Mattiyu 1 – HCB & CRO

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 1:1-25

Asalin Yesu Kiristi

(Luka 3.23-38)

1Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.

2Ibrahim ya haifi Ishaku,

Ishaku ya haifi Yaƙub,

Yaƙub ya haifi Yahuda da ’yan’uwansa,

3Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu;

Ferez ya haifi Hezron,

Hezron ya haifi Ram,

4Ram ya haifi Amminadab,

Amminadab ya haifi Nashon,

Nashon ya haifi Salmon,

5Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa,

Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa,

Obed ya haifi Yesse,

6Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda.

Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.

7Solomon ya haifi Rehobowam,

Rehobowam ya haifi Abiya,

Abiya ya haifi Asa,

8Asa ya haifi Yehoshafat,

Yehoshafat ya haifi Yehoram,

Yehoram ya haifi Azariya,

9Azariya ya haifi Yotam,

Yotam ya haifi Ahaz,

Ahaz ya haifi Hezekiya,

10Hezekiya ya haifi Manasse,

Manasse ya haifi Amon,

Amon ya haifi Yosiya,

11Yosiya kuma ya haifi Yekoniya1.11 Wato, Jehohiyachin; haka ma a aya 12 da ’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.

12Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon.

Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel,

Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,

13Zerubbabel ya haifi Abiyud,

Abiyud ya haifi Eliyakim,

Eliyakim ya haifi Azor,

14Azor ya haifi Zadok,

Zadok ya haifi Akim,

Akim kuma ya haifi Eliyud,

15Eliyud ya haifi Eleyazar,

Eleyazar ya haifi Mattan,

Mattan ya haifi Yaƙub,

16Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.

17Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.1.17 Ko kuwa Kiristi. Kiristi (Da Girik) Almasihu (Da Ibraniyanci) duk suna nufin “Shafaffe.”

Haihuwar Yesu Kiristi

(Luka 2.1-7)

18Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki. 19Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.

20Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne. 21Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu,1.21 Yesu da Girik shi ne Yoshuwa da Ibraniyanci, wanda yake nufin Ubangiji yana ceto. gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”

22Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa, 23“Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel”1.23 Ish 7.14 (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).

24Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa. 25Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.

Knijga O Kristu

Matej 1:1-25

Isusovi preci

(Lk 3:23-38)

1Ovo je rodoslovlje Isusa Krista, potomka kralja Davida koji je bio Abrahamov potomak.

2Abrahamu se rodio Izak.

Izaku se rodio Jakov.

Jakovu su se rodili Juda i njegova braća.

3Judi je Tamara rodila Peresa i Zeraha.

Peresu se rodio Hesron,

a Hesronu Ram.

4Ramu se rodi Aminadab.

Aminadabu se rodi Nahšon,

a Nahšonu Salma.

5Salmi je Rahaba rodila Boaza.

Boazu je Ruta rodila Obeda.

Obedu se rodio Jišaj.

6Jišaju se rodio kralj David.

Davidu je bivša Urijina žena rodila Salomona.

7Salomonu se rodio Roboam.

Roboamu se rodio Abija.

Abiji se rodio Asa.

8Asi se rodio Jozafat.

Jozafatu se rodio Joram,

a Joramu Ahazja.

9Ahazji se rodio Jotam,

Jotamu Ahaz,

a Ahazu Ezekija.

10Ezekiji se rodio Manaše,

Manašeu Amon.

Amonu se rodio Jošija.

11Jošiji su se, u vrijeme progonstva u Babilon, rodili Jehonija i njegova braća.

12Poslije progonstva u Babilon

Jehoniji se rodio Šealtiel.

Šealtielu se rodio Zerubabel.

13Zerubabelu se rodio Abiud.

Abiudu se rodio Elijakim,

a Elijakimu Azor.

14Azoru se rodio Sadok.

Sadoku se rodio Akim,

a Akimu Elijud.

15Elijudu se rodio Eleazar.

Eleazaru Matan,

a Matanu Jakov.

16Jakovu se rodio Josip, muž Marije koja je rodila Isusa zvanoga Krist.

17To je, dakle, ukupno četrnaest naraštaja od Abrahama do kralja Davida, četrnaest naraštaja od kralja Davida do progonstva u Babilon i četrnaest naraštaja od progonstva do Krista.

Rođenje Isusa Krista

(Lk 1:26—2:20)

18Evo kako se zbilo rođenje Isusa Krista: Njegova majka Marija bila je zaručena s Josipom. Ali dok je još bila djevica, začela je po Svetome Duhu. 19Kako je njezin muž Josip bio pravedan čovjek i kako ju nije htio javno osramotiti, naumi ju potajice napustiti.

20Razmišljajući o tome, zaspao je te mu se u snu ukaže Božji glasnik. “Josipe, sine Davidov,” reče mu on, “ne oklijevaj uzeti Mariju za ženu! Jer dijete koje nosi začeto je po Svetome Duhu. 21Ona će roditi sina i nazvat ćeš ga Isus (što znači: ‘Gospodin spasava’) jer će spasiti svoj narod od njegovih grijeha.” 22Sve se to dogodilo da bi se obistinilo što je Gospodin rekao po proroku:

23“Slušajte! Djevica će zanijeti!

Rodit će sina koji će se zvati Emanuel”,

(što znači: “Bog je s nama”).

24Kad se Josip probudio, učini kako mu je Božji glasnik zapovjedio—dovede Mariju svojoj kući da mu bude žena. 25Nije joj prišao kao muškarac dok nije rodila sina. A onda mu nadjene ime Isus.