Mattiyu 1 – HCB & NSP

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 1:1-25

Asalin Yesu Kiristi

(Luka 3.23-38)

1Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.

2Ibrahim ya haifi Ishaku,

Ishaku ya haifi Yaƙub,

Yaƙub ya haifi Yahuda da ’yan’uwansa,

3Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu;

Ferez ya haifi Hezron,

Hezron ya haifi Ram,

4Ram ya haifi Amminadab,

Amminadab ya haifi Nashon,

Nashon ya haifi Salmon,

5Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa,

Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa,

Obed ya haifi Yesse,

6Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda.

Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.

7Solomon ya haifi Rehobowam,

Rehobowam ya haifi Abiya,

Abiya ya haifi Asa,

8Asa ya haifi Yehoshafat,

Yehoshafat ya haifi Yehoram,

Yehoram ya haifi Azariya,

9Azariya ya haifi Yotam,

Yotam ya haifi Ahaz,

Ahaz ya haifi Hezekiya,

10Hezekiya ya haifi Manasse,

Manasse ya haifi Amon,

Amon ya haifi Yosiya,

11Yosiya kuma ya haifi Yekoniya1.11 Wato, Jehohiyachin; haka ma a aya 12 da ’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.

12Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon.

Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel,

Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,

13Zerubbabel ya haifi Abiyud,

Abiyud ya haifi Eliyakim,

Eliyakim ya haifi Azor,

14Azor ya haifi Zadok,

Zadok ya haifi Akim,

Akim kuma ya haifi Eliyud,

15Eliyud ya haifi Eleyazar,

Eleyazar ya haifi Mattan,

Mattan ya haifi Yaƙub,

16Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.

17Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.1.17 Ko kuwa Kiristi. Kiristi (Da Girik) Almasihu (Da Ibraniyanci) duk suna nufin “Shafaffe.”

Haihuwar Yesu Kiristi

(Luka 2.1-7)

18Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki. 19Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.

20Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne. 21Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu,1.21 Yesu da Girik shi ne Yoshuwa da Ibraniyanci, wanda yake nufin Ubangiji yana ceto. gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”

22Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa, 23“Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel”1.23 Ish 7.14 (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).

24Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa. 25Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.

New Serbian Translation

Матеј 1:1-25

Исусови преци

1Ово је родословна књига Исуса Христа – сина Давидовог, сина Аврахамовог.

2Аврахам је имао сина Исака,

Исак Јакова,

Јаков је имао Јуду и његову браћу,

3Јуда је са Тамаром имао Фареса и Зару,

Фарес је имао Есрона,

Есрон Арама,

4Арам Аминадава,

Аминадав Насона,

Насон Салмона.

5Салмон је са Рахавом имао Воза,

Воз са Рутом Овида,

Овид је имао Јесеја.

6Јесеј је био отац цара Давида.

Давид је са Уријином женом добио Соломона.

7Соломон је имао Ровоама,

Ровоам Авију,

Авија Асафа,

8Асаф Јосафата,

Јосафат Јорама,

Јорам Озију,

9Озија Јотама,

Јотам Ахаза,

Ахаз Језекију,

10Језекија Манасију,

Манасија Амоса,

Амос Јосију.

11Јосији су се родили Јехонија и његова браћа за време вавилонског изгнанства.

12Јехонија је, после вавилонског изгнанства, имао Салатила,

Салатило Зоровавеља,

13Зоровавељ Авијуда,

Авијуд Елијакима,

Елијаким Азора,

14Азор Садока,

Садок Ахима,

Ахим Елијуда,

15Елијуд Елеазара,

Елеазар Матана,

Матан Јакова,

16Јаков Јосифа, који је био муж Марије, која је родила Исуса званог „Христос“.

17Дакле, од Аврахама до Давида било је четрнаест колена, од Давида до вавилонског изгнанства четрнаест колена, и од вавилонског изгнанства до Христа такође четрнаест колена.

Исусово рођење

18А ево како се Исус Христ родио: његова мајка, Марија, била је испрошена за Јосифа. Међутим, пре него што су постали супружници, испостави се да је она затруднела по Светоме Духу. 19Њен муж Јосиф, који је био праведан човек, не желећи да је јавно извргне срамоти, науми да потајно раскине веридбу.

20Тек што је он то наумио, кад гле, анђео Господњи указа му се у сну и рече му: „Јосифе, Сине Давидов, не бој се да узмеш Марију за жену. Дете које је у њој зачето, дело је Светога Духа. 21Она ће родити сина, а ти ћеш му дати име ’Исус’, јер ће он спасти свој народ од њихових греха.“ 22Све се ово догодило да се испуни оно што је Господ рекао по пророку:

23„Ево, зачеће девица и родиће сина, и даће му име ’Емануил’.“1,23 Иса 7,14. (То у преводу значи „Бог је с нама“.)

24Када се Јосиф пробудио, учинио је оно што му је анђео Господњи заповедио: узео је Марију за жену, 25али као супружници нису живели, све док она није родила сина. Јосиф му даде име „Исус“.