1. Janův 3 – SNC & HCB

Slovo na cestu

1. Janův 3:1-24

1Jak nás Otec miluje! Přijal nás za syny a dcery. Lidé nás často nechápou, protože Boha neznají. 2Už teď jsme jeho děti, ale neumíme si představit, jak nás Bůh ještě přetvoří. To však víme, že až Kristus přijde a my ho uvidíme v celém jeho majestátu, bude v nás dokončena proměna do jeho podoby. 3Každý, kdo v něj složil tuto naději, vyhýbá se všemu zlu, protože i Kristus je bez poskvrny.

4Kdo hřeší, staví se proti Bohu, protože hřích je porušení Božího zákona. 5Víte, že Boží Syn přišel, aby nás hříchů zbavil. U něho nemá žádný hřích místo. 6Kdo se Krista drží, ten se hříchu vyhýbá; kdo si s hříchem zahrává, Krista nezná a nerozumí mu.

7Děti, nedejte se nikým oklamat. Podle činů se pozná, zda se podobáme Kristu, který žil v souladu s Boží vůlí. 8Komu se hřích neoškliví, podobá se ďáblu, který se odjakživa staví proti Bohu. Boží Syn přišel proto, aby zrušil ďáblovo dílo. 9Kdo se stal Božím dítětem, vyhýbá se hříchu, protože v něm působí Bůh. Nemůže setrvávat v hříchu, neboť Bůh a hřích se navzájem vylučují. 10Podle toho se pozná, ke komu kdo patří: kdo se dopouští bezpráví a nemiluje bratra, nepatří Bohu.

Vzájemná láska

11Když jste poprvé slyšeli o Kristu, slyšeli jste také: milujte se navzájem. 12Podívejte se na Kaina. Přiklonil se k ďáblu a skončilo to bratrovraždou. Proč zabil svého bratra? Protože Ábelův příkladný život ho usvědčoval z hříchu. 13A tak se nedivte, když vás mnozí nenávidí.

14Víme, že už nepodléháme vládě smrti, ale vládě života, protože se navzájem milujeme. 15Kdo nemiluje, zůstává v zajetí smrti. Kdo nenávidí, rozsévá smrt a ztrácí podíl na věčném životě. 16Pravou lásku nám ukázal Kristus tím, že za nás obětoval život. To nás zavazuje, abychom byli ochotni nasadit za bratra i život.

17Kdo má dostatek a nedbá, že jeho bratr je v nouzi, marně tvrdí, že miluje Boha. 18Nemilujme jenom slovy, ale opravdovými činy. 19Taková láska nám dá vnitřní jistotu a uspokojí naše svědomí. 20Ale i při nejlepší snaze jsme odkázáni na Boží pochopení a odpuštění.

21Moji drazí, když zachováváme jeho přikázání a děláme, co se mu líbí, svědomí nás neobviňuje 22a smíme Bohu s důvěrou předkládat své prosby a očekávat, že je splní. 23A co nám tedy Bůh přikazuje? Abychom věřili, že Ježíš Kristus je Boží Syn, a milovali se navzájem. 24Kdo se podle toho řídí, je s Bohem zajedno. O této jednotě s Bohem nás ujišťuje Duch svatý.

Hausa Contemporary Bible

1 Yohanna 3:1-24

1Dubi irin ƙaunar da Uba ya ƙaunace mu da ita mana, har ana ce da mu ’ya’yan Allah! Haka kuwa muke! Dalilin da ya sa duniya ba tă san mu ba shi ne, don ba tă san shi ba. 2Abokaina ƙaunatattu, yanzu, mu ’ya’yan Allah ne, kuma abin da za mu zama nan gaba ba a riga an bayyana ba. Sai dai mun san cewa sa’ad da Kiristi ya bayyana, za mu zama kamar sa, domin za mu gan shi kamar yadda yake. 3Duk mai wannan bege a cikinsa yakan tsarkake kansa, kamar yadda shi Kiristi yake da tsabta.

4Duk mai yin zunubi yana karya doka ne; tabbatacce, zunubi, karya doka ne. 5Sai dai kun san cewa Kiristi ya bayyana ne domin yă ɗauke zunubanmu. A cikinsa kuwa babu zunubi. 6Ba mai rayuwa a cikinsa da yake cin gaba da yin zunubi. Kowa da yake aikata zunubi, bai taɓa ganinsa ba, bai ma san shi ba.

7’Ya’yana ƙaunatattu, kada ku yarda wani yă ruɗe ku. Duk mai yin abin da yake daidai mai adalci ne, yadda Kiristi yake mai adalci. 8Duk mai aikata abin da yake zunubi shi na Iblis ne, domin Iblis mai aikata zunubi ne tun farko. Dalilin da ya sa Ɗan Allah ya bayyana kuwa shi ne don yă rushe aikin Iblis. 9Babu haifaffe na Allah da zai ci gaba da yin zunubi, domin iri na Allah yana a cikinsa; ba zai iya ci gaba da yin zunubi ba, domin haifaffe ne na Allah. 10Ta haka muka san waɗanda suke ’ya’yan Allah da kuma waɗanda suke ’ya’yan Iblis. Duk wanda ba ya yin abin da yake daidai, ba ɗan Allah ba ne; haka ma wanda ba ya ƙaunar ɗan’uwansa.

Ku ƙaunaci juna

11Wannan shi ne saƙon da kuka ji tun farko. Ya kamata mu ƙaunaci juna. 12Kada ku zama kamar Kayinu, wanda ya zama na mugun nan, ya kuma kashe ɗan’uwansa. Me ya sa ya kashe shi? Domin ayyukansa mugaye ne, na ɗan’uwansa kuma na adalci ne. 13Kada ku yi mamaki ’yan’uwana, in duniya ta ƙi ku. 14Mun san cewa mun riga mun ratsa daga mutuwa zuwa rai, domin muna ƙaunar ’yan’uwanmu. Duk wanda ba ya ƙauna matacce ne har yanzu. 15Duk mai ƙin ɗan’uwansa mai kisankai ne, kun kuma san cewa ba mai kisankan da yake da rai madawwami a cikinsa.

16Yadda muka san ƙauna ke nan, wato, Yesu Kiristi ya ba da ransa dominmu. Ya kamata mu ma mu ba da rayukanmu domin ’yan’uwanmu. 17In wani yana da arziki, ya kuma ga ɗan’uwansa cikin rashi, bai kuwa taimake shi ba, anya, ƙaunar Allah tana a cikinsa kuwa? 18’Ya’yana ƙaunatattu, kada mu yi ƙauna da fatar baki kawai, sai dai mu nuna ta ta wurin aikatawa da kuma gaskiya.

19Ta haka muka san cewa mu na gaskiya ne, kuma za mu iya tsaya a gaban Allah ba tare da rawar jiki ba. 20Idan zuciyarmu ta nuna mana muna da laifi, mun san cewa Allah ya fi zuciyarmu, ya kuma san dukan kome. 21Abokaina ƙaunatattu, in zukatanmu ba su ba mu laifi ba, muna da ƙarfin halin tsayawa a gaban Allah ke nan. 22Muna kuma samun dukan abin da muka roƙa daga gare shi, domin muna biyayya da umarnansa, muna kuma yin abin da ya gamshe shi. 23Umarninsa kuwa shi ne, mu gaskata da sunan Ɗansa, Yesu Kiristi, mu kuma ƙaunaci juna kamar yadda ya umarce mu. 24Waɗanda suke biyayya da umarnansa kuwa suna rayuwa a cikinsa, shi kuma a cikinsu. Ta haka muka san cewa yana raye a cikinmu. Mun san haka ta wurin Ruhun da ya ba mu.