1天使让我看城内街道当中一道流淌着生命水的河,清澈如水晶,从上帝和羔羊的宝座那里流出。 2河两岸有结十二种果子的生命树,每个月都结果子,叶子能医治万民。 3再也没有咒诅,因为城里有上帝和羔羊的宝座,祂的奴仆都要事奉祂。 4他们必见上帝的面,上帝的名字必印在他们的额上。 5再没有黑夜,也不需要灯光和阳光,因为主上帝必做他们的光。他们要执掌王权直到永永远远。
基督的再来
6天使对我说:“这些话真实可靠。赐圣灵感动众先知的主上帝已差遣祂的天使,将那些快要发生的事指示给祂的奴仆们。”
7“看啊,我快要来了。遵行这书中预言的人有福了!”
8以上都是我约翰亲眼看见、亲耳听见的事。当我听见、看见这些事后,就俯伏敬拜将这一切指示给我的天使。 9天使对我说:“千万不可!我与你、你的众先知弟兄和那些遵行这书上话语的人同是上帝的奴仆,你要敬拜上帝。”
10他又对我说:“不可封住这卷书上的预言,因为时候快到了。 11不义的,让他继续不义;污秽的,让他继续污秽;公义的,让他保持公义;圣洁的,让他保持圣洁。”
12“看啊,我快要来了,到时候我要按各人的行为施行赏罚。 13我是阿拉法,我是俄梅加;我是首先的,我是末后的;我是开始,我是终结。 14那些洗净自己衣裳的人有福了!他们有权吃生命树的果子,也可以从城门进入城中。 15那些如同恶犬的败类、行邪术的、淫乱的、杀人的、拜偶像的和一切喜欢弄虚作假的,都要被拒之城外。 16我耶稣差遣我的天使到众教会,向你们证明这些事。我是大卫的根,也是大卫的后裔,又是明亮的晨星。”
17圣灵和新娘都说:“来吧!”听见的也要说:“来吧!”口渴的,让他来吧!愿意的,让他白白享用生命水吧!
警告
18我郑重警告所有听见这书上预言的人:如果谁在这书上增添什么,上帝必将这书上所记载的灾祸加在他身上; 19如果有人从这预言书上删减什么,上帝必使他无份于这书上所记载的生命树和圣城。
20那位证明这些事的说:“是的,我快要来了。”阿们!主耶稣啊,我愿你来!
21愿主耶稣的恩典与众圣徒同在。阿们!
An maido da Eden
1Sai mala’ikan ya nuna mini kogin ruwan rai, mai ƙyalli kamar madubi, yana gangarawa daga kursiyin Allah da na Ɗan Ragon, 2yana bin tsakiyar babban titi na birnin. A kowane gefen kogin akwai itacen rai mai ba da ’ya’ya goma sha biyu, yana ba da ’ya’yansa kowane wata. Ganyayen itacen kuwa saboda warkar da al’ummai ne. 3Ba za a ƙara samun la’ana ba. Kursiyin Allah da na Ɗan Ragon zai kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa hidima. 4Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu. 5Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin.
Yohanna da Mala’ikan
6Mala’ikan ya ce mini, “Waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa, ya aiki mala’ikansa, don yă nuna wa bayinsa abubuwan da za su faru nan ba da daɗewa ba.”
7“Ga shi! Ina zuwa da wuri! Mai albarka ne wanda yake kiyaye kalmomin annabcin da suke cikin wannan littafi.”
8Ni, Yohanna, na ji, na kuma ga abubuwan nan. Kuma sa’ad da na ji, na kuma gan su, sai na fāɗi a ƙasa a gaban mala’ikan da yake nuna mini su, don in yi sujada. 9Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da ’yan’uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye kalmomin wannan littafi. Allah za ka yi wa sujada!”
10Sa’an nan ya gaya mini cewa, “Kada ka rufe kalmomin annabcin littafin nan, domin lokaci ya yi kusa. 11Duk mai yin laifi yă ci gaba da yin laifi; duk mai aikata ƙazanta yă ci gaba da aikata ƙazanta. Duk mai aikata abin da yake daidai, yă ci gaba da aikata abin da yake daidai. Kuma duk wanda yake mai tsarki, yă ci gaba da yin abin da yake da tsarki.”
Maganar ƙarshe. Gayyata da gargaɗi
12“Ga shi, ina zuwa da wuri! Ladan da zan bayar yana tare da ni, kuma zan ba wa kowa gwargwadon abin da ya yi. 13Ni ne Alfa da kuma Omega, na Fari da kuma na Baya, Farko da kuma Ƙarshe.
14“Masu albarka ne waɗanda suka wanke tufafinsu, don su sami izinin ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta ƙofofi. 15Waɗanda suke waje kuwa karnuka ne, masu sihiri, masu fasikanci, masu kisankai, masu bautar gumaka, da duk wanda yake ƙaunar ƙarya yake kuma aikata ta.
16“Ni, Yesu, na aiko mala’ikana ya ba ka wannan shaida saboda ikkilisiyoyi. Ni ne Tushe da kuma Zuriyar Dawuda, da kuma Tauraron Asubahi mai haske.”
17Ruhu da kuma amarya suna cewa, “Zo!” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo!” Duk mai jin ƙishirwa, yă zo; duk mai bukata kuma, yă ɗibi ruwan rai kyauta.
18Ina yin wa duk wanda ya ji kalmomin annabcin wannan littafi gargaɗi. Duk wanda ya ƙara wani abu a kansu, Allah zai ƙara masa annoban da aka bayyana a littafin nan. 19Duk wanda kuma ya yi ragi a kalmomi daga littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai da kuma na birnin nan mai tsarki, waɗanda aka bayyana a littafin nan.
20Shi da ya shaida waɗannan abubuwa ya ce, “I, ina zuwa da wuri.”
Amin. Zo, Ubangiji Yesu!
21Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da mutanen Allah. Amin.