Haihuwar Yesu
(Mattiyu 1.18-25)
1A waɗancan kwanaki, Kaisar Augustus ya ba da doka cewa ya kamata a yi ƙidaya a dukan masarautar Roma. 2(Wannan ce ƙidaya ta fari da aka yi a lokacin da Kwiriniyus yake gwamnar Suriya.) 3Sai kowa ya koma garinsa don a rubuta shi.
4Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne. 5Ya tafi can don a rubuta shi tare da Maryamu, wadda aka yi masa alkawari zai aura, tana kuwa da ciki. 6Yayinda suke can, sai lokacin haihuwar jaririn ya yi, 7ta kuwa haifi ɗanta na fari. Ta nannaɗe shi a zane ta kuma kwantar da shi cikin wani kwami, don ba su sami ɗaki a masauƙi ba.
Makiyaya da Mala’iku
8Akwai makiyaya masu zama a fili kusa da wurin, suna tsaron garkunan tumakinsu da dare. 9Sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, suka kuwa tsorata ƙwarai. 10Amma mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Na kawo muku labari mai daɗi na farin ciki mai yawa ne wanda zai zama domin dukan mutane. 11Yau a birnin Dawuda an haifa muku Mai Ceto; shi ne Kiristi Ubangiji. 12Wannan zai zama alama a gare ku. Za ku tarar da jariri a nannaɗe a zane kwance a kwami.”
13Ba labari sai ga taron rundunar sama suka bayyana tare da mala’ikan, suna yabon Allah suna cewa,
14“Ɗaukaka ga Allah a can cikin sama,
a duniya kuma salama ga mutane waɗanda tagomashinsa yake bisansu.”
15Da mala’ikun suka bar su, su suka koma sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu je Betlehem mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar mana.”
16Sai suka tafi da sauri, suka tarar da Maryamu da Yusuf, da kuma jaririn kwance a kwami. 17Sa’ad da suka gan shi, sai suka baza maganar da aka gaya musu game da yaron, 18duk kuwa waɗanda suka ji wannan, suka yi mamaki a kan abin da makiyayan suka faɗa. 19Amma Maryamu ta riƙe dukan waɗannan abubuwa ta kuma yi ta tunaninsu a zuciyarta. 20Makiyayan kuwa suka koma, suna ɗaukaka suna kuma yabon Allah saboda dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.
Miƙa Yesu a haikali
21A rana ta takwas, da lokaci ya yi da za a yi masa kaciya, sai aka ba shi suna Yesu, sunan da mala’ika ya ba shi kafin a yi cikinsa.
22Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji 23(yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji”2.23 Fit 13.2,12), 24don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko ’yan tattabarai biyu.”2.24 Fir 12.8
25To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi. 26An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji. 27Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci, 28sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
29“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari,
yanzu ka sallami bawanka lafiya.
30Gama idanuna sun ga cetonka,
31wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
32haske don bayyanawa ga Al’ummai
da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”
33Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi. 34Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba, 35ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”
36Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure, 37ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu.2.37 Ko kuwa gwauruwa na shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a. 38Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.
39Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu. 40Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.
Yesu a haikali
41Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa. 42Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada. 43Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba. 44Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin ’yan’uwansu da abokansu. 45Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa. 46Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi. 47Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa. 48Da iyayensa suka gan shi sai suka yi mamaki. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, don me ka yi mana haka? Ni da mahaifinka duk mun damu muna nemanka.”
49Sai ya ce, “Don me kuke nemana? Ba ku san cewa, dole in kasance a gidan Ubana ba?” 50Amma ba su fahimci abin da yake faɗin musu ba.
51Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta. 52Yesu kuwa ya yi girma, ya kuma ƙaru cikin hikima, ya kuma sami tagomashi a wurin Allah da mutane.
Рождение Исы Масиха
1В те дни император Август2:1 Август был римским императором с 27 г. до н. э. до 14 г. н. э. издал указ о проведении переписи по всей Римской империи. 2Это была первая перепись, она проводилась в то время, когда Сирией управлял Квириний2:2 Квириний, вероятно, был римским чиновником или полководцем, который проводил эту первую перепись в Сирии, длившуюся с 11 по 4 гг. до н. э., а во время второй переписи с 6 по 9 гг. н. э. он был римским наместником.. 3Поэтому каждый отправился в свой город для регистрации. 4Юсуф тоже пошёл из галилейского города Назарета в Иудею, в город Давуда, называемый Вифлеем, потому что он был потомком царя Давуда. 5Он отправился на перепись вместе с Марьям, которая была с ним обручена и ожидала ребёнка. 6В Вифлееме у Марьям подошло время родов, 7и она родила своего первенца, запеленала Его и положила в кормушку для скота, потому что для них не нашлось места в гостинице2:7 Или: «в комнате для гостей»..
Ангелы возвещают пастухам радостную весть
8Неподалёку были пастухи, которые жили в поле и стерегли ночью своё стадо. 9Вдруг перед ними предстал ангел от Вечного, окружённый сиянием славы Вечного. Пастухи очень испугались, 10но ангел сказал им:
— Не бойтесь. Я пришёл сообщить вам весть, что принесёт великую радость всему народу! 11Сегодня в городе Давуда родился ваш Спаситель2:11 Спаситель— ср. Ис. 43:11; Ос. 13:4. — Масих2:11 Масих (переводится как ‘Помазанник’) — праведный Царь и Освободитель, Спаситель, обещанный Всевышним ещё в Таурате, Забуре и Книге Пророков., Повелитель! 12Вот вам знак: вы найдёте младенца, запелёнатого и лежащего в кормушке.
13И вдруг к ангелу присоединилось многочисленное небесное воинство, славившее Всевышнего и восклицавшее:
14— Хвала Всевышнему в вышине небес!
А на земле мир тем людям, к которым Он благоволит!
15Когда ангелы вернулись на небеса, пастухи сказали друг другу:
— Пойдём в Вифлеем и посмотрим, что там произошло, о чём это нам объявил Вечный?
16Они поспешили туда и нашли Марьям, Юсуфа и младенца, лежащего в кормушке для скота. 17Когда они Его увидели, то рассказали всё, что им было сказано об этом младенце. 18Все, кто слушал, удивлялись рассказу пастухов, 19а Марьям всё запоминала и размышляла об этом. 20Пастухи возвратились, прославляя и восхваляя Всевышнего за всё, что они видели и слышали: всё оказалось точно так, как им и было сказано.
Обрезание, наречение имени и посвящение Исы Масиха Всевышнему
21На восьмой день, когда пришло время совершить над Ним обряд обрезания, Его назвали Иса — имя, которое ангел дал Ему ещё до того, как Он был зачат. 22Когда закончилось время очищения, предписанное Законом Мусы2:22 По Закону очищение женщины завершалось на сороковой день после рождения сына (см. Лев. 12:2‒8)., Марьям и Юсуф понесли младенца в Иерусалим, чтобы посвятить Его Вечному, 23потому что в Законе Вечного написано: «Каждый первенец мужского пола должен быть посвящён Вечному»2:23 См. Исх. 13:2, 12, 15.. 24Они должны были также по Закону Вечного принести в жертву пару горлиц или двух молодых голубей2:24 См. Лев. 12:6‒8..
Благословение и пророчество Шимона
25В Иерусалиме в это время был человек, которого звали Шимон. Он был праведен и благочестив и с надеждой ожидал Того, Кто принесёт утешение для Исраила, и на нём был Святой Дух. 26Святой Дух открыл ему, что он не умрёт, пока не увидит Масиха, посланного Вечным. 27Ведомый Святым Духом, Шимон пришёл в храм, и когда родители принесли младенца Ису, чтобы совершить над Ним то, что было установлено Законом, 28Шимон взял Его на руки и прославил Всевышнего, сказав:
29— Владыка! Теперь, как Ты и обещал,
Ты отпускаешь Своего раба с миром,
30потому что мои глаза увидели спасение Твоё,
31которое Ты приготовил перед лицом всех народов,
32свет откровения язычникам
и славу народа Твоего, Исраила!2:32 См. Ис. 42:6; 49:6.
33Отец и мать удивлялись тому, что было сказано об Исе. 34Потом Шимон благословил их и сказал Марьям, матери ребёнка:
— Это дитя будет причиной падения и возвышения для многих в Исраиле и станет знамением от Всевышнего, которое будет многими отвергаемо, — 35да и тебе самой меч пронзит душу. Через всё это откроются тайные мысли многих людей.
36Там находилась также пророчица Ханна, дочь Пануила, из рода Ашира. Она была в глубокой старости. Ханна прожила семь лет со своим мужем, 37а всю остальную жизнь она жила вдовой. Ей было восемьдесят четыре года2:37 Или: «Она была вдовой восемьдесят четыре года».. Она никогда не покидала храма, день и ночь служа Всевышнему постами и молитвами. 38Подойдя в этот момент к тем, кто принёс младенца, она возблагодарила Всевышнего и говорила о ребёнке всем ожидавшим избавления для Иерусалима.
39Когда родители Исы сделали всё, что предписывал Закон Вечного, они возвратились в Галилею, в свой родной город Назарет. 40Ребёнок рос и набирался сил и мудрости, и Всевышний был благосклонен к Нему.
Двенадцатилетний Иса в храме
41Каждый год на праздник Освобождения2:41 Праздник Освобождения— этот праздник отмечался исключительно в Иерусалиме в память об избавлении иудейского народа под руководством пророка Мусы из Египетского рабства (см. Исх. 12; 13:17‒22; 14; Втор. 16:1‒8). родители Исы ходили в Иерусалим. 42Когда Ему было двенадцать лет, они, как обычно, пошли на праздник. 43После окончания праздника, когда все возвращались домой, мальчик Иса остался в Иерусалиме, но Его родители об этом не знали. 44Полагая, что Он идёт среди других путников, они после целого дня пути стали искать Его среди родственников и знакомых. 45Не найдя, они возвратились в Иерусалим, чтобы искать там. 46Через три дня они нашли мальчика в храме. Он сидел среди учителей, слушал их и задавал вопросы. 47Все, кто Его слышал, поражались Его пониманию и Его ответам. 48Родители были изумлены, увидев Его там.
— Сынок, почему Ты так с нами поступил? — спросила Его мать. — Твой отец и я беспокоились и искали Тебя.
49— Зачем же вы Меня искали? — спросил Он. — Разве вы не знали, что Я должен быть в доме Отца Моего?
50Но они не поняли, о чём Он им говорил. 51Он возвратился с ними в Назарет и был послушен им. Но всё происшедшее Его мать хранила в своей памяти.
52Иса взрослел и становился мудрее. Его любили и люди, и Всевышний2:52 Ср. 1 Цар. 2:26..