Markus 16 – HCB & CARS

Hausa Contemporary Bible

Markus 16:1-20

Tashin Yesu daga matattu

(Mattiyu 28.1-8; Luka 24.1-12; Yohanna 20.1-10)

1Da Asabbaci ya wuce, sai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub, da kuma Salome suka sayi kayan ƙanshi domin su je su shafa wa jikin Yesu. 2A ranar farko ta mako, da sassafe, bayan fitowar rana, suna kan hanyarsu zuwa kabarin ke nan, 3sai suka tambaye juna suka ce, “Wane ne zai gungura mana dutsen daga bakin kabarin?”

4Amma da suka ɗaga kai, sai suka ga cewa, an riga an gungura dutsen. Dutsen kuwa babba ne. 5Da suna shiga cikin kabarin, sai suka ga wani saurayi sanye da farar riga, yana zaune a hannun dama, sai suka firgita.

6Ya ce, “Kada ku firgita. Kuna neman Yesu Banazare wanda aka gicciye ne. Ya tashi! Ba ya nan. Ku dubi inda aka kwantar da shi. 7Amma ku tafi ku gaya wa almajiransa da kuma Bitrus cewa, ‘Ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi, kamar yadda ya faɗa muku.’ ”

8Da rawan jiki da kuma ruɗewa, matan suka fita a guje daga kabarin. Ba su kuwa gaya wa kowa ba, don suna tsoro.

[Waɗansu rubuce-rubucen hannu na farko-farko da waɗansu shaidu na dā ba su da ayoyi 9-20.]

9Da Yesu ya tashi daga matattu da safe, a ranar farko ta mako, ya fara bayyana ga Maryamu Magdalin, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta. 10Ta je ta gaya wa waɗanda dā suke tare da shi, waɗanda kuma suke makoki da kuka. 11Da suka ji cewa Yesu yana da rai, har ma ta gan shi, ba su gaskata ba.

(Luka 24.13-35)

12Daga baya Yesu ya bayyana a wani kamanni dabam ga biyunsu, yayinda suke tafiya ƙauye. 13Waɗannan kuwa suka koma suka shaida wa sauran, amma su ma ba su gaskata ba.

14Bayan haka, Yesu ya bayyana ga Sha Ɗayan, yayinda suke cin abinci. Ya tsawata musu a kan rashin bangaskiyarsu, da yadda suka ƙi gaskata waɗanda suka gan shi bayan ya tashi.

15Ya ce, musu, “Ku tafi cikin dukan duniya, ku yi wa’azin bishara ga dukan halitta. 16Duk wanda ya gaskata, aka kuma yi masa baftisma, zai sami ceto. Amma duk wanda bai gaskata ba kuwa, zai hallaka. 17Waɗannan alamu za su kasance tare da waɗanda suka gaskata. A cikin sunana za su fitar da aljanu, za su yi magana da sababbin harsuna. 18Za su ɗauki macizai da hannuwansu. In kuwa suka sha mugun dafi, ba zai cuce su ba ko kaɗan. Za su ɗibiya hannuwansu a kan marasa lafiya, su kuwa warke.”

19Bayan Ubangiji Yesu ya yi musu magana, sai aka ɗauke shi zuwa sama, ya kuma zauna a hannun dama na Allah. 20Sai almajiran suka fita, suka yi wa’azi ko’ina. Ubangiji kuwa ya yi aiki tare da su, ya tabbatar da maganarsa ta wurin alamu da suke biye da maganar.

Central Asian Russian Scriptures

Марк 16:1-20

Воскресение Исы Масиха

(Мат. 28:1‒8; Лк. 24:1‒12; Ин. 20:1‒18)

1Поздно вечером, по окончании религиозного дня отдыха16:1 Букв.: «когда прошла суббота». Суббота, религиозный день отдыха иудеев, начавшись поздно вечером предыдущего дня, завершалась с закатом солнца., Марьям из Магдалы, Марьям, мать Якуба, и Саломия купили душистые мази, чтобы назавтра пойти и помазать тело Исы. 2Рано утром в первый день недели16:2 У иудеев неделя начиналась с воскресенья., едва лишь взошло солнце, они пришли к могильной пещере. 3По дороге они говорили друг другу:

— Кто же откатит нам камень от входа в пещеру?

4Но когда они пришли, то увидели, что камень уже отвален, а он был очень большим. 5Они вошли в могильную пещеру и увидели юношу, одетого в белое, он сидел справа от входа. Женщины испугались. 6А он сказал им:

— Не бойтесь. Вы ищете распятого Ису из Назарета? Он воскрес! Его здесь нет. Посмотрите на место, где Его положили. 7Идите и скажите Его ученикам, включая Петира, что Он встретит вас в Галилее. Там вы Его увидите, как Он вам и говорил.

8Женщины вышли и побежали от могильной пещеры, испуганные и изумлённые. Они ничего никому не сказали, так сильно они испугались.

Явление Исы Масиха ученикам

9Воскреснув рано утром в первый день недели, Иса явился сначала Марьям из Магдалы, из которой Он когда-то изгнал семь демонов. 10Она пошла и сообщила Его ученикам, горевавшим и плакавшим. 11Когда они услышали, что Иса жив и что Марьям видела Его, они не поверили.

12Потом Иса явился в другом облике двоим из них, когда те шли из города. 13Эти двое возвратились и рассказали остальным, но и им не поверили. 14Позже Иса явился одиннадцати ученикам, когда те возлежали за столом. Он упрекнул их за неверие и упрямство, потому что они не поверили тем, кто видел Его воскресшим.

Великое поручение и вознесение Исы Масиха

15Он сказал им:

— Идите по всему миру и возвещайте Радостную Весть всем людям. 16Тот, кто поверит и пройдёт обряд погружения в воду16:16 Или: «обряд омовения»., будет спасён, а тот, кто не поверит, будет осуждён. 17Уверовавших будут сопровождать знамения: они будут Моим именем изгонять нечистых духов, говорить на новых языках; 18они будут брать в руки змей, и если даже выпьют смертельную отраву, это не повредит им; они будут возлагать руки на больных, и те будут выздоравливать.

19Когда Повелитель Иса сказал им всё это, Он вознёсся на небеса и сел по правую руку от Всевышнего16:19 См. Заб. 109:1.. 20А ученики пошли и повсюду проповедовали, и Повелитель содействовал им, подтверждая их слово знамениями16:20 В древнейших рукописях ст. 9‒20 отсутствуют..