Mattiyu 11 – HCB & NIRV

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 11:1-30

Yesu da Yohanna Mai Baftisma

(Luka 7.18-35)

1Bayan Yesu ya gama yi wa almajiransa sha biyun nan umarni, sai ya yi gaba daga can don yă koyar yă kuma yi wa’azi a garuruwan Galili.11.1 Da Girik a cikin garuruwansu

2Sa’ad da Yohanna Mai Baftisma ya ji a kurkuku abin da Kiristi yake yi, sai ya aiki almajiransa 3su tambaye shi, “Kai ne wanda zai zo, ko kuwa mu sa ido ga wani?”

4Yesu ya amsa ya ce, “Ku koma ku gaya wa Yohanna abin da kuka ji, kuka kuma gani. 5Makafi suna gani, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin labari mai daɗi. 6Mai albarka ne mutumin da bai yi tuntuɓe ba saboda ni.”

7Sa’ad da almajiran Yohanna suke barin wurin, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna. “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne? 8In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da riguna masu kyau ne? A’a, masu sa riguna masu kyau, ai, a fadan sarakuna suke. 9To, me kuka je kallo ne? Annabi? I, ina gaya muku, ya ma fi annabi. 10Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa,

“ ‘Zan aiki ɗan saƙona yă sha gabanka,

wanda zai shirya hanyarka a gabanka.’11.10 Mal 3.1

11Gaskiya nake gaya muku. A cikin dukan waɗanda mata suka haifa, ba wani da ya taso da ya fi Yohanna Mai Baftisma girma; duk da haka mafi ƙanƙanta a mulkin sama ya fi shi girma. 12Tun daga kwanakin Yohanna Mai Baftisma har yă zuwa yanzu, mulkin sama yana sha da ƙyar, fitanannu kuma sun kama mulkin sama sun riƙe gam. 13Gama dukan Annabawa da kuma Doka sun yi ta annabci har yă zuwa kan Yohanna. 14In kuna niyya ku yarda da wannan, to, shi ne Iliya da dā ma zai zo. 15Duk mai kunnen ji, yă ji.

16“Da me zan kwatanta wannan zamani? Suna kama da yara da suke zaune a kasuwa, suna kiran juna, suna cewa,

17“ ‘Mun yi muku busa,

ba ku kuwa yi rawa ba,

mun rera waƙar makoki,

ba ku kuwa yi makoki ba.’

18Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo ba ya ciye-ciye, ba ya shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ai, yana da aljani.’ 19Ɗan Mutum ya zo yana ciye-ciye, yana shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ga mai haɗama da kuma mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’ Amma akan tabbatar da hikima ta wurin ayyukanta.”

Kaiton biranen da ba su tuba ba

(Luka 7.18-35)

20Sai Yesu ya fara yin tir da biranen da aka yi yawancin ayyukansa na banmamaki, don ba su tuba ba. 21“Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida! Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne aka yi a Taya da Sidon, da tuni sun tuba sanye da rigar makoki da toka. 22Amma ina gaya muku, za a fi jin tausayin Taya da Sidon a ranar shari’a, fiye da ku. 23Ke kuma Kafarnahum, za a ɗaga ki sama ne? A’a, za ki gangara zuwa zurfafa ne. Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne a aka yi a Sodom, da tana nan har yă zuwa yau. 24Amma ina gaya miki, za a fi jin tausayin Sodom fiye da ke a ranar shari’a.”

Hutu domin waɗanda suka gaji

(Luka 10.13-15)

25A wannan lokaci sai Yesu ya ce, “Ina yabonka, Uba, Ubangijin sama da ƙasa, gama ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. 26I, Uba, gama wannan shi ne abin da ka ji daɗin yi.

27“Dukan kome Ubana ya danƙa mini. Ba wanda ya san Ɗan sai dai Uban, ba kuma wanda ya san Uban, sai dai Ɗan da kuma waɗanda Ɗan ya so yă bayyana musu shi.

28“Ku zo gare ni, dukanku da kuka gaji kuke kuma fama da kaya, zan kuwa ba ku hutu. 29Ku ɗauki karkiyata a kanku, ku kuma yi koyi da ni, gama ni mai tawali’u ne marar girman kai, za ku kuwa sami hutu don rayukanku. 30Gama karkiyata mai sauƙi ce, kayana kuma marasa nauyi ne.”

New International Reader’s Version

Matthew 11:1-30

Jesus and John the Baptist

1Jesus finished teaching his 12 disciples. Then he went on to teach and preach in the towns of Galilee.

2John the Baptist was in prison. When he heard about the actions of the Messiah, he sent his disciples to him. 3They asked Jesus, “Are you the one who is supposed to come? Or should we look for someone else?”

4Jesus replied, “Go back to John. Report to him what you hear and see. 5Blind people receive sight. Disabled people walk. Those who have skin diseases are made ‘clean.’ Deaf people hear. Those who are dead are raised to life. And the good news is preached to those who are poor. 6Blessed is anyone who does not give up their faith because of me.”

7As John’s disciples were leaving, Jesus began to speak to the crowd about John. He said, “What did you go out into the desert to see? Tall grass waving in the wind? 8If not, what did you go out to see? A man dressed in fine clothes? No. People who wear fine clothes are in kings’ palaces. 9Then what did you go out to see? A prophet? Yes, I tell you, and more than a prophet. 10He is the one written about in Scripture. It says,

“ ‘I will send my messenger ahead of you.

He will prepare your way for you.’ (Malachi 3:1)

11What I’m about to tell you is true. No one more important than John the Baptist has ever been born. But the least important person in the kingdom of heaven is more important than he is. 12Since the days of John the Baptist, the kingdom of heaven has been under attack. And violent people are taking hold of it. 13All the Prophets and the Law prophesied until John came. 14If you are willing to accept it, John is the Elijah who was supposed to come. 15Whoever has ears should listen.

16“What can I compare today’s people to? They are like children sitting in the markets and calling out to others. They say,

17“ ‘We played the flute for you.

But you didn’t dance.

We sang a funeral song.

But you didn’t become sad.’

18When John came, he didn’t eat or drink as you do. And people say, ‘He has a demon.’ 19But when the Son of Man came, he ate and drank as you do. And people say, ‘This fellow is always eating and drinking far too much. He’s a friend of tax collectors and “sinners.” ’ By wise actions wisdom is shown to be right.”

Towns That Do Not Turn Away From Sin

20Jesus began to speak against the towns where he had done most of his miracles. The people there had not turned away from their sins. So he said, 21“How terrible it will be for you, Chorazin! How terrible for you, Bethsaida! Suppose the miracles done in you had been done in Tyre and Sidon. They would have turned away from their sins long ago. They would have put on clothes for mourning. They would have sat down in ashes. 22But I tell you this. On judgment day it will be easier for Tyre and Sidon than for you. 23And what about you, Capernaum? Will you be lifted to the heavens? No! You will go down to the place of the dead. Suppose the miracles done in you had been done in Sodom. It would still be here today. 24But I tell you this. On judgment day it will be easier for Sodom than for you.”

Rest for All Who Are Tired

25At that time Jesus said, “I praise you, Father. You are Lord of heaven and earth. You have hidden these things from wise and educated people. But you have shown them to little children. 26Yes, Father. This is what you wanted to do.

27“My Father has given all things to me. The Father is the only one who knows the Son. And the only ones who know the Father are the Son and those to whom the Son chooses to make him known.

28“Come to me, all you who are tired and are carrying heavy loads. I will give you rest. 29Become my servants and learn from me. I am gentle and free of pride. You will find rest for your souls. 30Serving me is easy, and my load is light.”