Ibraniyawa 1 – HCB & NVI-PT

Hausa Contemporary Bible

Ibraniyawa 1:1-14

1A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri, 2amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. 3Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama. 4Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.

Ɗan ya fi Mala’iku

5Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa,

“Kai Ɗana ne;

yau na zama Uba a gare ka”1.5 Zab 2.7?

Ko kuwa,

“Zan zama Ubansa,

shi kuma zai zama Ɗana”1.5 2Sam 7.14; 1Tar 17.13?

6Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce,

“Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”

7Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce,

“Ya mai da mala’ikunsa iska,

bayinsa kuma harsunan wuta.”1.7 Zab 104.4

8Amma game da Ɗan ya ce,

“Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin,

adalci kuma zai zama sandan mulkinka.

9Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta;

saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka,

ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”1.9 Zab 45.6,7

10Ya kuma ce,

“Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya,

sammai kuma aikin hannuwanka ne.

11Su za su hallaka, amma kai kana nan;

dukansu za su tsufa kamar riga.

12Za ka naɗe su kamar mayafi,

kamar riga za su sauya.

Amma kai ba za ka canja ba,

shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”1.12 Zab 102.25-27

13Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa,

“Zauna a hannun damana,

sai na sa abokan gābanka

su zama matashin sawunka”1.13 Zab 110.1?

14Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?

Nova Versão Internacional

Hebreus 1:1-14

O Filho é Superior aos Anjos

1Há muito tempo Deus falou muitas vezes e de várias maneiras aos nossos antepassados por meio dos profetas, 2mas nestes últimos dias falou-nos por meio do Filho, a quem constituiu herdeiro de todas as coisas e por meio de quem fez o universo. 3O Filho é o resplendor da glória de Deus e a expressão exata do seu ser, sustentando todas as coisas por sua palavra poderosa. Depois de ter realizado a purificação dos pecados, ele se assentou à direita da Majestade nas alturas, 4tornando-se tão superior aos anjos quanto o nome que herdou é superior ao deles.

5Pois a qual dos anjos Deus alguma vez disse:

“Tu és meu Filho;

eu hoje te gerei”1.5 Sl 2.7?

E outra vez:

“Eu serei seu Pai,

e ele será meu Filho”1.5 2Sm 7.14; 1Cr 17.13?

6E ainda, quando Deus introduz o Primogênito no mundo, diz:

“Todos os anjos de Deus o adorem”1.6 Dt 32.43 (segundo a Septuaginta e os manuscritos do mar Morto)..

7Quanto aos anjos, ele diz:

“Ele faz dos seus anjos ventos,

e dos seus servos, clarões reluzentes”1.7 Sl 104.4.

8Mas a respeito do Filho, diz:

“O teu trono, ó Deus, subsiste para todo o sempre;

cetro de equidade é o cetro do teu Reino.

9Amas a justiça e odeias a iniquidade;

por isso Deus, o teu Deus,

escolheu-te dentre os teus companheiros,

ungindo-te com óleo de alegria”1.8,9 Sl 45.6,7.

10E também diz:

“No princípio, Senhor, firmaste os fundamentos da terra,

e os céus são obras das tuas mãos.

11Eles perecerão, mas tu permanecerás;

envelhecerão como vestimentas.

12Tu os enrolarás como um manto,

como roupas eles serão trocados.

Mas tu permaneces o mesmo,

e os teus dias jamais terão fim”1.10-12 Sl 102.25-27.

13A qual dos anjos Deus alguma vez disse:

“Senta-te à minha direita,

até que eu faça dos teus inimigos

um estrado para os teus pés”1.13 Sl 110.1?

14Os anjos não são, todos eles, espíritos ministradores enviados para servir aqueles que hão de herdar a salvação?