Židům 11 – SNC & HCB

Slovo na cestu

Židům 11:1-40

Příklady věrných

1Víra je naprostá důvěra, že se stane to, v co doufáme, a ona způsobuje, že nepochybujeme o tom, co nevidíme. 2K takové víře předků se Bůh přiznal a podal o ní svědectví prostřednictvím proroků. 3Vírou chápeme, že vesmír byl stvořen Božím slovem a nevznikl nějakým neznámým způsobem. 4Ve víře obětoval Adamův syn Ábel lepší oběť než jeho bratr Kain a pro víru byl prohlášen za bezhříšného. Kain ho po oběti zabil, ale Ábel navzdory smrti mluví skrze svou víru dál.

5Pro svou víru byl Henoch ušetřen smrti, protože Bůh si ho vzal k sobě. Předtím o něm bylo vydáno svědectví, že se líbil Bohu. 6To je bez víry nemožné. Ten, kdo přistupuje k Bohu, musí věřit, že Bůh je a že odměňuje ty, kteří ho hledají.

7Noe uvěřil Bohu, který mu předpověděl potopu, ačkoliv na ni v té době ještě nic neukazovalo. Poslušně začal stavět loď k záchraně své rodiny. Svou vírou vynesl soud nad světem a dosáhl dokonalosti, která je z víry.

8Vírou Abraham uposlechl, když byl vyzván, aby se vypravil do země, která měla být dědičně svěřena do užívání jeho rodu. Uvěřil a uposlechl, ačkoliv nechápal, kam jde. 9S důvěrou bydlel jako cizinec v zemi, která mu byla přislíbena. Žil se spoludědici zaslíbení – synem Izákem a vnukem Jákobem – ve stanech jako kočovník 10a toužil po pevně založeném městě, jehož stavitelem a tvůrcem je sám Bůh.

11Také Abrahamova manželka Sára vírou přijala od Boha moc, aby se stala matkou, ačkoliv už překročila svůj čas. Pevně věřila tomu, kdo jí dal zaslíbení. 12Proto z jednoho muže – a to už starce – vzešlo „množství lidu jako hvězd na nebi a jako nespočetný písek na břehu moře.“

13Ti všichni zemřeli ve víře, aniž se dočkali splnění všech zaslíbení. Víra je posilovala, byla jim útěchou a pomáhala jim k vyznání, že jsou na zemi jenom cizinci a poutníky. 14A kdo říká něco takového, naznačuje, že hledá vlast. 15Kdyby přitom měli na mysli vlast, kterou opustili, měli ještě dost času, aby se do ní vrátili. 16Oni toužili po lepší – nebeské. Proto jim Bůh připravil město a nemusí se stydět, že ho vzývali jako svého Boha.

17-19Bůh vznesl na Abrahama neuvěřitelný požadavek: Přál si, aby obětoval svého jednorozeného syna Izáka, se kterým bylo spojeno zaslíbení o rozmnožení rodu. Abraham se k tomu poslušně rozhodl v přesvědčení, že Bůh má moc vzkřísit i mrtvého. Proto mu Bůh Izáka vrátil jako obraz budoucího vzkříšení.

20Ve víře požehnal Izák svým synům Jákobovi a Ezauovi; on totiž věřil, že se uskuteční, co bylo zaslíbeno. Jákob měl pak dvanáct synů, z nichž nejznámější je Josef. Bratři se ho zbavili tím, že jej bez vědomí otce prodali do Egypta. Po počátečních nesnázích se tam nakonec stal místodržícím. V této vysoké funkci se dal bratřím poznat a v době hladu pozval svého otce k sobě do Egypta. 21Než tam pak Jákob zemřel, ve víře požehnal dvěma Josefovým synům.

22Když Josef umíral, ve víře připomněl svému lidu, že Bůh po staletích vyvede izraelské syny z Egypta, a vyslovil přání, aby ti, kdo se toho dočkají, přenesli jeho ostatky do Palestiny, Ta doba nastala, když se narodil Mojžíš. Jeho rodiče tehdy prožili těžké chvíle. Egyptský král totiž nařídil, aby izraelští chlapci byli hned po narození usmrceni. 23Ale Mojžíšovi rodiče si svého chlapce zamilovali a ve víře jej navzdory královskému rozkazu ukrývali; věřili, že je to Bohem vyvolené dítě.

24Když Mojžíš dospěl, zřekl se postavení králova vnuka. 25Rozhodl se raději trpět společně s Božím lidem, než prožívat svůj život v nevázaném veselí na královském dvoře. 26Byl si vědom, že Bůh odměňuje své věrné, a proto si vážil potupy pro Krista více než egyptského bohatství. 27Ve víře opustil Egypt a nebál se faraónova hněvu, neboť se pevně držel Toho, jenž je neviditelný, jako by ho viděl.

28Po dlouhém pastýřském životě se na Boží rozkaz vrátil do Egypta, aby odtud vyvedl svůj lid. Nebylo to snadné. Na zarputilý Egypt dopadala za trest rána za ranou. Došlo to tak daleko, že měli zemřít prvorození ve všech domech, jejichž veřeje nebyly potřeny krví berana na znamení, že je to příbytek člena vyvoleného národa. Tak Mojžíš ve víře v Boží slovo ustanovil velikonoční hod s obětováním beránků, aby Zhoubce nezahubil prvorozené Izraele.

29Na útěku před Egypťany Boží lid ve víře překročil Rudé moře, jako by šel po souši. A když se o to pokusili Egyptští, utonuli. 30Po letech putování pouští, které bylo zaviněno neposlušností lidu, se Izraelci pustili pod vedením Jozue do dobývání Palestiny. Výsměšně před nimi stálo pevné Jericho. Ve víře je sedm dní obcházeli a pak jeho hradby padly. 31Z obyvatel Jericha byla zachráněna jedině rodina prostitutky Rachab, která nezahynula s ostatními, protože ve víře přijala před bojem do ochrany izraelské vyzvědače.

32Co k tomu mám ještě dodat? Nestačí mi čas na vyprávění o Gedeónovi, Barákovi, Samsonovi, Jiftáchovi, Davidovi, Samuelovi a prorocích, 33kteří ve víře dobývali království, uskutečňovali Boží spravedlnost, dosahovali toho, co jim bylo slíbeno, 34zavírali tlamy lvům, vzdorovali žáru ohně, unikali násilné smrti, v slabosti získávali novou sílu, nabývali převahu v boji a zaháněli nepřátelské armády. 35Někteří mrtví byli vzkříšeni a vrátili se ke svým rodinám. Jiní byli mučeni, odmítli záchranu a dali přednost něčemu lepšímu – totiž vzkříšení k věčnému životu. 36-38Byli kamenováni, rozřezáváni pilou a stínáni. Další se podrobili zkoušce posměchu a bičování, dokonce i pout a žaláře. V ovčích a kozích kůžích o hladu, v úzkostech a zubožení byli štváni po pustinách a horách, skrývali se v jeskyních a dírách. Svět jich nebyl hoden. 39A ti všichni ačkoliv, osvědčili svou víru, nedočkali se splnění všech zaslíbení. 40Neměli totiž dospět k cíli bez nás, protože Bůh si přeje, abychom vstoupili do věčného života společně.

Hausa Contemporary Bible

Ibraniyawa 11:1-40

Ta wurin bangaskiya

1Bangaskiya ita ce kasance tabbacin abin da muke bege a kai da kuma tabbatar da abin da ba mu gani ba. 2Abin da aka yabi kakanni na dā a kai ke nan.

3Ta wurin bangaskiya ne muka fahimci cewa an halicci duniya bisa ga umarnin Allah, saboda an halicce abin da ake gani daga abin da ba a gani.

4Ta wurin bangaskiya Habila ya miƙa wa Allah hadayar da ta fi wadda Kayinu ya miƙa. Ta wurin bangaskiya aka yabe shi cewa shi mai adalci ne, sa’ad da Allah ya yi magana mai kyau game da bayarwarsa. Ta wurin bangaskiya kuma har yanzu yana magana, ko da yake ya riga ya mutu.

5Ta wurin bangaskiya ne aka ɗauki Enok daga wannan rayuwa, ta haka bai ɗanɗana mutuwa ba; ba a kuwa same shi ba, domin Allah ya ɗauke shi. Gama kafin a ɗauke shi, an yabe shi a kan ya gamshi Allah. 6In ba tare da bangaskiya ba kuwa, ba ya yiwuwa a gamshi Allah, domin duk mai zuwa wurin Allah dole yă gaskata cewa yana nan, kuma shi ne yakan sāka wa waɗanda suke nemansa da gaske.

7Ta wurin bangaskiya Nuhu, sa’ad da aka yi masa gargaɗi a kan abubuwan da ba a gani ba tukuna, a cikin tsoro mai tsarki ya sassaƙa jirgi don ceton iyalinsa. Ta wurin bangaskiyarsa ya hukunta duniya ya kuma zama magājin adalcin da ake samu ta wurin bangaskiya.

8Ta wurin bangaskiya ne Ibrahim, sa’ad da aka kira shi ya fita zuwa wata ƙasar da zai karɓi gādo daga baya, ya kuwa yi biyayya ya tafi, ko da yake bai san inda za shi ba. 9Ta wurin bangaskiya ya yi zama a ƙasar da aka yi masa alkawari kamar baƙo a baƙuwar ƙasa; ya zauna a tentuna, haka ma Ishaku da Yaƙub, waɗanda su ma magādan alkawarin nan ne tare da shi. 10Gama yana zuba ido ga birnin nan mai tushe, wanda mai zānen gininsa da kuma mai gininsa Allah ne. 11Ta wurin bangaskiya Ibrahim, ko da yake shekarunsa sun wuce, Saratu kanta kuma bakararriya ce ya iya zama mahaifi domin ya11.11 Ko kuwa Ta wurin bangaskiya Saratu ma, wadda shekarunta sun wuce, ta iya haifi ’ya’ya domin ta amince cewa shi wanda ya yi alkawarin mai aminci ne. 12Saboda haka, daga mutum ɗaya, wanda dā shi ma da matacce kusan ɗaya ne, zuriya masu yawa suka fito kamar taurari a sararin sama da kuma kamar yashin da ba a iya ƙirgawa a bakin teku.

13Duk mutanen nan suna cikin bangaskiya sa’ad da suka mutu. Ba su kuwa karɓi abubuwan da aka yi alkawari ba; sun dai hango su suka kuma marabce su daga nesa. Suka kuma amince cewa su baƙi ne, bare kuma a duniya. 14Mutane masu faɗin irin abubuwan nan sun nuna cewa suna neman ƙasar da take tasu. 15Da a ce suna tunanin ƙasar da suka bari a baya, da sun riga sun sami damar komawa. 16A maimako, suna marmarin wata ƙasa mafi kyau, ta sama. Saboda haka Allah ba ya kunya a kira shi Allahnsu, domin ya riga ya shirya musu birni.

17Ta wurin bangaskiya Ibrahim, sa’ad da Allah ya gwada shi, sai ya miƙa Ishaku hadaya. Shi da ya karɓi alkawaran ya yi shirin miƙa makaɗaicin ɗansa, 18ko da yake Allah ya ce masa, “Ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.”11.18 Far 21.12 19Ibrahim ya yi tunani cewa Allah yana iya tā da matattu, a misalce kuwa, ya sāke karɓan Ishaku daga matattu.

20Ta wurin bangaskiya ne Ishaku ya albarkaci Yaƙub da Isuwa game da nan gabansu.

21Ta wurin bangaskiya ne Yaƙub, sa’ad da yake bakin mutuwa, ya albarkaci kowane ɗan Yusuf, ya kuma yi sujada yayinda yake jingine a kan sandansa.

22Ta wurin bangaskiya ne Yusuf, sa’ad da kwanakinsa suka yi kusan ƙarewa, ya yi magana game da fitowar Isra’ilawa daga Masar ya kuma ba da umarni game da ƙasusuwansa.

23Ta wurin bangaskiya ne iyayen Musa suka ɓoye shi har wata uku bayan haihuwarsa, domin sun ga cewa shi ba kamar sauran yara ba ne, ba su kuwa ji tsoron umarnin sarki ba.

24Ta wurin bangaskiya ne Musa, sa’ad da ya yi girma, ya ƙi a kira shi ɗan diyar Fir’auna. 25Ya zaɓa yă sha wahala tare da mutanen Allah, maimakon yă ji daɗin sha’awace-sha’awacen zunubi na ɗan lokaci. 26Ya ɗauki wulaƙancin da yake sha saboda Kiristi ya fi dukiyar Masar daraja, domin ya sa ido ga ladansa. 27Ta wurin bangaskiya ya bar Masar, ba tare da jin tsoron fushin sarki ba; ya kuwa jure domin ya ga wannan wanda ba a iya gani. 28Ta wurin bangaskiya ya kiyaye Bikin Ƙetarewa ya kuma yayyafa jini, domin kada mai hallakar ’ya’yan fari yă taɓa ’ya’yan fari na Isra’ila.

29Ta wurin bangaskiya ne mutane suka bi ta cikin Jan Teku, sai ka ce a kan busasshiyar ƙasa; amma da Masarawa suka yi ƙoƙari su yi haka, sai aka nutsar da su.

30Ta wurin bangaskiya ne katangar Yeriko ta rushe, bayan mutane suka yi ta kewaye ta har kwana bakwai.

31Ta wurin bangaskiya ne ba a kashe Rahab karuwan nan, ta tare da marasa biyayya ba don ta marabci ’yan leƙan asiri.

32Me kuma zan faɗa? Ba ni da lokacin da zan ba da labari a kan Gideyon, Barak, Samson, Yefta, Dawuda, Sama’ila, da kuma annabawa, 33waɗanda ta wurin bangaskiya ne suka ci nasara a kan mulkoki, suka aikata adalci, suka kuma sami abin da aka yi alkawari; waɗanda suka rurrufe bakunan zakoki, 34suka kashe harshen wuta, suka kuma tsere wa kaifin takobi; waɗanda aka mai da rashin ƙarfinsu ya zama ƙarfi; waɗanda suka yi jaruntaka wajen yaƙi suka kuma fatattaki mayaƙan waɗansu ƙasashe. 35Mata suka karɓi ƙaunatattunsu da aka sāke tasar daga matattu. Aka azabtar da yawancin mutanen nan, amma suka ƙi a sake su, domin sun tabbata za su sami lada mafi kyau sa’ad da aka tā da matattu. 36Waɗansu suka sha ba’a da bulala, har da dauri da sarƙa, da kuma jefa su cikin kurkuku. 37Aka jajjefe su da duwatsu; aka raba su biyu da zarto; aka kashe su da takobi. Suka yi ta yawo saye da fatun tumaki da na awaki, suka yi zaman rashi, suka sha tsanani da kuma wulaƙanci 38duniya ba tă ma cancanci su zauna a cikinta ba. Suka yi ta yawo a cikin hamada da a kan duwatsu, da cikin kogwanni da kuma cikin ramummuka.

39Waɗannan duka an yabe su saboda bangaskiyarsu, duk da haka babu waninsu da ya sami abin da aka yi alkawari. 40Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau. Kuma bai so su kai ga maƙasudin bangaskiyarsu ba sai tare da mu.