté nos maladies

(Mc 1.29-34 ; Lc 4.38-41)

14Jésus se rendit alors à la maison de Pierre. Il trouva la belle-mère de celui-ci alitée, avec une forte fièvre. 15Il lui prit la main, et la fièvre la quitta. Alors elle se leva et se mit à le servir.

16Le soir venu, on lui amena beaucoup de gens qui étaient sous l’emprise de démons : par sa parole, il chassa ces esprits mauvais. Il guérit aussi tous les malades. 17Ainsi s’accomplissait cette parole du prophète Esaïe :

Il s’est chargé de nos infirmités

et il a porté nos maladies8.17 Es 53.4..

L’engagement total du disciple

(Lc 9.57-62)

18Lorsque Jésus se vit entouré d’une foule nombreuse, il donna ordre à ses disciples de passer de l’autre côté du lac. 19Un spécialiste de la Loi s’approcha et lui dit : Maître, je te suivrai partout où tu iras.

20Jésus lui répondit : Les renards ont des tanières et les oiseaux du ciel des nids ; mais le Fils de l’homme n’a pas d’endroit où reposer sa tête.

21– Seigneur, lui dit un autre qui était de ses disciples, permets-moi d’aller d’abord enterrer mon père.

22Mais Jésus lui répondit : Suis-moi et laisse à ceux qui sont morts le soin d’enterrer leurs morts.

Plus fort que la tempête

(Mc 4.35-41 ; Lc 8.22-25)

23Il monta dans un bateau et ses disciples le suivirent. 24Tout à coup, une grande tempête se leva sur le lac et les vagues passaient par-dessus le bateau. Pendant ce temps, Jésus dormait. 25Les disciples s’approchèrent de lui et le réveillèrent en criant : Seigneur, sauve-nous, nous sommes perdus !

26– Pourquoi avez-vous si peur ? leur dit-il. Votre foi est bien petite !

Alors il se leva, parla sévèrement au vent et au lac, et il se fit un grand calme.

27Saisis d’étonnement, ceux qui étaient présents disaient : Quel est donc cet homme pour que même les vents et le lac lui obéissent ?

Plus fort que les démons

(Mc 5.1-20 ; Lc 8.26-39)

28Quand il fut arrivé de l’autre côté du lac, dans la région de Gadara8.28 Gadara se trouvait en territoire non juif, à 10 kilomètres au sud-est du lac de Galilée., deux hommes qui étaient sous l’emprise de démons sortirent des tombeaux et vinrent à sa rencontre. Ils étaient si dangereux que personne n’osait plus passer par ce chemin. 29Et voici qu’ils se mirent à crier : Que nous veux-tu, Fils de Dieu ? Es-tu venu nous tourmenter avant le temps ?

30Or, il y avait, à quelque distance de là, un grand troupeau de porcs8.30 Le porc était, selon la Loi de Moïse, un animal impur (Lv 11.7). Seuls les non-Juifs élevaient des porcs. en train de paître. 31Les démons supplièrent Jésus : Si tu veux nous chasser, envoie-nous dans ce troupeau de porcs.

32– Allez ! leur dit-il.

Les démons sortirent de ces deux hommes et entrèrent dans les porcs. Aussitôt, tout le troupeau s’élança du haut de la pente et se précipita dans le lac, et toutes les bêtes périrent noyées.

33Les gardiens du troupeau s’enfuirent, coururent à la ville et allèrent raconter tout ce qui s’était passé, en particulier ce qui était arrivé aux deux hommes qui étaient sous l’emprise de démons. 34Là-dessus, tous les habitants de la ville sortirent à la rencontre de Jésus et, quand ils le virent, le supplièrent de quitter leur territoire.