دوم قرنتیان 1 – PCB & HCB

Persian Contemporary Bible

دوم قرنتیان 1:1-24

سلام و درود از پولس

1از طرف من، «پولس»، كه به خواست خدا رسول عيسی مسيح هستم، و از طرف برادر عزيز ما «تيموتائوس،»

به شما مسيحيان اهل «قرنتس» و نيز به همهٔ مسيحيان سراسر ايالت «اخائيه» واقع در يونان.

2از درگاه پدرمان خدا، و خداوندمان عيسی مسيح، برای شما خواهان رحمت و آرامش می‌باشم.

تسلی خدا برای تمام مشكلات كافی است

3‏-4چقدر بايد خدا را شكر كنيم، خدايی كه پدر خداوند ما عيسی مسيح است، خدايی كه سرچشمهٔ لطف و مهربانی است و در زحمات، ما را تسلی و قوت قلب می‌بخشد. بلی، او ما را تسلی می‌دهد تا ما نيز همين تسلی را به كسانی دهيم كه در زحمتند و به همدردی و تشويق ما نياز دارند. 5يقين بدانيد كه هر قدر برای مسيح بيشتر زحمت ببينيم، از او تسلی و دلگرمی بيشتری خواهيم يافت. 6‏-7ما برای رساندن نجات و تسلی خدا به شما، زحمات بسياری متحمل می‌شويم. اما در اين زحمات، خدا ما را تسلی عطا كرده است، كه اين نيز به منظور كمک به شماست؛ تا بدانيد كه وقتی شما نيز در سختی قرار می‌گيريد، او شما را تسلی خواهد داد. او به شما اين قدرت را خواهد بخشيد كه ناملايمات را تحمل كنيد.

8ايمانداران عزيز، بی‌شک شنيده‌ايد كه در ايالت «آسيا» چه سختیها كشيديم. فشار مشكلات به حدی بود كه اميد نداشتيم زنده بمانيم، 9و احساس می‌كرديم كه محكوم به مرگ هستيم، چون برای نجات خود، كاری از دستمان برنمی‌آمد. اما اين زحمات درس خوبی به ما داد تا ديگر به خودمان متكی نباشيم، بلكه به خدايی توكل كنيم كه می‌تواند حتی مرده‌ها را زنده كند. پس همه چيز را به دست خدا سپرديم. 10او نيز ما را ياری داد و از مرگی وحشتناک رهايی داد؛ و اميد داريم كه بعد از اين نيز باز ما را رهايی بخشد. 11اما شما نيز بايد با دعاهايتان ما را ياری كنيد. وقتی ببينيد كه خدا به دعاهايی كه در حق ما و برای سلامت ما می‌كنيد، اين گونه پرشكوه جواب می‌دهد، آنگاه خدا را بيشتر سپاس خواهيد گفت.

در رفتار با شما همواره صادق و بی‌ريا بوده‌ايم

12آنچه باعث افتخار ماست، اينست كه می‌توانيم با نهايت صداقت بگوييم كه در رفتارمان با مردم و مخصوصاً با شما، هميشه صادق و بی‌ريا بوده‌ايم، و چشم اميدمان فقط به ياری خداوند بوده است، نه به توانايی‌های خودمان. 13‏-14نامه‌هايی كه به شما نوشتيم، همه روشن و واضح بوده‌اند و هيچگاه مطلبی سربسته نگفته‌ايم. اما در حال حاضر شما ما را به خوبی نمی‌شناسيد، ولی اميدوارم كه روزی ما را به طور كامل بشناسيد و به ما افتخار كنيد، همچنانكه تا حدی چنين كرده‌ايد. آنگاه ما نيز در روز بازگشت خداوندمان عيسی، به شما افتخار خواهيم كرد.

15‏-16با چنين اطمينانی به درک و فهم روحانی شما بود كه تصميم گرفتم در راه سفرم به ايالت «مقدونيه» و نيز به هنگام بازگشت از آنجا، نزد شما بيايم تا دوباره سبب تقويت روحانی شما گردم، و شما نيز مرا در سفرم به «يهوديه» ياری دهيد.

17حال ممكن است بپرسيد كه چرا تصميم خود را عوض كردم. آيا دودل بودم يا همانند بسياری از مردم اين دنيا شده‌ام كه وقتی می‌گويند «بلی»، منظورشان «نه» است؟ 18نه، چنين نيست. آن خدايی كه سخنانش راست و قابل اعتماد می‌باشد، شاهد است كه سخنان ما نيز قابل اعتماد می‌باشد و وقتی می‌گوييم «بلی»، منظورمان همان «بلی» است. 19زيرا فرزند خدا، عيسی مسيح، كسی نيست كه وقتی می‌گويد «بلی»، منظورش «نه» باشد، بلكه همواره هر چه گويد، همان را انجام می‌دهد؛ و پيغام و موعظهٔ ما يعنی من و «سلوانوس» و «تيموتائوس»، دربارهٔ يک چنين كسی بود. 20اوست كه تمام وعده‌های خدا را، هر چند كه بسيار باشند، عملی می‌سازد، و ما نيز همه جا اعلام كرده‌ايم كه او چقدر نسبت به وعده‌هايش امين و وفادار است، تا او جلال يابد. 21چنين خدايی است كه من و شما را تبديل به مسيحيان وفادار كرده و ما را مأمور نموده تا پيغام انجيل او را به همگان برسانيم؛ 22و مهر مالكيت خود را بر ما زده، و روح‌القدس را به عنوان بيعانهٔ بركات آينده در دلهای ما نهاده است.

23بنابراين، چنين خدايی را شاهد می‌گيرم كه علت نيامدنم نزد شما، اين بوده كه نمی‌خواستم شما را با سرزنشهای سخت خود، ناراحت كنم. 24در ضمن اگر هم بيايم، قادر نخواهم بود كه ايمانتان را چندان تقويت نمايم، چون به اندازهٔ كافی قوی هست. پس خواهان خوشی شما هستم. می‌خواهم شما را شاد سازم، نه غمگين.

Hausa Contemporary Bible

2 Korintiyawa 1:1-24

1Bulus, manzon Kiristi Yesu ta wurin nufin Allah, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu,

Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, tare da dukan tsarkaka a ko’ina a Akayya.

2Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.

Allah na dukan ta’aziyya

3Yabo ya tabbata ga Allah, da Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba mai tausayi, da kuma Allah na dukan ta’aziyya, 4wanda yakan yi mana ta’aziyya a cikin dukan wahalolinmu, domin mu kuma mu iya ta’azantar da waɗanda suke cikin kowace irin wahala, da ta’aziyyar da mu kanmu muka samu daga Allah. 5Gama kamar yadda wahalar Kiristi ta cika har tana zuba a cikin rayuwarmu, haka nan kuma ta wurin Kiristi ta’aziyyarmu ta cika har tana zuba. 6In muna shan wahala, ai, muna shanta domin ta’aziyyarku, da cetonku ne, in mun sami ta’aziyya, ai, mun same ta domin ta’aziyyarku ce, wadda take sa ku jure wa irin wahalan nan, da muke sha. 7Begen da muke da shi dominku kuwa, tabbatacce ne, domin mun san cewa kamar yadda kuke tarayya da mu a cikin wahalolinmu, haka kuma kuke tarayya da mu a cikin ta’aziyyarmu.

8’Yan’uwa, ba ma so ku zama da rashin sani, a kan wahalolin da muka sha a lardin Asiya. Mun sha wahaloli sosai, har abin ya fi ƙarfinmu, ya sa muka fid da tsammanin rayuwa. 9Ba shakka, a zuciyarmu mun ji kamar hukuncin kisa ne aka yi mana. Wannan kuwa ya faru ne domin kada mu dogara da kanmu, sai dai ga Allah, wanda yake tā da matattu. 10Shi ya cece mu daga irin wannan hatsari na mutuwa, zai kuwa cece mu. A kansa muka kafa bege cewa zai ci gaba da cetonmu, 11yayinda kuke taimakonmu ta wurin addu’o’inku. Mutane da yawa kuwa za su yi godiya ta dalilinmu, saboda albarkar da aka yi mana, ta amsa addu’o’i masu yawa.

Canja shirye-shiryen Bulus

12Wannan shi ne taƙamarmu. Lamirinmu yana ba da shaida cewa mun yi zamanmu a duniya, musamman a dangantakarmu da ku cikin tsarki, tsakani da Allah. Mun yi haka ta wurin bishewar alherin Allah, ba bisa ga hikimar duniya ba. 13Gama ba mu rubuta muku abin da ba za ku iya karatu ko ku kāsa fahimta ba. Ina kuma fata cewa, 14kamar yadda kuka ɗan fahimce mu, za ku kai ga cikakkiyar fahimta cewa za ku iya yin taƙama da mu, kamar yadda mu ma za mu yi taƙama da ku a ranar da Ubangiji Yesu zai dawo.

15Saboda na amince da haka, shi ya sa na so zuwa wurinku da fari, domin ku sami albarka riɓi biyu. 16Na yi shiri in ziyarce ku a kan hanyata zuwa Makidoniya, in kuma sāke dawo wurinku a kan hanyata daga Makidoniya, sa’an nan ku yi mini rakiya a hanyata zuwa Yahudiya. 17Kuna gani na yi wannan shirin ba da sanin abin da nake yi ba ne? Ko kuwa, kuna gani na yi shirin nan da halin mutuntaka ne, don in ce, “I” in koma in ce, “A’a”?

18Kamar dai yadda ba shakka Allah yake mai aminci, haka ma maganar da muka yi muku, ba “I” da kuma “A’a” ba ce. 19Gama Ɗan Allah, Yesu Kiristi, wanda ni da Sila da Timoti muka yi muku wa’azinsa, ai, ba “I” da “A’a” ba ne, amma a cikin Kiristi, “I” ne kullum. 20Domin dukan alkawaran Allah cikarsu a gare shi suke, ta wurinsa ne kuma muke faɗar “Amin”, domin a ɗaukaka Allah. 21Allah ne fa yake sa mu da ku mu tsaya daram cikin Kiristi. Shi ne ya shafe mu, 22ya buga mana hatiminsa a kan mu nasa ne, ya kuma sa mana Ruhunsa a cikin zukatanmu, domin yă tabbatar da abin da yake zuwa nan gaba.

23Labudda, Allah shi ne shaidata cewa don kada in ƙara muku wahala ne ya sa ban koma Korint ba. 24Ba nuna muku iko a kan bangaskiyarku muke yi ba, sai dai muna aiki tare da ku ne saboda farin cikinku, domin bisa ga bangaskiya ce kuke tsaye da ƙarfi.